Author : EEDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Category : KDP NOVELS
gobe zan bayar dan Allah Mami na canja kaya na bi ku."Mami tayi gaba tana faɗin."kafin na dawo ki tabbatar kina islamiyya."
Daga haka Mami ta juya ta nufi kofa Sadiya tabi bayanta a hankali Aydah ta ture plate ɗin jelop ɗin shinkafar dake gabanta tafi minti biyar a haka kafin ta miƙe ta kai sauran abincin kitchen. Kai tsaye ɗakinta ta wuce tana tsinewa halin yaya Sadiya aranta tasan da bata yi magana ba da tsab Mami za taje da ita.
Har AB ya koma part ɗinsa yana mamakin wannan hali da Sadiya ta tsira, tunawa da maganarta akan a shirye take a ƙara mayar da aurensu ba ƙaramin tsaya masa arai ya yi ba da ya tuna haka sai ya ji gabansa ya wani irin faduwa. Gashi har lokacin ya kasa sanar da Rumaisa akan auren da Daddy zai haɗasa da Aydah wannan karon kuma bai san taya zata dauki al'amarin ba. Har yanzu bai cire ransa ba akan mafarki ne yake, so yake kawai ya tashi yaga cewa mafarki ne da gaske.
Mami na driving zasu je gidan Aunty Safeena.
Sadiya ta kalli Mami cikin fuskar damuwa ta ce."Anya Mami kina ganin zai amince ya mayar dani ɗakina cikin sauki?"
"Zai iya amma idan kika ci-gaba da yimasa dabaruku na mata na kissa
shi da kansa zai je wa Daddynku da zancen zai mayar dake ya haƙura da auren Aydah.
Shiru Sadiya ta yi tana kwantar da kanta cikin seat ɗin mota tana fatar Allah ya karbi addu'arta yasa zancen Mami ya zama gaskiya da tasan sai tafi kowacce macce sa'a a duniya samun mijin aure irin Abba Bashir ai ba ƙaramin sa'a bane a arayuwa, tana jin yadda moment ɗin rungumesa da ta yi yana zauna mata acikin zuciyarta wani irin azababben son yayan nata ke shiga lungu da sako dake cikin zuciyarta. Sosai Aunty Safeena ta yi murnar ganin yayarta ta
Sadiya ta zauna cikin kujerun da suka ƙawata parlor tana gaishe da small mum ɗinta. "Aunty Safeena ban ji hayaniyar su Malika ba.?
"Sun tafi islamiyya maimoon kuma tana gidan Hajiya.
Aunty safeena ta zauna tana kallon Mami "Yaya hop Daddyn Siyama ya amince?" Wani gwaron numfashi Mami ta sauke tana faɗin."ai na faɗa maki da kyar idan zai yarda kin manta taurin kansa, shiyasa ma yanzu na taho da Sadiya ɗin anan mu san wace shawara kuma ya kamata mu yi. Mami ta baiwa Aunty Safeena labarin abunda ya faru tsakanin Abban, da Sadiya Aunty Safeena ta juya kan Sadiya tana faɗin ."kinga kalar taurin kai irin na ubanki abunda ya jawo maki kou?"da yanzu kina gidan Abba hankalinki a kwance sosai naji takaicin raba wannan auren naki da Abba, yanzu tunda kin san ciwon kanki kin dawo right sense ɗinki sai ki yi ƙoƙari cikin kwana shidda kafin Daddyn naku ya kara maimaita wani kuskuren duk yadda za ki yi, ki dakatar da aurensa da Aydah ya zama kece zaki kara zama matarsa a karo na biyu. Da haka suka kai karshen maganar, koda suka koma gida dab da magarib kowanne ya shige ɗakinsa dan yin sallah basu haɗu ba sai bayan ishai da suka fito cin abincin dare. Har lokacin Aydah kumbure-kumburen fuska take ,duk fushinta akan Mami taki fita da ita ne. Da Sadiya taga har an kusa kammala cin abincin na dare bata ga bullowar yayan nasu ba ta zuba masa komai da komai cikin tray ta nufi bangarensa Siyama, dai sai bin yayarta ta kurum take da kallo ganin wai yaya Abba ne, za ta kaiwa abinci yau.
Sai da ta yi knocking ƙofar parlor aka bata izinin shiga ta aje tray ta ɗan buɗe kofar sa'annan ta ɗauki tray ta shige cikin parlor yana zaune cikin parlor yana aiki da laptop ɗinsa kallo ɗaya ya yi mata ya ɗauke kai Allah yasa ma jallabiyya ce ajikinsa tun da ya dawo sallar ishaai bai cire ba dan yasan Aydah za ta iya fado masa ko wane lokaci. Bin Sadiya kawai yake da kallo har ta aje tray ɗin da ta shigo dashi akan center table ga mamakin sa Sadiya ta yiwa kanta mazauni gaf da shi tana dan leƙa cikin laptop ɗin cike da kulawa ta ce "yayanmu aiki kake ashe? kowa ya fito cin abincin dare banda kai shiyasa na ɗibar maka na kawo ma.
"Thanks! kawai ya iya faɗa mata ya mayar da hankalinsa kan laptop ɗinsa ya ci-gaba da aiki cikin kwarewa ita dai Sadiya tallabe cheeks ɗinta tayi da hannuwanta duka biyu tana kallon yadda yake aiki cikin kwarewa, a gefe ɗaya kuma ƙamshin turaren Sadiyar ya dami AB sosai.
Sai Allah-Allah kawai yake ta tafi
har kusan minti goma yaga batada alamar zata tafi ya ture laptop ɗin gabansa yana kallonta yana faɗin."ki tafi sai da safe aiki nake. Yadda ya faɗa babu alamar wasa saman fuskarsa yasa gabanta ya shiga faɗuwa ,cikin sanyin murya da kwantar da kai take faɗin."Yaya magana nakeso muyi shiyasa nakeso na jiraka har ka gama aiki naka muyi maganar ta yadda bazan takuraka ba."
Wani numfashi ya sauke cike da gajiya a muryarsa yake faɗin "ina jinki" har ta buɗe baki za tayi magana taji ana knocking ƙofar parlor lokaci ɗaya mood ɗin Sadiya ya canja. kai tsaye AB ya bada izinin shigowa ,ran Sadiya ya yi mummunan ɓaci ganin wacce ta turo ƙofar sanye take cikin rigar bacci wacce da kaɗan ta wuce gwiwarta sai hular net da ta saka akanta ,tunda ta shigo take kallon Sadiya da yayanta. Ta cire takalmin ta ƙaraso cikin parlor tana kallon Sadiya take faɗin."Yaya Sadiya yaci abincin?" banza Sadiya ta yi mata karshema miƙewa tayi tsaye tabar parlorn a ɓoye AB ya saki wata irin ajiyar zuciya harga Allah ya ji daɗin zuwan Aydah dan da bai san yadda zai yi da Sadiya ba. Aydah ta nufi wurin tray ɗin tana buɗe abincin da Sadiya ta zubo masa ta haɗe rai tana kallon AB da ya ci-gaba da aikinsa a laptop "yayanmu ai ba kaci komai ba fa.
"Idan na gama zanci ya faɗa batare da ya kara kallonta ba. jin haka yasa taje ta zauna kusa dashi ta dauki dayar wayarsa tana game, knocking suka ji a ƙofar shigowa sai da ya bada izini Siyama ta shigo Parlor da dogon hijab har kasa dan har tayi shirin kwanciyya ta saka kayan bacci Mami ta tasota wai taje ta kira Aydah a part ɗin Yayansu Allah ya gani yau agajiye ta dawo makaranta bacci ne sosai a idanunta ,a bakin ƙofa Siyama ta tsaya ta gaishe da AB ya amsa yana kallonta kafin ta mayar da kallonta kan Aydah tana faɗin."ki je Mami na nemanki daga haka Siyama ta yiwa yayan nasu sai da safe ta wucewarta ,Aydah ta miƙe tsaye har lokacin wayar AB na hannunta take faɗin."yayanmu na je da wayarka dan Allah da safe kafin na tafi school sai na shigo na kawo maka"
Hannu ya miƙa mata alamar ta basa wayar, miƙa masa tayi tana wani turo baki haka ta fice daga part ɗin nasa kamar zata tashi sama kallo ya bita dashi yana sakin murmushi a hankali zuwa ya yi ya sakawa ƙofarsa key, a tsaye tasamu Mami na jiranta kallo ɗaya ta yiwa fuskar Mami ta ji gabanta yayi mummunan faɗuwa tsayawa tayi batare da ta ƙaraso ba
A tsawace Mami ke faɗin."sai ki ƙaraso nan! jiki na rawa Aydah ta ƙaraso Mami ta turata cikin ɗaki ta rufe ƙofa cikin masifa Mami take faɗin "Na lura kwanan nan kina wani shigewa Abba, naga alamar bakida hankali ko kaɗan kalli shigar da kika je masa dashi tarbiyyar da na baki kenan Zulaiha?" Mami ta faɗa a tsawace tana kiran sunanta na ainihi da sauri Aydah ta shiga girgiza kai hawaye har sun taru a idonta "uban me kike zuwa yi part ɗinsa da dare?" daga yau idan na ƙara ganin ƙafarki a part ɗin Abba wallahi-tallahi sai na karyaki a gidan nan, na riga da na faɗamaki bani na haifi Abba ba ba daddynku ya haifesa ba so ba muharraminki bane da za ki rika shige masa koda yaushe. Haka kika ga yayunki nayi masa?" Hawaye na sauka a idon Aydah take girgiza kanta "Na riga na faɗa maki duk namijin daba muharraminka ba ka yadda ko hannunka ya riƙa za ki iya yin ciki ko so kike kiyi cikin?" nan ma Aydah ta shiga girgiza kai hawayen idonta suka kasa tsayawa.
"To ki shiga hankalinki a gidan nan wuce ki je ki kwanta wawuya kawai...!" da haka ta fice daga ɗakin na Mami sai lokacin ta ji kukan gaske na taho mata ita ta kasa fahimtar duka maganganun Mami bata san me Mami ke nufi ba meyasa ɗazun da yaya Sadiya ta rungumesa ba ta yi mata faɗa ba sai ita.? haka ta kwanta ta rika rusa kuka tamkar wacce aka yankawa naman jiki.
#Love story2023/2024
#Jeeddah Aliyu
#Asmy b Aliyu
#Team tagwaye Novels
#kurman Allo.
Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only
ACCOUNT NUMBER
0020428430
Ishaq Fatima A. Gtb
Or
8098456130
Fatima Ishaq
Opay digital services
Shaidar biya
08098456130
KATIN MTN Ta👇
07043079282
Shaidar biya ta 07065283730
Ko a tuntubi
08086207764
0816 114 6563
+234 704 040 2435
+234 903 056 9336
*ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU.
*BAQEER*
Ayusher Muhd
Umm Asghar
*KURMAN ALLO*
Asmy b Aliyu
Jidda Aliyu
*AKWAI SIRRI*
Zee Bawa
Hajja ce
*MUTALLAB ASAD*
Nana Diso
Billy S Fari
*KULUWA*
Zee yabour
Sadiya Dan
Duka Biyar ɗin akan 2k
Hudu 1600
Uku 1200
Biyu 800
Ɗaya 500
VIP💕🔥
Duk guda ɗaya 1k
NORMAL GROUP 500
VIP 1000
[12/17/2023, 9:48 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO*
(A beautiful Love story)
NA
JEEDDAH ALIYU
&
ASMY B ALIYU
*AREWABOOK*:Jeddah3256
Love Story
#Gwagwarmaya
#Team Tagwaye
026.
Kukan da Aydah take yi ya haifar mata da headache gashi ta kasa bacci sai wurare ƙarfe 3:00am ta sami bacci, shiyasa duk knocking ɗin da Siyama take mata da asuba tashi ta yi sallah ba ta ji ba. Shiru-shiru har lokaci tafiyar ta school ya wuce bata tashi ba misali ƙarfe 8:00am Siyama da Sadiya sune zaune a dining Area kowacce ta yi shirin tafiya school kuma dukkanninsu lectures ɗin safe suke da. Siyama ce ta kalli Sadiya ta ce "Yaya Sadiya har yanzu Aydah fa bata fito ba kuma a ka'idar tafiyarta school 7:30am ne gashi har 8:00 ya yi.
"Mtss! Da kike gayamin me kike so nayi mata?
Cike da mamaki Siyama take kallon Sadiya gani yadda yanayin ta ya canza nan take, gudun kada abin ya koma musu faɗa sai kawai cikin sanyi murya Siyama ta furta "Babu ni da nake da abun yi mata bari na je na duba ta ko ba komai she's my little sister and I love her the way she is idan ma wani abu tai miki kike nuna wannan bad attitude akanta idan Aydah ce kin yi a banza don ba fahimta za ta yi ba. Ba kuma shi zai hana gobe ta sake yi miki laifin da ta yi miki ba watakila ma yafi na farko.
Siyama tana ƙarashe magana ta miƙe batare da ta tsaya jin kalar amsar da Sadiyar za ta bata ba ta haura bene yayin da Sadiya ta bi ta da faɗar "Idan kuwa ta ci-gaba da shige min hanci da kududduni dukan masifa zan mata a gidanan ba abinda za a yi wallahi. Ai duk ku ke ɓata ta tana yiwa mutane sangarta banza da wofi ni karyata zan yi.
Sadiya tana cikin wannan mita Mami ta sauko ƙasa tana tambayar ita da wa da sassafe nan? Kai tsaye ta bata labari abunda ya faru guntun tsaki Mami ta ja can ƙasan zuciyarta cike yake da fargaba da alama Aydah za ta bata matsala, sai yanzu take regretting barin shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakaninta da Abba. Yadda ta shaƙuwa dashi ko ita da ta haife ta bata shaƙu da ita haka ba, tun da ta haife ta kulawa da ita kacokan ya koma kan Abba iyakancinta da ita idan ta yi kuka ya kawo ta ta bata nono, sannu-sannu ma sai ta daina shan nono sai madara hakan yasa Abba ya tattare kayanta ta koma part ɗinsa hatta da wankin kayanta shi ke mata ya goge ya shirya mata su a gun da ya ware mata a closet ɗinsa. Mami tana cikin wannan tunani Abba ya shigo cikin brown suit ɗin da suka yi masifar yi masa kyau sai dai ya ɗan yi rama a fuska a dalili rashin lafiyar da ya yi ga kuma damuwar da kullum ƙara yawa take masa ya rasa tudun dafawa. "Ina kwana Mami?"
Ya faɗa sa'ili da ya iso dab da ita yana mai ɗan runsuna wa. "Lafiya ƙalau!
Mami ta amsa fuskarta ba yabo ba fallasa yayin da AB ya ja kujera ya zauna batare da ya lura da yanayi da Mami ta amsa masa gaisuwa ba. "Ina kwana yayanmu?"
Sadiya ta faɗa tana fari da idanuwa "lafiya! Ya
Amsa mata a takaice ta taso da sauri ta zari plate ta yi masa serving har ta ajiye masa plate ɗin a gabansa bai ɗago ya kalleta ba hankalinsa naga wayarsa da yake operating.
Siyama ta ɗinga yiwa Aydah heavy knock can cikin bacci Aydah ta ji knocking ɗin sannu a hankali ta ɗan buɗe idanuwanta kanta ya yi mata mummunan sarawa tai sauri dafe forhead ɗinta, ta ɗauki daƙiƙu a haka kafin ta ƙarashe ware idanunta dukka, cike da kasala ta tashi zaune still hannunta na kan goshinta ta ya ye duvet ɗin jikinta tare da ture shi gefe ɗaya ta zura ƙafafuwanta ƙasa ta sauka daga gadon, tana tafe dizzy na ɗibarta a haka ta isa ga ƙofar ta cire key "Subhanalillah! Daman ba ki da lafiya Aydah shi ne kika kunshe a ɗaki batare da kin faɗawa kowa ba? So kike ki kashe kanki ko me?"
Zazzafan numfashi Aydah ta fesar wanda iskarsa ya sauka a fuskar Siyama da sauri ta kama ta suka koma ciki ɗakin ta zaunar da Aydah a gefen gado sannan ta ce "wait for me here while I make warm water for you to take a bath za ki ji ƙarfin jikinki.
Aydah ta gyaɗa kai Siyama ta wuce bathroom ta haɗa mata ruwan tana nan har Aydah ta fito daga wanka sosai kuwa ta ji daɗin jikin nata sai dai still kanta bai daina ciwo ba wannan kuma ya danganta ne da uban kukan da ta ci a daren jiya. Ta goge jikinta da hand towel as usual bata shafa mai ba roll on da turare kaɗai ta shafa ta zura plain cotton gown bata saka hula ba, ta kalli Siyama dake kitsa mata gadonta cikin sanyi murya ta furta "Nagode Yaya Siyam!
Harararta kawai Siyama ta yi ta kama hannunta "mu je ki yi breakfast kin ga saboda ke har na yi latti.
Da sauri Aydah ta rungume Siyama tana faɗin "I love you Yaya Siyama!
"Uhm! Kafin zuwa anjima ki ce you hate me ba.
'Yar dariya Aydah ta yi cikin shagwaɓe murya ta ce "Kai yaya Siyam.
"Kai Aydah!
Siyama ta faɗa tana kwaikwayar muryarta sai kawai suka yi dariya footsteps ɗinsu yasa Sadiya ta ɗaga kai ta kalle su gani Aydah ya ɓata mata mood ɗinta, har sai da ta ja guntun tsaki sai a kunne AB ya kalleta a fakaice sai kuma ya maida ganinsa akan abincinsa. Mami da ke zaune a parlor tana waya da ƙawarta Hajiya Zeena ta yada ganinta akan jikin Aydah tana ganinta sanye da personal clothe ba da school uniform ba, ta ɓata fuska ta ba wa Hajiya Zeena uzurinta tare da faɗin za ta kirata later on.
Kusan a tare Siyama da Aydah suka gaida yayan nasu cike da kulawa ya dire spoon ɗin hannunsa ya ɗago yana kallon Aydah ganinta sanye cikin kayan gida yasa shi ɗan zare idonsa "Baby me ya faru na ganki sanye da kayan gida school ɗin fa?"
Da wani irin takaici Sadiya take kallon AB musamman yanda ya yi magana with so much caring ga sexy eyes ɗinsa dukka akan Aydah har wani kalan tuƙuƙi take ji yana taso mata a zuciya.
"Yaya Abba I'm sick.
Aydah ta faɗa cikin shagwaɓaɓbiyar muryarta har wani langwaɓar da kai take yi.
"Subhanalillah! Me ke damunki?"
"Headache and dizzy.
"Zo nan ki zauna kina jin jiri shi ne za ki tsaya salon ya yarsar dake na shiga uku.
Ba wai iya Sadiya ba hatta Mami sai da ta ɗan zare idonta sai kuma ta tuna da irin yanda Abba ɗin ya damu da Aydah indai akanta ne fiye da hakan ma zai iya. Aydah ta kalli hannunsa fari sol da ya miƙa mata da nufi ta ɗora nata hannu kamar wacce ta tsorota da gani hannun nasa tai sauri kallon cikin parlor gun da Mami take wani mugun kallo Mami ta wulga mata tai sauri janye idanunta daga kan Mamin ɗin. Direction ɗin da take kallo AB ya bi da idanunsa duk abinda Mami tai yi mata akan idonsa sai kawai ya yi murmushin takaici saboda ba ƙaramin zafi ya ji ba aganinsa koda Daddy bai bijiro da zance aure tsakaninsa da Aydah ba ita ɗin tamkar wani tsagi ne na jikinsa, ko zai cutar da kowa a duniya nan ban da Aydah.
Aydah ta zagaya ta zauna kujerar dake kusa dashi tasa ƙafarta ta ɗan tabo ƙafarsa hakan yasa ya kalle ta tai ƙasa da murya "Yaya Abba ka yi haƙuri da naki kama hannunka Mami ce ke hararata.
Murmushi ne ya subuce mishi a zuciyarsa yana ayyana idan ma Mami ta faɗi wani abu akansa, bakin Aydah ba zai shiru ba tsaf za ta kwashe ta faɗa masa.
Siyama ta kalli Sadiya ta ce "Yaya Sadiya tashi mu tafi ko kin fasa zuwa school ɗin ne? naga kin saka wa da ƙanwa gaba kina kallo sai ka ce yau kika fara ganin su.
Rai ɓace Sadiya ta tashi ta ture kujerar da tashi akai da ƙarfi a fusace ta wuce ɗakinta ta dauko handbag da takardun ta suka fi ce. AB bai damu da Kasancewar Mami a parlor ba ya zuba wa Aydah abinci ta ci sai da ya bata magani tasha ya umurce da ta je ta kwanta sannan ya yiwa Mami sallama, zuciyar Mami na tafarfasa ta ce dashi "idan ka dawo ka same ni akwai maganar da za mu tattauna.
"Okay! Ita ce kalma da kurum AB ya iya furtawa Mami ya fi ce abinsa saboda ya gama fahimtar inda kurman allonta ya dosa.
*MASARAUTAR KUDU*
Jakadiyar Kilishi ce ta fito daga ɓangaren Kilishi sai da ta duba lugun da saƙo na farfajiyar gidan bata ga idanuwa kowa akanta ba. Dukka