Kurman Allo Sakamakon Kin Karɓar Gaskiya by EEDAH ALIYU & ASMY B ALIYU

Author :  EEDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Category :  KDP NOVELS

Chapter   74 / 80

219K to 222K   out of 237.2K words

'yarta ta taso a hannun Aydah saboda haka ni ba zan hana ku tafiya da baby Noor ba sai dai Dan Allah a dinga kawo mana ita akai-akai muna ganinta.
Ammi ta yi magana tana share hawaye da gefen hijab ɗinta "karki damu Hajiya indai dan wannan ne bakida matsala.
Daddy ya faɗa da murmushi akan fuskarsa sun ɗan daɗe a gidan Daddy da Alh Bello Madawaki suna hirar yaushe gamo, kamin Ammi ta haɗa kayan Baby Noor wacce tun zuwansu Aydah ta goye abarta, har wurin mota su Ammi suka rako su.


Love Story 2023/2024
#Jeeddah Aliyu
#Asmy b Aliyu
#Team tagwaye novels
#Kurman Allo.
[2/7, 3:02 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO*
(A beautiful Love story)


NA
JEEDDAH ALIYU
&
ASMY B ALIYU


#Love story
#Gwagwarmaya
#Team tagwaye Novels






099.




"Daddy ya kamata a samowa Auta mai Reno,saboda ba zai yiwuwa ba ta rika zuwa da Baby Noor a school ba hankalinta zai rabu gida biyu.
Sadiya ta faɗa tana kallon Daddy,Siyama ta amsa zancen da faɗin "Hakane Daddy,da Mami, zata bar Huwaila sai ta dawo gidan ta rika kula da Baby Noor kafin Aydah ta dawo school.
"wannan ma shawara ce mai kyau.
Daddy ya faɗa yana kallon Aydah yana cigaba da faɗin."ki kiramin Huwaila a waya ki faɗa mata gobe da safe ta taho ta sameni kafin na fita aiki ina ganin gobe zan koma office.
kallon mahaifinsu suke yi cike da farin ciki acikin fuskokinsu.
Da gaske za ka koma office Daddy?"
Aydah ta faɗa sounding so very happy a muryata.
"In shaa Allahu zan koma auta.
"mungode sosai Daddy. Siyama ta faɗa wearing a loverly smile
"Allah ya dafa maka ya shiga lamurranka a duk inda zaka taka kafafunka.
Cewar Sadiya ita ma da murmushin kwance a fuskarta.
"Ameen duka suka amsa har suka isa gida hirar farin ciki suke ba zasu iya tuna wane lokaci ne suka zauna suka yi farin ciki irin wannan tare da mahaifinsu ba ,tun kafin ayi zancen auren Sadiya da Abba.
Sai da suka ci abincin dare tare da mahaifinsu cikin nishadi da annashuwa Mami,dai sai binsu take da kallo. ga baki ɗaya jikinta a mace
yake sai da suka gama Daddy,ya koma bangarensa Aydah ta nufi ɗakinta da luggage ɗin Baby Noor. Sadiya da Siyama,suka nufi bangaren Mami
suka cimmata har ɗakinta sai da suka kwankwasa kofar tai masu izinin shiga sa'annan suka shiga da sallama a bakunan su kallo daya,Mami tayi masu ta dauke kanta ta cigaba da danna wayar hannunta. Daga Sadiya har Siyama jiki a sanyaye suka karaso cikin ɗakin,kan Soofa suka zauna. "Mami dan Allah kiyi hakuri bamu da niyyar mu bata maki rai kema muna son muganki cikin farin ciki kamar yadda muke so muga dayddy. Mami abubuwa sun ta faruwa marar dadi ji da gani tun akan auran yaya Abba Mami tunaninki ya canja imaninki yayi karanci duk da haka Allah ya nuna maki karfin ikonsa ya tabbatar da sai yaya Abba yayi zaman aure da Aydah. tau yanzu duk wannan rigingimun da ake yaya Abba baya ma duniyar sai idan mun tunasa muyi masa addu'a sai kuma gudan jininsa da yabar mana wanda ba zamu iya gudunta ba dole mu kaunaci abun da yafito daga jikin yaya Abba. kuma Mami,Noor kawai ce zata cirewa Aydah kewar yaya Abba kina ganin yadda damuwa tayi mata yawa
duk adalilin yaya Abba,yanzu mun samu abunda zai cire mata kewa miyasa ba zamu karbesa da hannu bibbiyu ba? Sadiya ta nisa ta cigaba da faɗin."Mami Ni kaina naga ishara tun a duniya?"nayi aure sama da watanni uku babu kwanciyar hankali duk akan sanadin abubuwan da kika yiwa yaya Abba ne Allah ya jarabceni haka nima abubuwan da nayi masu ne Allah ya nuna min kuskure na tun anan duniya ko makiyina bana son yayi irin rayuwar da nayi a gidan aurena watanni uku da yawuce,ga yar uwata nan Siyama ita ta nutsar dani ta nuna min illolin abubuwan da na dinga aikatawa a baya. Saboda Allah yana sona da rahama, nan take na tuba na nemi gafara wurin Ubangiji,hatta da Aydah sai da na sameta na nemi gafarta har yanzu kin san cewa Mami,bana bacci cikin farin ciki a kullum tunanina yaya Abba da Rumaisa da suka koma wurin mahalicci su ban nemi gafarar su ba a duk kwanan duniya girman laifin dana aikata masu yana hanani samun walwala. Ina addu'a ina yimasu sadaqa Allah ya kai haske kabarinsu.
Mami ki nemi Daddy afuwa duk irin laifukkan da kika yi masa a baya. Na san zai yafe maki Mami,kawai muna son ki tuba ki komawa Allah.
Sadiya ta karashe maganar cikin rawar murya kasa daurewa tayi saboda wani irin kuka da ya zo mata batare da ta shiryawa zuwansa ba, da gudu tabar ɗakin kuka na fitar hankali na fitowa tun daga karkashin zuciyarta. Haka Siyama ta tashi ta tabi bayanta ita ma da nata hawayen dake son zubowa. Suka bar Mami zaune a ɗaki tamkar an dasata hawayen idonta sun kasa tsayawa,tana jin girman laifukkan data aikata suna wani irin danneta ,bata san kuma tana ina za ta fara ba.
Washe gari karfe tara huwayila ta kwankwasa kofar falo sabuwar mai aikinsu ce mai suna Hanne ita ta zo ta buɗe mata ganin Huwaila zata girmeta yasa ta gaisheta Huwaila ta amsa tana fadar wurin Aydah ta zo ko ta tashi bacci?"Dan ita kanta Huwaila tsoron shiga cikin falon take tana gudun haɗuwa da Mami,dan bata san irin tarbar da za ta yi mata ba.
"Ki zauna bara na kira miki ita.
Hanne ta faɗa tana katsewa Huwaila tunanin da ta tafi lokaci ɗaya,kan rug Huwaila ta zauna.
Hanne ta je ta kwankwasa kofar ɗakin Aydah,Aydah ta yi mata izinin shiga ta shiga baby Noor ce goye a bayan Aydah dukansu sun yi wanka gwanin ban sha'awa zaka rantse Aydah ce ta haifeta a lokacin saboda ita ma Aydah jikinta ya buɗe ta cika komai na girma ya gama bayyana a jikinta
"Hanne ya aka yi ne kin gama jera komai ne akan dinning ɗin?"Aydah ta faɗa tana kallon Hanne, Dan tare suka shirya breakfast ita da Hanne ganin yau Mami bata sauko kasa ba tunda ta yi sallar asuba bata koma bacci ba. Tun bayan rasuwar AB da ta dawo gida ta zage ta koyi girki kala-kala a wurin Rumaisa da Mami har wani catering school ta shiga,idan taje gidansu Rumaisa haka zata mannewa Ammi suyi girki tare saboda Ammi ta kware a fannin girke-girken gargajiya,yanzu duk wannan sakarcin na son jikin Aydah tabarsa ta yi hankali tare da wata irin natsuwa ta ban mamaki.
Yawan aikin da take yi har ya daina bai wa Mami,mamaki ita ke gyara ɗakinta batareda ta nemi taimakon yar aiki ba.
"kin yi bakuwa tana kasa tana jiranki.
Hanne ta faɗa tana kallon Aydah, ɗan jim Aydah ta yi tana juya maganar Hanne aranta tana mamakin bakuwa?
Kafin tunaninta ya tsaya akan Daddy,yace Aunty Huwaila ta zo,cike da murna Aydah ta kalli Hanne tana faɗin."ki ce mata ina zuwa da haka Aydah ta ɗauki ƙaramin hijab ɗinta ta saka saboda kar sanyi ya yi wa Baby Noor yawa
Ta sauka downstairs gabanta na faduwa wannan karon bata san kalar tarbar da mami,zata yi wa Aunty Huwaila ba idan kuma taki amincewa da ita fa?" Wata zuciyar Aydah ta bata amsa sai ta ji jikinta ya yi sanyi lokaci ɗaya,har ta karasa cikin parlor ta ware ido da murna ta nufi Huwaila
tana gaisheta ita ma Huwaila da murna ta amsa tana ƙoƙarin duba Baby Noor.
"Ai bacci take yi Aunty Huwaila na samu nayi mata wanka.
Fitowar Mami,ya katse musu zance kowacce ta shiga hankalinta cikin rawar murya Huwaila ta gaisheda Mami,Mami ta amsa adakile.
"Daman Mami Daddy ne yace yau Aunty Huwaila ta samesa kafin ya fita office.
Sai da zuciyar Mami ta ɗan buga da ta ji Daddy ne yake neman Huwaila to tayi masa me?"nan take Mami ta shiga tashin hankali tunani na farko da yazo mata ko dai Daddy Huwaila zai aura dan ya rama abubuwan da ta yi masa abaya Girgiza kai Mami ta yi a ranta take faɗin "ai ba zai ma yiyuwa ba.
"Ki zauna bari nayi masa magana.
Mami ta fadawa Huwaila da rashin walwala a fuskarta kai tsaye bangaren Daddy ta nufa ta samesa har yayi wanka mami ta zauna ta gaishesa cikin sanyi murya ya amsa batareda ya kalli bangaren da take ba. Sa taji jikinta yayi bala'in sanyi saukowa tayi akan kujera ta haɗe hannunta wuri ɗaya cikin wani irin murya take faɗin."Dan Allah dan Annabi Daddy ,ka yafemun duk irin laifukkan da nayi maka a baya wallahi-tallahi sharrin zuciya ne da sharrin shaitan kai ma kasan ban taɓa ƙin Abba ba ni kaina bai san meya shiga kaina ba sai dai na danganta hakan da yadda abubuwa suka dinga yi min zuwan bazata.
Na yi nadamar waya'nnan abubuwa na aikata sosai wallahi dan Allah ka yafe min Alhaji.
Mami ta faɗa hawayen idonta na gudu akan fuskarta.
"Ni bani kika cuta ba Mariya wanda kika zalunta ya riga da yabar duniyar kawai ki je ki cigaba da addu'a da istgifari ko zaki ga daidai a Rayuwarki.
ɗan sanyi Mami,taji aranta,kafin ta daura da faɗin "Huwaila na falo tana jiranka,ban san kuma meyasa kake nemanta ba,nasan nayi maka laifi Alhaji karka haɗani kishi da Huwaila zuciyata za ta iya bugawa! Nasan halinku ku maza da zarar macce tayi maku laifi za ku nemi ku karo aure. Dan Allah karka yimin haka.
Wani murmushi Daddy,ya saki miyesa tun farko tunanin kara aure bai zo masa ba dan ya hukunta Mami sai yanzu data an karar dashi?wani kallo Daddy ya rika aikawa Mami ta saitin ta kafin yace "Idan ma na aureta ina ganin hakan ba haramun bane mariya?" Da shock Mami ke faɗin."Huwaila fa zata zo sa'ar Sadiya me za kayi da yarinyar daka haifa kuma wadda ta gama sanin sirrin gidan ka 'yarka aikinka wannan ba daidai bane Alhaji.
Mami ,ta faɗa a rude Daddy ya mike ya nufi kofar fita batareda ya kula Mami,ba ita ma a gigice tabisa zuciyarta banda rawa babu abunda take duk ranar da Daddy ya yi mata kishiya ita kam za ta iya mutuwa kishiyar ma kamar Huwaila. Har kasa Huwaila ta zube tana gaisheda daddy,
Banda uwar harara babu abunda Mami ke aikawa a saitin da Huwaila take."Huwaila yarinya nakeso ki samowa Aydah mai hankali wacce zata tayata rainon Baby Noor.
Da sauri Aydah ta kalli Daddy a shagwabe tana faɗin."Daddy nazata Aunty Huwaila fa za kace ta tayani raino ita kaɗai na yadda da ita idan aka dauko muguwa fa ta yi ta cin zalin Baby Noor.
Aydah ta karasa maganar tamkar za ta yi kuka , murmushi Daddy ya yi yana faɗin."ai mai hankali zata samo wacce tasan halinta.
Ita ma Huwaila ta dauka Daddy zai ce ita. murmushi Huwaila ta kirkira tana faɗin "in sha Allah za'a samu Daddy
akwai wata yarinyar makotanmu sunanta Bintalo zasu zo sa'annin juna da Aydah idan na koma za yiwa Babarta magana idan sun amince shi kenan gobe na kawo ta. Huwaila ta faɗa da respect a muryarta, murmushi kurum Daddy keyi yana kallon yadda Mami,ta ɗan saki ranta ganin ba Huwaila ce zata taya Aydah rainon Baby Noor ba.
Daddy ya kirga kuɗi dubu goma ya bai wa Huwaila ta yi na mota,sai godiya take masa. Bayan tafiyar Huwaila suna karin kumallo Aydah ta dubi mahaifinta tana faɗin."Daddy miyesa?"sai wata banccin ga Aunty Huwaila ni nafi sabawa da ita na kuma fi yadda da ita. A mugun fusace Mami,ke faɗin."to ba za'a dauketa ba ɗin idan an kawo maki wata ki korata Huwaila kanwar uwarki ce kota ubanki.? Mami,ta faɗa tamkar zata rufe Aydah da duka,ga baki ɗaya ta ji ta tsani Huwaila. Da haka Aydah ta koma daki tana hawaye ta kira Siyama,tana faɗa mata yadda Daddy ya ce, hakuri Siyama ta bata tana faɗin."ta yi wa Daddy uzuri maybe yana da dalilin sa, da haka Aydah ta haƙura,kwana biyu tsakani Daddy yana ta shawara a zuciyarsa ba wai yana jin son Huwaila bane sai dai aurenta shi zai sa ya zama izina ga Mami,har ga sauran mata masu irin halinta dan ya cigaba da zama da Mami haka bai hukunta taba yabarwa sauran mata kofofin da zasu rika yin yadda suke so a gidan mazajensu har su cigaba da shirka saboda son zuciya. ba'a yi sati ba Huwaila ta kawo Bintalo haka ta fadawa Aydah tana da hankali sosai ta kwantar ta hankalinta,nan ma Daddy wasu dubu goma ya bata yace ta yi na mota.Ya kasance ranar assabr kusan sati ɗaya da zuwan Bintalo gidan, Daddy ya kira Siyama da Sadiya a waya yace su haɗu a office ɗinsa da misalin karfe goma na safe akwai maganar da zasu tattauna. Haka ma Aydah kuma ya gargadeta karta sake ta fadawa Mami,da yake ranar tana da lecture zuwa 12 sai ta fita karfe goma bayan ta yiwa Baby Noor duk abubuwan da take mata dan ko wanka ita take yi mata iyakaci Bintalo ta yi mata wankin kaya tayi rainonta. Idan lokacin cin abincinta ya yi ta bata shikenan,da kuma Aydah ta dawo school zat a karbi abarta su shige ɗaki wani irin so take wa Baby Noor dukka soyayyar da take wa Ab ta tattaro ta, ta dawo da ita kan Baby Noor ko kuka ta yi yanzu Aydah za ta bi ta tashi hankalinta. Yadda Mami taga Aydah tana kula da tattalin Noor sai ta dinga tuna lokacin da Abba yake rainon Aydah haka yake mata tarihi dai yana neman ya maimaita kansa.
Kai tsaye office ɗin mahaifinta ta nufa da motar da AB ya siyamata wanda driver ne ya koya mata motar saboda zuwa makaranta. Wurin ta samu tayi parking motarta, ta fito tana kallon motocin yan uwanta cike da mamaki ta ƙarasa office ɗin Daddy,ta gaisheda yayunta suka amsa Siyama tana tsokanarta da faɗin "Auta dai yanzu kin zama ustaziyyah wannan dogon hijab da kike sakawa har suna ja ga kasa kin dauka shi zai sa samari su daina kula ki muslim ƙanin Saleem yana nan yana min naci kin ki kulasa.
Yar fara'ar dake cikin fuskar Aydah nan take ta ɓace batt a tabare ta kalli mahaifinsu dake kallonsu cike da farin ciki, Daddy a can kasan zuciyarsa yana jin kewar Abba.
"Daddy kaga yaya Siyam ko?"
Siyam ta buɗe ido tana faɗin "Daga faɗar gaskiya sai kai ƙarata lallai auta kina da abin mamaki.
"Siyama ki daina tun da bataso.
Daddy ya faɗa cike da kashedi daria Sadiya ta yi tana faɗin. "To wai Daddy haka za a zuba mata ido ta zauna bazata yi aure ba?"
Fashewa da kuka Aydah ta yi babu kalmar da tafi tsana a duniya a furta mata irin kalmar aure. Ganin da gaske kuka take yi sai suka hau rarrashinta wannan karon har da Daddy, sai da suka tabbatar ta daina kukan ta natsu sa'annan Daddy,ya dubesu yana faɗin."Shawara nake so ku bani a matsayinku na 'ya'yana wani gefe kuma abokanina duk duniyar nan babu wanda ya kamata na nemi yaddarsa da shawararsa baya ga ku ɗinan kune kaɗa dole na. Duba da nayi yadda duniyar ta zama yanzu babu amana,ko ƙanƙani ku kaɗai na yarda daku nasan kowanne ku zai bani shawarar data dace kafin na yanke hukunci.
Dukkansu natsuwa suka yi suna sauraren mahaifinsu."Har yanzu na kasa manta irin rashin kyautatawa da mahaifiyarku tayi min ita gani take yi bansan cewa ita silar shiga tsakanina da Abba tai min asirin da na kori Abba da kaina wannan abun da mahaifiyarku ba zan taɓa iya mantawa dashi cikin sauki ba. Duk sanda na tuna haka sai naji wani iri araina duk da na yafe mata har cikin zuciyata kawai dai na kasa mantawa ne. Kuma wani bangaren na zuciyata ina son na hukuntata cikin ruwan sanyi yadda zata kara yin nadamar haka zalika ya zama izina ga masu hali irin nata.
Ga baki ɗaya sai suka yi shiru sun tattara hankalinsu akan bayanin da mahaifinsu keyi duk cikinsu babu wacce hankalinta bai tashi ba
duk tunaninsu ya tsaya akan mahaifinsu zai rabu da mahaifiyarsu ne. Kamar daga sama suka ji Daddy,na faɗin."zan kara aure auren kuma bada kowa ba sai da Huwaila ita kaɗai ce nake ganin ya kamata na aura hankalina ya kwanta ganin mun yi kusan shekaru goma a tare da ita. A wani irin razane suka daga kai suna kallon mahaifin nasu da sauri Aydah ta shiga girgiza kai duk da mahaifiyarsu mai laifi ce wannan hukunci yayi mata tsauri da yawa. "Daddy miyasa sai Huwaila kana gani ba zai zama cin fuska a wurin Mami ba a matsayin Huwaila na 'yar aikinta? Daddy ka canja wata dan Allah banda ita.
Kusan su duka suka furta suna haɗa baki da wani yanayi shimfide akan fuskokinsu.
"Aure babu fashi nayi niyya kuma ba gudu ba jada baya ba, ai don naci mata fuska yasa nace aure mai aikin nata. To amman meyasa bakwa son Huwaila ba ku san halinta bane ko yaya ko kun fiso naje na dauko wacce ke shirka wacce bata yarda da ƙaddara ba irin mahaifiyarku? Dukkansu shiru suka yi Daddy ya cigaba da faɗin "dukkan ku kun fini sanin halin Huwaila da tana da wani mugun hali da ko kaɗan ba zan yi wa kaina sha'awar aurenta ba don haka na shirya tsaf sai na hada mahaifiyarku kishi da wannan dai 'yar aikin nata Huwaila.
"Allah yasa haka shi yafi zama alkhairi Daddy,ina goyon bayanka dari bisa dari.
Sadiya ta faɗa tana jin wani iri a zuciyarta har ga Allah tana taya mahaifiyarta kishi, Siyama ma ta yi wa Daddy fatan alkhairi kafin Aydah ita ma tayi nata duka jikinsu a sanyayyen, nasiha sosai Daddy ya yi masu akan jin tsoron Allah kafin su yi masa sallama su fita. Aydah ce ta fara tafiya kafin Siyama ta kalli Sadiya tana faɗin "tsoron Allah ya ƙara shigata yaya Sadiya ni Babu wanda nake ji irin Mami.
Allah yasa hakan ya canjata gabaki ɗaya.
Sadiya ta faɗa duk jikinta a mace kafin kowace ta shige motar ta ta wuce.
Tun daga nesa Marwan Garkuwa ya hangota sai dai yanayin dake shimfide akan fuskarta yayi bala'in tsinka masa zuciya yau ko baccin kirki bai samu ya yi ba saboda kawai dan ya ganta ya shigo makarantar kafin su fara lecture rabon shi da ita tun shekaran jiya.


















#JEEDDAH ALIYU
#ASMY B ALIYU
#KURMAN ALLO
[2/8, 2:43 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO*
(A beautiful Love story)


NA
JEEDDAH ALIYU
&
ASMY

74 / 80