Kurman Allo Sakamakon Kin Karɓar Gaskiya by EEDAH ALIYU & ASMY B ALIYU

Author :  EEDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Category :  KDP NOVELS

Chapter   66 / 80

195K to 198K   out of 237.2K words

fuskarsa na kan laptop ɗinsa,sai kuma ya kalli Rumaisa yana faɗin.
"zan nemi alfarma a wurinki Habeebty Allah yasa zan samu.
Da sauri Rumaisa ta zauna tana kallonsa alamar dai tana jin sa,ki riƙa jan Aydah kitchen tana tayaki girki har ta iya tun da ba iyawa tayi ba haka kuma zai sa ku shaku da juna.
Baki buɗe Rumaisa ke kallonsa
"Ki yi hakuri dan Allah!
Da gaske Abba ya raina mata hankali ita ce zata rika shiga kitchen da kishiya har ta koya mata abinci.
Tun da daman yau Aydah za ta karɓi girki da dare ma sai ku yi tare bana jin daɗin yadda bakwa sakewa da juna.
Da sauri Rumaisa ta kallesa
"Bangane za ta karɓi girki ba kamar ya?"
Da mamaki AB ke faɗin.
"Kin manta kwana bakwai nayi a bangaren ki yau ya kamata na koma ɗakin Aydah?
Da mamaki Rumaisa ke faɗin."Amman kana bangarena kuma kana zuwa wurin Aydah da kwanakina akanka kuma ka ga ai bani da lafiya ba wani amarci muka yi ba. kawai ka yi haƙuri ka ƙara min sati ɗaya.
Da mamaki AB ke kallon Rumaisa jin yayi shiru tace "Ya naji ka yi shiru kuma. "Yoo ba dole nayi shiru ba naga kin zo min da hauka.
"Hauka fa ka ce habeebi?"
"Hauka mana Rumaisa akan me za ta ƙara miki sati ɗaya?
"Saboda ban gama more amarcina ba ta cuce ni ta sako min zubar jini don haka dole ta ne ta kara min sati ɗaya koda kuwa bata so.
"Ba zan iya ba Rumaisa kwana biyu kamar gobe ne nq dawo wurinki,duk wata kofa ta zuwa wurin Aydah ke kika buɗe min ita duk da bakya da lafiya da kina taimaka min ina samun natsuwa da ban je gareta ba.
Da wani irin fusata Rumaisa ta wuce daga parlor nasa da ido ya bi ta kusan minti goma da fitar ta ya aje laptop ɗin ya nufi ɗakin Aydah samun ta ya yi tana karanta novel a wayarta ya shigo da sauri ta tura wayar cikin pillow tayi saurin tashi zaune a bakin kofa ya tsaya yace "me kike yi yanzu?"
"Babu komai.
"owk! fita ki rikawa Rumaisa aikin abinci rana.
Babu musu Aydah ta miƙe ta nufi kofa shi ma bangarensa ya koma Huwaila da Rumaisa ta samu a kitchen daman Rumaisa na ganin ta shigo ta kalli gefen da Huwaila take tana gyara kayan miya tace "Huwaila ki barwa Aydah kayan miyan ta gyara zo ki gyara cabbage ɗin da za'a haɗa coslow.
Huwaila tasan Aydah ba iya gyaran kayan miya tayi ba amman ita kanta Huwaila tana son Aydah ta zama full house wife kamar ko wace macce."Auta ƙaraso ki gyara tamkar Aydah za tayi kuka take faɗin."Aunty Huwaila ki dai gyara ya ji zai shigarmin a idona.
A wani irin fusace Rumaisa ta yiwa Huwaila tsawa tace tabarwa Aydah gyaran kayan miyan.
Wani irin kallo Aydah ta riƙa bin Rumaisa dashi "Ban san kin cika marar kunya ba sai kinzo ki dakeni zan san ke ɗin bakida tarbiyya baki iya komai ba Amman kin iya kwanciya da namiji a gado ki ware masa ƙafafu.
Ita dai Huwaila bata ce komai ba da sauri ta saukar da kanta a kasa
tarugu kawai Aydah ta gyara koshi tana gudun masifar yayanta daman tattasai gefe ta ajesa tace ba zata gyara ba hannunta zai yi yaji ta dauki albasa ta fara gyarawa sai hawaye take ga baki ɗaya ta galabaita kai da ganinta kasan bata saba ba,tana can ido a rufe ta datsawa yatsanta wuƙa ga wuƙar sabuwa, wani kalar ihu ta saki ta jefar da wuƙar tana riƙe da hannunta da jini ya fara fita da sauri Huwaila tayi wurinta tana ƙoƙarin riƙo hannunta AB ya shigo kitchen ɗin shi ma fitowar sa parlor kenan yaji ihunta kuma yau weekend babu inda ya fita da sauri AB ya nufeta Huwaila tayi saurin jada baya.
Yadda take wani irin kukan tabara yasa AB duk ya gigice ya juya yana yiwa Rumaisa faɗan meyasa za'a bata aikin da zata rika wuƙa tun da tasan bata iya ba koya ne take yi kamata ya yi ta fara yi mata demonstration kafin ta bata wuƙa.
Saboda takaici kasa cemasa komai tayi a haka ya riƙa hannun Aydah dake famar rusa kuka har lokacin suka fice daga kitchen ɗin wani mugun kallo Rumaisa tabi AB dashi a haka zata zauna tana shiga kitchen da wannan yarinyar duk iya ƙokarinta baya gani ashe kuwa akwai bala'i da masifa a gaba.








#JEEDDAH ALIYU
#ASMY B ALIYU
#KURMAN ALLO.
[1/31, 2:10 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO*
(A beautiful Love story)


NA
JEEDDAH ALIYU
&
ASMY B ALIYU


Love Story
#Gwagwarmaya
#Team Tagwaye


089.


AB ya zaunar da Aydah akan kujera ya nufi upstairs da sauri ya je ya dauko first aid box ya yi mata dressing ciwon nata sai wani ƙara narkewa take yi shi kuma sai biye mata yake yi daga ƙarshe ya sake komawa kitchen ya tarar da Rumaisa har ta yi nisa da aikin ya kira sunansa cikin taushi murya.
"Habibty!
"Na'am!
Ta amsa tare da juyawa tana kallonsa karasa shigowa kitchen ɗin ya yi hakan yasa Huwaila ta fice da sauri daman tana so ta sami dalili da za ta je ta duba Aydah, kamar Ab zai faɗin abu kirki musanman yadda ya kira Rumaisa da tattausan kalami.
"Habibty ki yi haƙuri ki cigaba da yi mana girki har zuwa gaba idan baby ta ƙara girma sai ta karɓe ki.
"Jar ubanan! Abba Bashir na gaji da raini hankalinka fa kar fa ka ɗauke ni shashasha wacce batasan abun da take yi ba.
Cike da zallan mamaki AB ya zaro manyan idanunsa yana kallon Rumaisa yadda ta yi amfani da kalmar rashin ɗa'a akansa kanta tsaye sai ka ce wani sa'anta.
"Rumaisa ni ke faɗa wa kalaman rashin ɗa'a to da kika ce jar ubanan da uban waye kike Allah yasa dai ba nawa kike nufi ba?"
"Yoo kai kana da uba ne balle a zagi sa ai zagin ubanka tamkar harara ne a duhu.
Abun da Rumaisa ta faɗa a can kasan zuciyarta kenan amman a bayyane sai ta ce "Ka ga Habibi banaso rigima yarinyar da duk ta iya kwanciya da namiji girki ne ba za ta iya ba. Ka cire son zuciya ka fuskanci gaskiya, ni dai ba 'yar aikinka bace balle ka cilasta min cigaba da girki a gidanan.
Shiru AB ya yi yasan iya gaskiya Rumaisa ta faɗa to amma kuma bayaso duk wani abun da zai wahalar da Aydah.
"Shi kenan duk ranar girkinta Huwaila ta dinga yi ke kuma ranar naki ki yi mana, har Allah yasa ta kara wayau ta dinga yi da kanta ai komai ɗan hakuri ne wata rana ma sai ki ga tafi ki iyawa.
"Allah ko?"
Rumaisa ta faɗa tare da yi masa kallon uku saura kwabo ta juya ta cigaba da aikinta tana ji wani irin tuƙuƙi baƙin ciki, lallai ya zama mata dole ta nemi hanyar da za ta dakile wannan iskancin da Ab ya tsira mata dashi, idan har bata yiwa tufkar hanci ba da wurwuri to kuwa kwabarta za ta yi ruwa tsululu abun da bata fatar faruwar sa.
AB ya gallawa gadon bayanta harara ya juya ya fice yana mai jin haushinta don shi bai ga abun tada jijjiyoyin wuya anan ba, fitina ce kawai irin ta Rumaisa.
*******
Anaal ta haɗa kayanta cikin farin ciki ta baro hotel ɗin gudun kada Ummie tai mata faɗa rashin sauka gidan Aunty Zeenah da ta yi yasa ta biya gidan cikin rashin sa'a ta tarar da Aunty Zeenah ɗin bata nan ta tafi Mubi bikin aure maigidanta kawai ta tarar Alhaji Sanusi, shi ma ya kira mata Aunty Zeenah ɗin a waya suka gaisa da yake ita bata da number ɗinta. Hajiya Zeenah matar ƙani Daddy mahaifin AB da Aydah ashe yayarta mahaifiyar Anaal ce uban su ɗaya.(tofa ana wata ga wata😳)
Zuciyar Anaal wasai ta baro garin Kano ta ɗauki hanyar birnin kudu koda ƙarfe biyu ta buga tana cikin masaurata.
Kilishi ga baki ɗaya ta gama ficewa daga hayyacinta domin duk wata dabara ta ƙare mata, tabi bokaye da malaman tsinbo daban-daban domin a hana wa Ciroma zama sarkin kudu sai dai kuɗin ta kawai suke ci, ta tsinewa Ciroma yafi shurin masaki ko son ganinsa bata yi shiyasa duk wannan shirye-shirye da ake yi na naɗin sarautar babu ita aciki ko raguwar yaranta taso ta hana masu su bar Ciroma shi kadai ya yi kidansa ya yi rawarsa sai da jakadiya ta ankarar da ita illar da take kokarin haifar wa da kanta, sannan fa ta barsu sai dai hakan ba ƙaramin ƙuna mata rai ya yi ba.
Washegari masarauta ta cika da mutane daban-daban domin wasu sun zo ne daga wa'yansu garuruwa dake makwabtaka da birnin na kudu, ga manyan sarakuna dukka sun hallara mai martaba sarkin Kano ya je,ga mai martaba sarkin musulmi shi ma ya zo sai sarkin Zazzau duk wani basarake dake arewacin Nigeriya yana garin Kudu, Ciroma aka fara nadawa kafin a naɗa Aliyu na Uku sai kuma aka cigaba da naɗin ƙanana sarautu da suka biyo baya. Bayan an kammala naɗin aka wuce reception dukka anan cikin masarauta yayin da mata suka gundanar da kwarya-kwarya walima aka ci aka sha aka kuma raba sovaniers manyan bags masu ɗauke da hotunan sarakuna biyu.
Bayan kammala reception kowa ya kama gabansa sai lokacin Aliyu na Uku ya nufi ɓangaren mai babban ɗaki tana arba dashi sanye da rawani ta fashe da kukan farin ciki ta dinga kwararo masa addu'o'in har tana cewa ko yau Allah ya dauki rayuwarta burinta ya cika. Sai wuraren karfe goma biyun dare Aliyu na Uku ya sami damar fitowa daga ɗakinsa yana so ya yi waya da Maysun throughout bai ji muryarta ba bata ji tasa ba. Sai da ya tabbatar da baccin Safiya ya yi nisa shi ne fa ya sato jiki ya fito balcony ya kira ta kamar jira take yi ta yi picking daman ta kasa bacci a dalilin rashin ji daga garesa, muryarta kaɗai dake ratsa masa kunne natsuwa take saukar masa ya rasa wane irin azababben so yake yiwa Maysun. Anaal da ta kasa bacci tana tunani ta ya ya za ta aiwatar da plan b ɗinta daman duk cikin plan ɗinta plan A ya fi sauki, a hankali ta nufi window ɗakinta dake cikin balcony ta buɗe sai ta hango Abbunta dafe da waya a kunnensa sai zuba uban murmushi yake yana shafa sumar kansa kamar dai wani ɗan saurayi mai shekaru talatin da bakwai a duniya jikin Abbu baya nuna shekarunsu ga kuma Abbu ɗan kwalisa ne koda yaushe cikin gyming yake yi ga kuma tsadaddun mayukan gyaran fata da yake amfani dasu. Ko a yanzu Abbu zai iya aure yarinya mai 'yar sha bakwai don kuwa he's very good looking ga kyau ga naira.
Ko Anaal bata tambaya ba tasan da wannan ruwa biyu ce(halfcast) yake waya nan da nan ta ji ranta ya yi mugun ɓacin musamman da ta tuna da irin hidimomin da Ummie tayi masa yayin naɗinsa, ta aikatu ba kaɗan ba shi ne yanzu tana yi bacci ya sato jiki ya baro ta can kwance ita kadai tsabar rashin adalci irin nasa dole ta jajirce ta kawo karshen wannan baƙin zalunci da mahaifinta yake gwada wa mahaifiyarta. A fusace ta maida window ta rufe ta zura bedroom slippers ɗinta ta fice har ta iso bayansa bai sani ba ya yi nisan da fadawa Maysun tsadaddun kalaman soyayya, yadda yake fitar da kalaman ko waye kai sai ka girgiza ashe Abbu ɗan soyayya ne yasan yarda ake tattalin mace asata farin ciki ummie ce kawai da ya tsana ita ce baya iya ba wa lokacinsa. Lallai Abbu mugun mutum ne mai bala'in son zuciya.
Duk Wadannan zantukan Anaal ce ke yi su acan kasan zuciyarta da ta fahimci al'amari na Abbunta ya fara fin ƙarfin ƙwaƙwalwarta sai tai hanzari taka masa birki ta hanyar gyaran murya a ɗan tsorace ya juyo a zatonsa ko Safiya ce har yanzu bai shirya gabatar mata da Maysun ba yana jiran lokacin da ya dace ya yi hakan.
Yana juyawa idanunsa suka sarke da na Anaal wacce tayi bala'in murtuƙe fuskarta babu rahama ko kaɗan akanta, ga kuma wani kallon tuhuma da take bin Abbu dashi.
"Anaal lafiya ba ki yi bacci ba?"
Aliyu na Uku ya faɗa bayan ya yiwa Maysun goodnight.
"Nima abun da zan tambaye ka kenan Abbu hankalina ya tashi da na hango ka tsaye anan kana waya duba da dare ne yanzu, shi ne na fito na duba ka na ji abun da ke faruwa da kai da ya hanaka bacci musamman yau da kake cikin dimbin gajiya.
Deep breath Aliyu na Uku ya sauke tare da faɗin "na kira Maysun ne don na ji lafiyarta.
"Uhm! Abbu Dan Allah ka bi a hankali kada Ummie ta rutsa ka kana waya da wannan matar duba da yadda ka ce ba ka shirya bayyana ta wa family ɗinka ba. Abbu karka manta Ummie tana fama da ciwon damuwa (depression) idan har ta tsinci wannan labari daga sama komai fa zai iya faruwa da ita. Abbu ka tuna ummie ta kamu da wannan ciwon ne ta dalilinka ko sau ɗaya ne ka yi mata adalci, Ummie ta yi maka sadaukarwa da dama ta kaunace ka da dukkan zuciyarta ta ba ka yarda dari bisa dari kada ka rushe wannan yarda a lokaci guda idan maganganu na sun yi maka ba daɗi ka yafe min Abbu dukkan ku biyu ina so naga kun yi rayuwar farin ciki zamantakewar ku ta daidaita kamar na sauran ma'aurata. Na barka lafiya Abbu zan je na kwanta sai da safe.
Daga haka Anaal ta juya zuwa ɗakinta Aliyu na Uku ya bi ta da kallo yana auna maganganun ta a mizani na hankali kafin ya juya shi ma ya koma ɗakinsa adaidai kofar shiga ɗaki ya kusan cin karo da Safiya ta farka bata ganshi ba shi ne ta fito ta duba shi da damuwa akan fuskarta take kallonsa tare da faɗin "Abbu na farka ban ganka ba shi ne na fito na duba ka ko kana buƙatar wani abu ne?"
Kafe ta ya yi da idanunsa wani irin tausayinta ne ya yi masa dirar makiya, batare da ya bata amsar tambayarta ba ya rungumo kafaɗarta "mu je mu kwanta mar'atul saliha.
Ya yi magana ƙasa-ƙasa murmushi kurum Ummie ta yi mai nuni da ta ji daɗin sunan da ya kira ta dashi.
Rumaisa ita kadai ta yi girkinta hatta da Huwaila da ke taimaka mata cewa ta yi bataso ta yi tafiyarta, tana kammala wa ta zuzzuba a warmers ta kai dining room ta yi arranging table sannan ta wuce ɗakinta ta yi wanka, lokaci da ta cire pant ɗin jikinta ta ga babu ko digon jini wani irin farin ciki ne marar misaltuwa ya lulluɓe ta, ranta farin tass tayi wanka tsarki da tuna yau Aydah za ta karbi girki duk sai ta ji farin cikinta yana komawa ciki tana idarda sallah ta zauna ta tsantsara kwalliya ta Musamman, ta nufi parlorn Ab dawowarsa daga masallaci kenan ta shigo ya shaƙi daddaɗan ƙamshinta har sai da ya lumshe idanuwansa tana murmushi ta zo ta zauna kusa dashi, sai ɗaya ya kalleta ya kauda fuska ya yi kamar bai ganta ba dan har yanzu da raguwar haushinta daƙare a zuciyarsa. Yadda ya yi mata ba ƙaramin ɓata mata rai ya yi ba kwalliyar da aka yi domin ko kallonta bai yi ba ballantana ya yaba ta kuma san dalili bai wuce ƙi amincewa da ta yi da bukatarsa na cigaba da yiwa Aydah girki dare ya yi su shige ɗaki shi da ita gaskiya Abba Bashir bala'in ɗan raini wayau ne shi ko cewa ta yi za ta dinga yiwa Aydah girki ai shi mai yi mata faɗa ne domin kuwa komawa baya ya yi yawa.
"Wai Habibina fushi kake yi dani? Don na ce ba zan yiwa wancan yarinya girki ba?"
"Kwarai kuwa domin kin nuna min ban isa dake ba.
"Ayya! Ai kuwa indai sai na yiwa Aydah girki ne za ka isa dani ashe kuwa kana da jan aiki a gabanka don ba zan taɓa yi ba daga nan har bayyanar Isah.
"Ya ishe ki kada ki sake ki yi min rashin kunya kin dai ce ba za ki yi ba fine banaso kananun maganganu.
Rumaisa ta taɓe baki tare da maida hankalinta akan wayarta sai da ta ji haushinsa da take ji ya sauka kana ta ɗago ta kalle shi tana faɗin "Habibi tashi mu je mu ci abinci ya kalleta ba.
"A'ah! Me zai hana na kira ta ai cin tuwon kishiya ranko nima za ta biyani nan da ɗan wani lokaci.
Ta ƙarashe magana tare da miƙewa ta nufi ɗakin Aydah batare da neman izini ba kanta tsaye ta tura ƙofa Aydah dake tsaye gaban dressing mirror tana shafa turare ta juya idanunta suka sauka kan fuskar Rumaisah, ranta ta ji yana ɓaci akan me za ta shigo mata ɗaki batare da neman izinin ta ba.
"Idan kin ga dama ki fito mu ci abinci.
"Idan kuma banga ni ba fa?"
"Sai ki yi ta zama har a busa ƙaho.
"Ai shi mijinki da ya aiko ki, ki kirani ba zai taɓa yarda hakan ta faru ba. Idan kuma kina so na cire miki tantama ki je ki ce masa ba zan zo ba.
Kallon ta taɓe da baki Rumaisa ke yi tana mamaki yaushe wannan kwailar yarinyar ta yi bakin mayar mata da magana, dole fa ta zage damtse ta koya mata hankali idan bata nuna mata banbanci dake tsakani babba da yaro ba, ba za ta taɓa dawowa cikin hankalinta ba.
"Ke ni kike gayawa magana ashe bakida kunya fitsararriya?"
"Auu! Wai ke sai yau kika sani?Ai kuwa tuntuni banida kunya kece kaɗai ba ki fahimci hakan ba amma ai shi mijinki yasan wacece ni a fagge rashin kunya da fitsara har kyautar tsadaddiyar mota ya yi min akan iya rashin kunyata.
Tuni Rumaisah ta gama fahimtar shagwabe ne Aydah take mata wanka mai kamar jirwaye ranta ya yi mugun ɓaci musamman da ta ambata mata motar nan da AB ya bata wacce tai mata tsaye a ƙahon zuciya, sosai idanuwan Rumaisa suka rufe ta yi kan Aydah tana zuwa ta ɗauke ta da mugun mari. Da Aydah ta kurma ihu sai da ga baki ɗaya amon muryarta ya karaɗe gidan da gudun bala'in Ab yake haura mattakalar

66 / 80