Idan An Ciza Book 3 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Complete Novels

Chapter   20 / 49

57K to 60K   out of 146.6K words

ce" Mi ye illar mgana ta? Na ga ita da kanta ta ce ba ta son auran domin na taimaka mata komai ya kare laifi ne?
Sai kawai Mmi ta miƙe tana kallon Dr kafin tace" Dr gobe ko jibi zam koma Gombe."
Ta na gama faɗin haka ta bar musu ɗakin.
Khadi ta kai duban ta kan Madiha kafin ta ce"Gaskiya Sisto ba ki kyauta ba, kamar ni ne fa ki zagi Muhammad"
Madiha ta taɓe baki kafin ta ce"Muhammad dabam wannan talakan dabam, ki daina ma haɗa su."
Khadi na dariya shi kuma Dr ya haɗe rai yana mata faɗan abin da ta yi na ta kyauta ba sai kawai ta ce"Au don nace matsiya ci? Karya na yi? To shike nan na cire bakina."
Ba za ta daina ba halin su ɗaya da Abi shigen kafiya aiko har washegari Mimi ba ta ƙara yi ma Madiha mgana ba sai ta nemi ma jirgin Komawa Gombe ta samu na yamma.

Dr bai hana ta tafiya ba, an kulla mata Naman suna da yaji na ta da na Hajiya, Jirgin karfe biyar ta bi zuwa Gombe Dr. da Khadi su ka kaita filin Jirgi sai da za ta tafi sannan ta yi ma Madiha sallama ta amsa a daƙune ita gani take yi ina laifi domin ta faɗi gaskiya.
Sai dai Hajiya ta ga Mimi sarkin Ya ji kamar daga sama kuma ba domin mganar Daddy ba, hutun ta ya ƙare ya zama dole ta dawo.
Hajiya ta yi murna Baaba Uwani ta ce daman gidan shuru da ba ta nan, ta kira Daddy ta ce masa ta dawo kila anan Mama taji ta gayama Jaheed daman tun da ya ji ta Dawo gida ya addabeta da waya yana gaya mata yana kan bakan shi ta ce ba shi ma da hankali da auranta ai ba ya mutu ba ne.
Sai da ya ji ta dawo wai zai biyo jirgi gobe su yi mgana. Daman a gidan Madiha zuwan sa uku wajenta yana mata magiya ta faɗa masa Mijinta bai saketa ba amman ya na ce wai zai taya ta karɓan sakin daman ai ba su da ce da juna ba, shi a tunanin shi Madiha na goyon bayan shi, shike nan ya same ta ya gama. Tun da ya ce mata zai zo washegari ta ce masa ka da ya zo, domin ita ta san abin da take yi da auranta ba za ta zo tana haɗuwa da shi ba.

Washegari hutawa ta yi a gida, shi kuma Jaheed bai samu dama a wajen aiki ba Shi ya sa bai zo ba, Aji kuma Daddy da kansa ya kira shi ya faɗa masa Mimi ta dawo daman ranar sun karɓi lambar wayar juna sai ya ce zai shigo gidan ko a ranar da daddare ko washegari da yammah.
Bai samu zuwa a daran ba sai washegari bayan la'sar daga gida yake ya je ya gaida Inna sai da ta kara masa mganan Mimi ya ce daga nan wajen ta zai nufa.
A motarsa ya je yana sanye da ƙananun kaya, megadi na buɗe masa get ya shiga motarsa Mimi na fitowa tare da Rukky da ta zo ta rakota sun tsaya suna mgana sai ganin Aji suka yi ya fito daga motarsa duk da ya saka hula P. cap ta rufe rabin fuskar shi ba zai hana taƙi gane shi ba.







*Janafty*

[9/8, 19:53] Auntyna: *INZB3008*

*INZ IS A PAID BOOK PAY N500 FOR REGULAR OR 1K FOR VIP SECTION. VIA 0007468217 ZAINAB INUWA TAJ BANK,*
*09069067488*

https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC

No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba.


Mansor na tsaye a tsakiyar falon gidan tsohon Sanata Alhaji Hamza sulaiman Dabo. Hannayensa harɗe a kirjinsa, lokaci ɗaya yana nazarin falon, ya taɓa shigowa falon kusan sau biyu wani lokacin a can baya Mimi ta matsa masa ya shiga suka gaisa na farko rashin lafiyan Hajiya na biyu ya manta falilin.
A haka Daddy ya zo ya same shi yana tsaye bai zauna ba, yana ƙarisowa ya miƙa masa hannu suka yi masabaha.
Sannan Daddy ya nuna masa kujera ya ce ya zauna amman sai bai zauna ba sai ya zauna a saman tattausan cafet ɗin da ya malale fallon gabaɗaya saboda ya tuna wayar su da Mu'azzam yana hanyar tahowa nan ya yi ta hadadda masa ya je neman sulhu ne kuma surukinsa ne ya kamata ya nuna masa girma da daraja.

"Haba ka tashi ka zauna saman kujera mana."

Kan Mansoor na ƙasa ya ce"A aa nan ma ya isa Alhaji."

Sai Daddy bai ja ba kawai sai ya gyara zama suka gaisa yana tambayan shi wajen iyayanshi a sanyaye ya ce Alhamdulillah, shuru na wani lokaci ba daɗewa sai ga Anty ta shigo da farantin ruwa da lemu ta sauke nan saman center table ɗin dake falon, Itama Mansoor ya gaisheta ta amsa cikin sakewa kafin ta ce"Ah yallaɓai ya ka bar surukin namu ya zauna a ƙasa kuma?

Daddy ya yi mirmishi kafin ya ce" Biko ya zo shi ya sa ya ninka biyayyarsa." Tare suka yi dariya shi da Anty sannan ta fice shi ko Mansoor kansa na ƙasa domin sai ya ji Daddy ya yi masa kwarjini ya kuma rasa ta ina zai fara ma mganar, In hr Mimi ta faɗa musu dukkan abin da ya aikata mata ai da Kunya, Shi kuma Daddy nazarinsa yake yi ta gefen ido amman bai nuna ba, wata Jarida ma ya ja anan gefe yana karantawa kamar yadda Daddy ya yi masa kwarjini haka shima Daddy ya ga ƙwarjinin Mansoor ya cika falon gabaɗaya.

"Ka sha ruwan mana."

Daddy ya katse shi lokaci ɗaya yana kallon sa, sai Mansoor ya muskuta ya ɗan mike ya isa ga wajen ruwa ya saka kofi ya tsiyaya Kaɗan ya sha sannan ya ijiye kofin sannan ya koma in da ya tashi ya zauna. Shuru ya sake wanzuwa na wani lokaci kafin Daddy ya sake katse shurun da cewa" Ya wajen aikin na ku? Kwanaki abokanka da ƙaninka suka zo sun ce wasa gare ku masu yawa baka samun lokaci."

Sai ya samu kansa da amsawa da E, shi kuma Daddy sai ya jinjina kai kafin yac e"Good! Allah ya saka albarka," Aji ya amsa da Amin cikin yanayin maganarsa amman muryansa ta yi kasa sosai.
Gani ya yi Daddy ya yi kamar bai san dalilin zuwanshi ba, ya ma cigaba da karatun Jaridarsa lokaci ɗaya kuma ya na amsa waya in an kira shi.
Mansoor kuma na duke ya rasa ta in da zai fara dakyar ya iya kundunbalan ɗagowa ya na kallon Daddy kafin lokaci ɗaya ya fara da faɗin.

"Alhaji dama kan mganar Fatima ne.."

Sai ya dakata shi kuma Daddy sai ya kalle shi kafin ya ce"E, ina jin ka, Mimi ba ai ta dawo mana nan cikin kuka, ta ce ka ce ba ka sonta sannan ta ce za ta tafi ka ce is better da ta tafi ɗin, ni kuma da na ji haka sai na ce ai ba dole a cikin aure kuma in ka ga alaqa ta fara lalacewa gwara rabuwar shi ya fi alheri."

Mansoor ya yi shuru kafin yac e" Alhaji ni ban ce ta tafin da gaske ba"

"To me ya sa bayan ta taho a daran ko washegari ba ka biyo sahun ta ba, in ba ka nufin ta tafin ba?

Kai tsaye Mansoor ya gyara zama yana faɗin" Ina da dalilina Alhaji, saboda ka san su mata wani lokacin in ransu ya ɓaci gwara ka yi nesa da su su huce, na ga ranta ya ɓaci a lokaci to ba laifi ba ne domin ta dawo gida ta huta amman ba na nufin wai ta tafi saboda ba na sonta, in ba na sonta ai ba zan yarda na aureta ba. Kawai na bata lokaci ne ta huta sannan ta huce daga ɓacin ran da take ciki."

Magana ɗaya bayan Ɗlɗaya haka Manaoor ke fitar da ita, Daddy yana kallonsa amman yana mirmishi kafin ya gyaɗa kai ya ce"Na ji dalilin ka, ta wani fannin kana da ƴar gaskiyar ka ta wani fannin kuma ba ka da shi, amman duk ba wannan ba babban abin shi ne ga rashin ba ka sonta sannan ta ce ka kasa manta abin da ya faru a shekarun baya sai ka riƙa kallonta da abin, ka ga kuwa ai ba kyau irin haka riƙo ba shi da amfani sannan tunda har da bakin ka ka ce ba ka so ai ba wanda zai yi maka dole da sai ka zauna da ita ko ba haka ba?

Kan Mansoor Aji na ƙasa ya ce"E, ta nan kam ina da laifi, amman na gane kuskurena Alhaji a yi hakuri in sha Allahu hakan ba zai kara faruwa ba."

"Maganar rashin son fa? Ba zan ba ka bikon ƴata ba sai na ji gaskiyar mgana.*

Ya faɗa ya na ɗan haɗe rai. Sai Mansoor ya sadda kansa ƙasa cikin jin nauyi kafin ya ce"Ita ce ko a da, a yanzun ma ita ce har gobe da jibi ma ita ce, ɓacin rai ne ya sa na yi mata mganganu cikin fushi amman in sha Allahu hakan ba za ta ƙara faruwa ba."

Sai Daddy ya saki fuska yana faɗin" Alhamdulillah Allah ya sa na ji daɗin haka, ka burgeni yadda ka amshi laifukan ka sannan ka ce za ka gyara sannan na amince zan baka damar yin bikon matarka saboda dalilai guda biyu na farko ka yi laifi kuma ka amsa laifin ka, ka ba da hakuri sannan ka yi niyar gyara na biyu kuma na ji labarin ka je Abuja da kano ba ka samu ganinta ba hakam ma ya saka ni yarda da mganarka ta farko. Tabbas da farko da ta dawo gida da Koke koken cewa ita a raba auran ku in da ban yi zurfin tunani da duka rayuka sun ɓaci amman sai na bata lokaci kamar yadda ka ce itama ta sauka daga fushinta na tabbata a yanzu ba za ta so rabuwar auran ku ba sai dai daman an tauna aya ne domin tsakuwa ta ji tsoro. Sannan ina son na yi maka nasiha shi riƙo ba shi da amfani mu kasance ma su afuwa tunda Allah ma muma yi masa laifi, yana yafe mana kuma shi ya ce mu kasance masu afuwa, sannan shi kan shi Yaya Kabiru kafin rasuwarsa wallahi ya yi nadama kan abin da ya aikata maka kuma Hajiya da Brr. sun je sun yi mgana da kai sun kuma nema masa afuwarka sannan kafin rasuwarsa shi ya ce duk abin da Mimi take so a yi mata dalilin da ya saka aka yi auran ku bisa duk Sharaɗɗun da ka saka ka ga ba wanda ma ya maida kansa, To me ya sa kai ba za ka yi hakuri ka manta baya ba? Sai ka bar abu na shekaru ya hana ka sukuni da zaman lafiya? Shi kan shi Yayan ina yake yau ? Ai ba shi a duniya ya ma manta shi ya taɓa rayuwar duniya, ni ma ƙila ban sani ba nan kusa ne, wataƙila kaima nan kusa ne duk ba mu san gawan fari ba, sai fatan Allah yasa mu dace sannan ka sani Allah ya yi ma masu Afuwa wani babban tanadi, Ina ba ka shawaran ka manta baya don Allah domin samar ma kan ka da zuciyarka salama."

Gabaɗaya jikin Mansoor ya yi sanyi mganganun sun shiga zuciyarsa sosai daman kuma shi tuni ya saki wannan abun Sai ya ji kamar ana rage masa nauyin zuciya cikin jinjina kai ya ce"In sha Allahu komai ya wuce. na gode Alhaji Allah ya ƙara girma." Sai Daddy ya ji daɗi har ya nuna a saman fuskarsa ya kalli Aji Lokaci ɗaya yana faɗin" Na ji daɗin yadda ka saurare ni, da duka amincewata Mimi za ta koma ɗakinta, zan kirata da kaina na ce ta dawo amman sai ka same ta ku tattauna wannan kuma tsakanin ku ne ba zan shiga ba."
Aji ya rankwafar da kai yana godiya Daddy yace"Ba laifi. Na gode kwarai Allah ya yi ma rayuwa albarka Allah kuma ya kaɗe fitina a tsakanin ku."

Aji ya amsa da Amin Amin kafin ya zura hannu a cikin aljihun rigarsa ya zaro kuɗi bai san ko nawa ba ne ya ijiye a gaban Daddy sannan ya miƙe yana yi masa sallama Daddy duk da yana da rufin asirin sa amman ya girmama wannan alherin ya miƙe Lokaci ɗaya y na ɗaukan kuɗin kafin ya ce"Har da ɗawainiya? To yau dai zan ce na ci kuɗin ƙwallo kenan."
Mirmishi kawai mansoor ya yi ba tare da ya yi mgana ba Har haraban gidan Daddy ya rako shi, suka kara yin sallama shi ya koma cikin gidan shi kuma sai ya hau mashin ɗinsa ya bar gidan, yana tafe iska na kaɗa shi yana jinsa kamar ya na shawagi a sararin samaniya, sannan nauyin da ke zuciyarsa ya ji ya yaye, wani irin nishaɗi da farinciki ke shigar sa bai sani ba, Yana tafe yana Faman mirmishi shi kaɗai.


Daddy kuma yana komawa cikin gida Mama daman na falo tana jiran shi ya na shigowa ta miƙe tana faɗin" Har ya tafi? Shi kuma bai ba ma tambayarta wani muhimmamci ba ya ce" E."
Ya faɗa lokaci ɗaya ya na zama kan ɗaya daga cikin kujerun falon gefensa ta koma ta zauna tana faɗin" Allah sa dai ba ka ba shi fuska ba"
Kai tsaye ya kalleta kafin ya ce" wani fuskan kuma ? Na saurari bayaninsa na nuna masa Kuskuransa kuma ya karɓa ya ce zai gyara na kuma bashi izinin in Mimi ta dawo ya je su zauna su daidai ta."
Mama ta yi wani iri wanda har sai da rashin jin daɗin ya bayyana saman fuskarta.
Cikin mamakinta Alhaji Hamza ya kalleta kafin ya ce"Sai na ga kamar ba ki ji daɗin jin hakan ba ko?
Da sauri ta ce"Ba wai ban ji daɗi ba gani na yi yarinyar nan ita ta ce ta na so daga farko amman yanzu kuma ta ce ba ta so, kana ganin a tsaya sauraran shi ba ɓata lokaci ba ne? Sannan sam ba su dace da juna ba ji irin gidan da ya kai Mimi domin Allah fa."

Mirmishi ya yi domin shi ya gama gano in da ta dosa amman gudun ka ɗora ma mutun zargi ya sa yac e" To ba ki san tsakanin mata da miji sai Allah ba kenan? Itama a lokacin ɓacin rai ne amman tana son mijinta kuma ba za ta so rabuwarsu ba, mganar gida kuma ai ta san ra'ayin sa tun farko kuma ta ce ta ji ta gani, ba hurumun ba ne yanzu mu san abin da suka yanke ni dai na ce ya same ta su yi mgana abin d suka tattauna namu na saka albarka ne."

"Amman ba dai wanman gidan na su za ta koma ba ko?
Mama ta faɗa cikin yanayin damuwa a muryanta kai tsaye ya ce"Ban sani ba,ko ma can ne ko wani gidan ne can tsakanin su dai."
Sai Mama ta sauke ajiyar zuciya ba tare da ta yi mgana ba sai Daddy ne ya kalleta na wani ookaci kafin ya ce"Na san damuwarki kan Jaheed ne."
Da Sauri ta juya gare shi tana faɗin"Yallabai Yaron mu na son Mimi har yau ya kasa ba ma wata mace dama, bayan dawowan nan nata baka gq murnan da ya yi ba."
Dariyansu na manya ya yi kafin ya ce"Shi ma dai sakarai ne, mace da mijinta bai sake ta ba ne yake murna a kanta? Ke ce kuma ba ki ga ya masa gaskiya ba gwara tun da wuri ya hakura da Mimi in da ace tana son shi da ta zaɓe shi amman tunda ba ta iya zaɓarsa a baya ba yanzu ma ba za ta zaɓe shi ba, ki zauna ki gaya masa gaskiya Mimi ta haramta gare shi gwara tun lokaci bai ƙure masa ba ya nemi wata domin ba zan barshi ya tsallake shekaran nan bai yi aure ba."

Yana gama faɗin haka ya mike ya shige ciki ya barta zaune da tagumi, har Allah ta na jin haushin Hajiya domin ita taƙi ba ma Jaheed goyon baya in da tana so da Mimin ba ta isa ta yi gaddama ba, amman an na ce an ce sai abin da take so ga ta nan ga abin da ta ke so ɗin nan ya na wahalar da ita. Ranta ba daɗi itama ta bar falon zuwa ɗaakinta tana tunanin kiran ƙanwarta Hajiya Turai su tattauna mganar.



*******

*MIMI*

Lokacin da Daddy ya samu wayar Madiha wajen kwana uku da zuwan Aji wajensa ya na ta kiran wayar Mimi ba ya samu sai ya kira ta Madihan tunda suna tare, bayan sun gaisa ya ce ta haɗa shi da Mimi sai ta ce tana na ɗakinta in sun fito zuwa masallaci da yammah zata sanar da ita akan ta kira shi.

Wannan saƙon Madiha ta gaya ma Mimi sai ita kuma ta kunna wayarta ta nemi Daddy a waya suka yi mgana ba tare da wani dogon mgana ba ya ce" An gaya miki mijin ki nata zuwa neman ki baya samun ki?
Sai ta amsa masa bai ba ta samar mgana ba ya cigaba da faɗin" To daga ƙarshe dai ya zo ya same ni mun tattauna ya karɓi laifukansa ya ce zai gyara na ba shi damar ya same ki ku yi mgana kin ji ko?
Gaddama ba halinta ba ne ya sa ta ce masa in sha Allahu sannan ya ƙara da cewa"Yaushe za ku dawo?
Kai

20 / 49