AUREN WATA UKU by Sameena Aleeyou

Author :  Sameena Aleeyou Category :  KDP NOVELS

Chapter   28 / 103

81K to 84K   out of 306.8K words

hukunci zai zamana yana wajenmu.! "

Sosai Mama Dije ta tsareta da idanu tana ji akwai wata a k asa. Dan ta tabbata wann aure ba auren Allah da Annabi bane.. Duk yanda akai akwai wata shiryayya. Idan auren tsakani da Allah ne bayan duk abinda ta sanar ma Asshe a gaban Suwaiba wacce take mahaifiya ga Ummul ba yanda za ai Asshe ta amince akaima D ansu mace irin Ummul.

Umma harda sujudusshukur tayi dan farin ciki. Ta shiga d aga hannaye sama tana mik a ma Allah godiya  Alhamdulillah..! Alhamdulillah Allah abin godiya.. Allah gatan bawansa.. Kai amma dai annamimi baiji dadi ba.. Zakaran da Allah ya nufa da cara ko fah ana Muzuru ko ana shaho sai yayi.. Kuma wllhi idan rana ta fito tafin hannunki bata isa ta rufesa ba Dije..! Tani ma ta buga Dani ta barni balle ke..! Ta k arashe tana mik ewa tsaye harda rangad a gud a.

 Bada garaje ba Suwaiba..! Muryar Asshe ya dakatar da ita.

Umma ta waro idanu waje dafe da k irji tana duban Asshe. Sai kuma ta soma girgiza Kai  A a dan Allah.. Ki rufa mun asiri Hajja Asshe.. Ki dubi girman Allah kar ki bari mak iya suyi dariya.. Wllhi duk abinda kikaji daga bakin Dije ba komai bane face sharrin mak iya..

Asshe ta dafa Umma tana murmushi  Kin yarda cewa aure rai ne dashi..?!

Umma ta jinjina kai tana duban Asshe.

Asshe taci gaba  Bazai Mutu ba sai kwanakin Sa ya k are.. Haka ne..?

Nan ma a sanyaye Umma ta jinina Kai.

Asshe ta juya ta basu baya daga Umma har mama Dije lokaci guda tana taka parlorn nata a hankali take ci gaba da fad in  Bari muce auren Ummul zai rayu ne na wani d an lokaci..!

Dummm! Haka k irjin Umma ya buga. Jiri ne taji na neman aikata k asa. Ta dafe garu tana furta  Ban ban.. Ban fahimceki ba Hajja Asshe.. Mai Kike nufi da cewa auren Ummul zai rayu ne na wani d an lokaci..?

Assshe ta juyo tana dubansu  Ina nufin zai rayu ne na tsawon watanni uku kacal.!

Dije ta gyara tsayuwarta sosai tana duban Asshe makirin murmushi kwance saman fuskarta. Cikin zuciyarta take furtawa  Eh Lallai.. Da alama yanzu ne wasan zai d au zafi.. Bari dai mu gani..!

Muryar Umma ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi.

 Ban.. Ban gane tsawon watanni uku kacal ba.. Me kike nufi Hajiya Asshe..? Me kike nufi da auren Ummul zai rayu ne na tsawon watanni uku kacal..? Ki min magana dan Allah.. Ki sanar Dani mai kike nufi..?!

 AUREN WATA UKU..! Ina nufin AUREN WATA UKU kawai mukayi ma D anmu da  yarki.. Bayan wata uku..

 Yarki zata dawo gareki.. Sai ki shirya mata wajen zama bayan wata uku..!

Duniyar Umma ya shiga juyawa sama na koma mata k asa& Ta girgiza kai tana jin hankalinta na neman gushewa da gaske. Cikin rawar murya Umma ke furta  Amma.. Amma meyasa haka Hajiya Asshe.. Shin wani irin aure kukai ma D anku da  Yata& Meyasa na wata uku kawai..?

 D an  Yar uwata yana aiki ne k ark ashin Kampanin Mahaifinsa. Mahaifinsa zai basa wani k wangila ne na tsawon watanni uku kawai idan yayi aure.. Bayan wata uku zai gama wann kwangilar.. Daga nan kuma bamuda buk atar  yarki dan kwangilar ta k are.. Kin fahimta..? Ta k arashe tana duban Umma sosai.

"Umma na girgiza kai cikeda rashin yarda take duban Asshe  Amm.. Amma.. Amma.. Bamu yi haka dake ba.. Wann zalunci ne..  Yata ta jima, ta d auki lokaci batayi aure ba.. meyasa kuka zab i cutar mun da  ya.. Ummul.. Ta wahala a rayuwa, ta fuskanci k alubale na gujewan manema.. Ta fuskanci k alubale da dama.. Bata cancanci irin wann auren ba..  Yata ta cancanci aure na gaske.. Aure mai d orewa ba mai rabewa ba.. Shin Auren Kwangila kukaima D anku da  yata..? Hajiya Asshe kin cuceni.! "

 Ban cuceki ba hasalima taimakon ki nayi.. Idan baki mance ba sadakin  yarki shine kud in jinyar mijinki.!

 Wani irin taimako ne wann..? Wane irin taimako ne haka.. Wann zalunci ne ba taimako ba..

"A zuciye Asshe ta katseta  Kar ki sake cewa na cuceki.. Ke kika cuci kanki.. Magana akan cuta.. Shin tsakanin ni da Ke waye ya cuci wani..? Ni da naima D ana auren cikan buri da  yarki ko kuma keda kika cuceni kika sakani a tsaka mai wuya, nai jagoranci wajen aura ma d an  Yaruwata wann  yar taki mai lullub e da Illan asiri da farar k afa.. shin ki fad a mun& Tsakanin mu biyun waye ya cuci wani..? Rayuwan d ana yana tsaka mai wuya a nan.. Idan Haidar Ya Mutu  yarki ce Sila.. Shin banyi adalci ba da nace zata zauna na tsawon watanni uku..?! "

Umma taci gaba da hawaye tana duk e wajen.

Asshe taci gaba  Ki gode ma Allah..  Yarki bazata fuskanci tozarci na mutuwan aure a daren aurenta ba.. Ki gode ma Allah bayan duk abubuwan da kikayi  yarki zata zauna k ark ashin Inuwan aure na tsawon watanni uku.. Ki gode ma Allah bazaki fuskanci dariya da gori harma da wulak anci idan har auren  yarki Ya Mutu a daren yau ba.. Domin kuwa duk wani Sirrinki da naji sai na bankad e.. Kuma Kinsan me..? Ta k arashe tana mai duk awa gaban Umma dake duk e tana hawaye  Zaki amar da duk wasu kud ad en da na kashe wajen nema ma D an  Yaruwata auren  yarki. Kaf ko kobo bazan bari yai ciwon kai ba.. Kin shirya biya.? Ta k arashe tana tsare Umma sosai da ido.

Inna Dije ta k arada  Daga nan kuma sai kiyi bankwana da Mijinki Suwaiba bayan kin rasa yaranki. Dan bayan abinda Ya faru ki sani zan d auke D anuwana na masa jinya bazan barshi tsakanin mata guda biyu da Babu Allah cikin zukatansu ba..!

Umma ta d ago idanunta masu zuban ruwa tana duban Dije da Asshe  Dan Allah.. Kar ku jefa rayuwata cikin garari.. Kuji tsoron Allah.. Kuji tausayin rai.. Ku tuna kuma iyaye ne.. Kuma burin ko wace uwa ta kai  yarta d akin miji.

 Kar kiyi mana maganan zama iyaye a nan.. Domin kaw baki tab a zama uwa ga  ya yanki ba Suwaiba.. Kuma yau zaki fara girban duk abinda kika shuka..! Dije ta k arashe tana sakin huci.

Asshe ta gyara tsayuwarta  A tsakanin watanni ukun ma inada sharud a.. Dan Kinsan a daren nan zan iya kashe auren  yarki Suwaiba haka ne..?! Ta k arashe tana duban Umma kannare da idanu.

Umma ta share hawayenta tana kuma jinjina kai a hankali kaman marainiyar mage.

Asshe ta jinjina kai  Shradina shine bazakiyi magana da Ummul ba har na tsawon watanni Uku. Ina nufin iyakacin wa adin zaman da zatai da D anmu. Keda had uwa da ita kuma sai kwangilar D ana Ya k are randa Ya cika aikinsa ya warware auren.. Ni kuma zan d auko  yarki da kaina na kawo miki ita cikin mutunci. Kin amince..?

Umma ta d ago a raunane tana duban Asshe jin da gaske dai Auren wutin gadi Ummul tayi ba kaman yanda taci mata buri ba. Sann ga wasu dokoki da sharud a Wanda aka gindaya na datse alak arta da  yarta  Dan Allah kar kiyi haka.. Kiyi hakuri& Kar ki rabani da Ummul.. Wllhi Ina son  Yata..

 Na zata kinfi so tayi aure tayi nesa dake& Ko ba haka bane..? Asshe ta katse ta.

Umma ta kuma rintse idanunta tana hawaye.

Muryar Inna Dije ya katseta  Burinki Ya cika Suwaiba.. Mata mazan  yarki tayi aure.. Amma aure mai gibi.. Wanda bada jimawa ba angulu zata koma gidanta na tsamiya.. Ta murmusa kafin taci gaba  Inama zanga Tani na bata wann babban Albishir..!

Umma ta shiga d ago hannaye daga duk e tana rok on Dije  Dan girman Allah ki rufa mun asiri Dije.. Kar abinda Ya faru yau ya fita ko ina.. Dan Allah Ku rufa mun asiri.. Wllhi na amince zanyi duk abinda kukace.. Amma kafin nan dan Allah ku barni nai Sallama da Ummul.. Ku barni nai Sallama da  Yata..!

Dije da Asshe suka dubi juna kafin Asshe ta jinina kai  Kinada minti talatin kacal kiyi Sallama da  yarki.. Sann ki aje wann a ranki.. Kaman dai yau nan da watanni uku zaki sake had uwa da  yarki.. Watak ila had uwa ta Har abada..

Umma ta shiga jinina kai tana godiya. Jiki Babu laka ta mik e ta nufi sashen da aka aje Ummulkhairy.

Umma tana shigewa Dije ta juyo tana duban Asshe duban irinta gogaggu. Dukansu biyu suka tsare juna da idanu. Kai da gani zaka fahimci wann ta naima wann kallon biri ne waccan tanai ma d aya kallon ayaba. Ko wacce irin duban da take ma juna kenan.

Dije ta murmusa tace  Kin d auki kasada mai girma ma d anki dukda na sanar dake ga abinda Ya samu nawa d an.. Meyasa..? Meye dalinlinki..?

Asshe ta murmusa irinta gogaggun wayayyu  Aw.! Baki yarda da hujjata bace..? Cewar auren kwangila na tsawon watanni uku mukai da  yarku.?

Murmushi Inna Dije Tai  Kar kiyi zaton wayewarki zaisa ki shashashantar Dani kamar yanda kika shahsantar da Suwaiba.. Ni ba Suwaiba bace.. K ar nake kallonki.. Dan haka Ki sanar dani meye asalin dalilinki.. Dan babu wanda zaiji abinda na fad a Ya kuma amince D ansa ko wani nasa yai tarayya da Ummul.. Bayan jifa na asiri dake jikinta ita d in barazana ce ga rayuwarsa.. Anya akwai wacce zata amince wani nata Ya zauna da Ummul matsayin matar aure..? Ko da yake ba d anki da kika haifa bane.. D an  Yaruwarki ne.. Tabbas akwai banbanci.! Ta k arashe shu umin murmushi saman fuskarta.

Asshe ta murmusa  Jifa na asiri..? Toh kodai kece kikai jifan.. Dan idan Har Zan amince D an  Yaruwata ya auri  yarku mai tawaya na asiri.. Bana jin akwai wacce zata tona ma  yar D an uwanta asiri irin haka.. Kaman dai yanda kikai ma Ummul.. Da ni dake dukanmu  Yanuwa ne ga iyayen Ummul da kuma Haidar.. Haka ne..?

Dije Tai shiru tana duban Asshe. Ta kula su duka biyun Sun k ware a iya buga wasan. Tabbas kuskure kad an zatai gaban matar nan ta sha k asa.. Koda wasa bazata bari hakan ta kasance ba. Gwara ta gyara d amararta da kyau.

Murmusawa Dije tai tace  Af! K warai haka fah.. Magana ake na gwaggwani da Innoni.. Wanda yafi nuna kula ga nasa.. Tabbas shi zai d auki kambin.. Mai zai faru idan na tafi na samu  yaruwarki na sanar da ita ga abinda kika shirya ma D anta& A bayan idonta..? Ta k arashe tana tsare Asshe da idanu ga muguwar murmushi saman fuskarta.

Asshe ta d an d auki lokaci tana dubanta. Dukda bugu da zuciyarta keyi bai hanata tattaro natsuwarta ba dan bata so ta bama Dije k ofan da zata d ago rauninta. ta murmusa tace  Wai ance da D an gari akanki gari.. Kin tab a jin an shiga gari yak i Anci yak in ba tareda taimakon D an gari ba..? Ina nufin kinada masaniyar wace irin yarda ce tsakanin  yanuwa biyu.? Ta k arashe tana tsare Dijen da idanu itama..

"Su dukansu biyu suna duban juna. Asshe ta murmusa ganin Dije bata bata amsa ba. Ta k araso ta dafa Dije kad an  A shawarce  Kowa ya tsaya a masarautarsa , Ina nufin kiyi yanda kikaso da Suwaiba harma da D anuwanki.. Kar ki shiga tsakanina da  Yaruwata.. Dan nasan bazaki so yin wasa da wuta ba.. Ta k arashe murmushi saman fuskarta."

Dije ta murmusa  D iyar mak eri bata shakkan wuta.. Hasalima ta saba wasa da wuta.. Kiyi tunani kan abinda na sanar dake. Domin kuwa kaman yanda kika amshi bak oncina cikin gidanki ba tareda kin gayyaceni ba. Toh ina mai tabbatar Miki zan kai ziyara ma  yaruwarki ta birnin tarayya.. Ina nufin mahaifiyar surkinmu. Ta k arashe murmushi saman fuskarta.

Shiru Asshe tai zuciyarta na kuma bugawa. Lallai wann matar babbar barazana ce a gareta. Dan tabbas idan ta tafi ta samu Kwaise ta sanar da ita abinda ke faruwa toh fah tata ta k are. Sosai tai nisa cikin duniyar tunanin yanda zata b ullo ma wann Dijen wacce ta zamto babban threat a gareta.

Inna Dije ta gyara zaman mayafinta  Kiyi tunani da kyau.. Ni zan tafi.. Dare yana yi.. Amma kafin na tafi ki zuba mun lambobinki a nan.. Sabuwar k awata.. Ta k arashe tana duban Asshe da ta zama deep in thoughts.

Asshe ta dubeta irin duban baki kai ki shiga jerin matsayin kawayena ba.. Sai kuma ta murmusa abinka da gogaggiya  K awa..? Oh haka ne& Ta bayan fage..! Ta k arashe maganar tana Shafa kwantattun gwalgwalan dake zube wuyanta zuwa kunnuwanta da hannayenta. Dije sai dubanta take tana jinina barikin matar nan. Watau bazata fad a mata matsayinta da baki ba saidai yanayin shigarta da suturan dake jikinta Ya tantance hakan.

Lokaci guda ta d auki wayarta ta mik a ma Inna Dije  Zuba min lambobinki a nan..

Inna Dije ta murmusa kafin ta dubi wayar kaman zata amsa sai kuma ta tabe baki tace  Baki tunanin ban Saba da rik e irin wayoyin nan naku ba.. K awa..! Ta k arashe tana juya mata gajiyayyar wayar dake rik e hannunta harda d aurin robber ring jiki.

"Asshe ta murmusa tace  Gashi Ba hand sanitiser kusa, bara na sanar dake da baki sai ki juye a naki wayar.. Ya Miki.. "

Dije ta jinjina kai  Kar ki damu.. matuk a bazaki lank wasa harshe ba.. Anyi alimantari an samu na zama cikin Al umma.. Kar ki mance lambobin gaske zaki bada dan idan ba haka ba. Zan riga ki isa wajen  yaruwarki. Ta k arashe murmushi saman fuskarta.

A haka dai sukai exchanging phone numbers kowa tana watsa ma juna bak ar magana da sako a dunk ule.

Inna Dije zata fice Asshe ta dakatar da ita  Ina Miki ta aziyar D anki.. Ina kuma fata hakan bazai faru da nawa D an ba..

Inna Dije ta murmusa  Fata mai kyau.. Allah yasa.. Idan kuma fatanki bai amsu ba.. Sai ki tanadi farin k yalle nan da watanni uku.. Watak ila akwai cin gumba gidan k awata..

Suka sakar ma juna murmushi Wanda yafi kama da yake. Kafin daga bisani suka kuma yin Sallama. Asshe ta juya idanu cikeda k osawa Har Inna Dije ta fice.

Zama Tai cikin kujera tana mai furtawa a fili  Oh ni Asshe wasu irin mutane na jajib o mana ne wai.. Ita Suwaiba nayi zaton abin nata a shashanci da wauta kawai ya tsaya ashe Shegiya wawiyar gangance  yar boka. Ga Tani daga can gefe mai cinye gadon miji yana raye.. Ita kuma wann Dijen da alama itace tafi kowa hatsabibanci cikin ahalin domin kuwa idan har banyi da gaske ba zata zame min babban barazana..!

Ta mik e cikin sand a ta nufi d akin da Umma ke ban kwana da Ummul d inta. Jikin k ofa ta mak ale tana sauraron tattaunawar  ya da Uwan.

Umma tai k ok arin saita kanta tana duban Ummul dake dubanta cikin rashin yarda hawaye kwance saman k uncinta. Sosai Umma ta sha mur kaman ba ita ba. Cikin zuciyarta kaw k ok arin danne raunin nata kawai take dan k arfafa gwiwar  yar tata. Cikin kakkausan murya ta ambato sunan Ummulkhairy snn taci gaba  Ina so ki mun alk awari guda d aya Ummulkhairy.. Watak ila shi kad ai ne alfarmar da zan nema daga wajenki.!

Ummul ta kuma duban mahaifiyar tata jiki a matuk ar sanyaye. Murya na tsananin rawa take furta  Umma kin wuce ki nemi alfarma wajena.. Kar ki mance ke mahaifiyata ce.. Ko me kike so nayi matuk a bai sab a wa Ubangijina ba zanyi& Dan cikan burinki& Zan zan Miki Umma..! Ta k arashe cikin sautin kuka.

Dukda kuka da yazo ma Umma amma sai

28 / 103