Idan An Ciza Book 3 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Complete Novels

Chapter   10 / 49

27K to 30K   out of 146.6K words

bai ji ta ba ya shige ɗakin Inna wacce ke salla ta kosa ta Idar kada Baban inna ya ƙara jawo mata wata masifar, Maeesha bakin ciki ya rufe ta sai kawai ta saka kuka tana faɗin an takura mata ita da gidan Mijinta ba ta da halin sararawa Walida na gefe tana yar eariya daman matar nan ta gama cika mata ciki da iskancin ta a cikin gidan nan saboda ita Bintu ta daina zuwa gidan in ta ga abun magana sai ta yi mgana Kuma tana mgana sai a fara hayaniya Ita kuma Inna yar zaman Lafiya ce ita ta ce in fitina ke kawo ta itama ta zauni gidanta.
Maeesha ta yi ta kumfar baki tana tunanin Magajiya za ta fito amman shuru ita kuma Walida sai ta tafa hannu kafin ta ce"Sorry fa, ko shi Yaya Saddiqun ba zai iya da Yayanmu ba ballantana ke karamar alhaki."
Da haka itama ta nufeta gadan gadan kamar za ta murje mata hannu ya sa da sauri ta mike tsaye Walida ta shige ɗakin Inna tana faɗin" Ashe karyan tsiya kike yi."
Fuu Maeesha ta koma ɗaki tana kuka ta kira Saddiqu tana gaya masa karya da gaskiya har ta na faɗin Aji ya saka yakalmi ya taka ta kuma da gangan.
Shi kuma cikin Kumfar baki ya ce mata ai ya Kusa dawowa zai yi sharia da wanda ya taɓa masa mata daman ai ya na jin hauahin warning ɗin da ya saka Auwalu ya kira shi ya yi masa to wai shi da me ya ke takama ne?

A ɗakin Inna ko ta na sallame sallah cikin ɓacin rai ta kalli Mansoor kafin ta ce"Ba na son fitina. Ba na so ina zaune lafiya ba za ka jawomin wata fitinar ba, in kai ba ka san darajan matar ka ba, wasu sun sani kuma da gaskiyanta gidan mijinta ne a barta ta yi abin da ta ga dama mana."
Lokacin ya na wasa da Junoir ne wanda tun shogiwarsa a she bai yi barci ba ya naɗe masa. Sai ya kasa mgana domin kamar gori ne Inna ta yi masa.
Walida ce ta tura baki kafin ta ce"Shikenan Inna sai a barta ta rika mana abin da ta ga dama."
A fusace Inna ta ce"Sai me? Ai wuri ta samu ɗan da ka haifa ma bai ji mganarka ba sai wani can ne za ka damu kanka domin ka yi masa mgana bai ji ba."
Yadda Inna Meri ke mgana ne ya sa ya san ranta ya ɓaci kai tsaye ya ce"Ki yi hakuri inna." Sai kawai ya miƙe ya na faɗin"Inna ki ba ni Junior na tafi da shi wajena ya kwana."
Wani kallo mai kama da harara Inna ta sakar masa kafin ta kalli Walida lokaci ɗaya tana faɗin"Ke karɓe shi, "
Walida ta yi shuru kafin ta karisa za ta karɓeshi shi kuma ya makale masa sai ta Juya tana faɗin" Inna ko za ki bari ya tafi da shi ne, duba fa ki gani baya son zuwa."
Inna ba ta sake mgana ba ta miƙe ta warce Junoir a hannun Babban Inna yaron ko ya fashe da kuka Inna ta mikama Walida shi tana faɗin ta kai shi ciki ya kwanta.
Ta kalli Manaoor da ya yi kasaƙe kawai yana na kallon Inna komawa ta yi ta zauna lokaci ɗaya tana faɗin" Mu kwana lafiya."

Takaici ya kume shi cikin ɗan jin haushi ya ce"Inna ɗan Ɗan uwane fa?
Inna kai tsaye ta ce"E fa! Amman ai ba ɗanka ba ne ko ? In ka ji haushi ka haifi naka sai ka rika kwana da su."
Har ya dawo gidansa in ya tuna kalaman Inna sai ya ji kamar ya yi kuka wai shi Inna ke yi ma gorin Mata da haihuwa, takaici ya sa a daran ya Kira Mu'azzam y na gayamasa shi kuma ya nuna bai ji daɗi ba.
Sai kawai Aji ya ce" Amman ba komai, ta kwantar da hankalinta sai ta gaji da ɗaukan Ƴaƴa na"
Mu'azzan sai ya ji ya ba shi tausayi ya kuma san Inna ta yi masa hakane Saboda ya ji haushi ya gyara abin da ya ɓata kuma kamar hakan ya yi tasiri daga baya shima ya zauna yana tunanin shekaru sun tura ya kamata ace shima yanzu ya wuce wannan matsayin tunda har Inna ta fara masa gorin mata da haihuwa to nan gaba bai kuma san wa zai masa gori ba, ya fi su fa bukatar matarsa akwai abubuwan da suka faru ne suke danne wannan bukatar ta shi amman cikin ikon Allah da shawarwarin Nasir tun kwanaki ya fara yaƙi da abin d ke ransa kuma Alhandulillah yana jin abun na raguwa.

Duk iya yadda ya so ya share Mimi sai ta neme shi amman ba ta neme shi ba Sai ya ji ya kasa hakuri ana neman cin wajen wata ɗaya sai ya fara jin tsoro kada fa ya yi sakacin da zai ƙara jefa rayuwarsa cikin yarari a karo na biyu.
Ba shi da wani abokin shawara sai Mu'azzam Shi ya kira ya na ce masa" Mu'azzam kana ganin na bi Mimi Abuja ba matsala.?
Mu'azzam na mirmishi ya ce"Me zai hana? Ba wata matsala, ka kirata in ba ta ɗauka ba ka tura mata sakon za ka zo sai ku zauna ku yi mgana." Kamar wani yaro sai ya ce ma Mu'azzam Toh, Sai yayan na shi ya ba shi tausayi yasan yadda ya tsani garin nan amman ga shi yau zai koma kuma a kan dalilan nan guda ɗaya wanda saboda shi ya je a karon farko a wannan karon ma saboda shi zai koma.

"Don Allah Yaya Mansoor kada ka ce za ka mata yi faɗa,  ka lallasheta tunda dai kai ne mai laifi."

"Uhm!

Kawai ya ce daga nan bai ƙara mgana ba Saboda a lokacin yana tunanin ya je ko kuma kar ya je,  amman ya bi shawaran Mu'azzam ya ƙara Sauke kai ya kira Mimi amman matar nan ba ta ɗauka ba sai ya tura mata sakon ta tura mishi adireshin gidansu zai zo su yi mgana.

Lokacin da ta ga sakon shi matuka ta sha mamaki, wani gidan y ke nufi? gidan da ya ce Allah ya yi masa tsari ya ƙara takawa,  ba ta yi gaggawan tura masa sai da ta kira Rukky ta sanar da ita, ita kuma tana dariya ta ce" Na fahimci ba ma zai yi mana wahalan kamuwa ba, tura masa kada ki sake ki gaya masa wani abu."

Kai tsayen ta tura mishi yadda zai gane, An yi wajen kwana biyu ba ta kara ji daga gare shi har Rukky ta kira ta na gayamata ta ji Aji shuru Rukky ta ce zai zo fa ki kwantar da hankalin ki, shi ko tunanin tafiyar ne amman haka nan dai ya sauke girman kansa da wannan rikon da ya yi a ranshi a ransa ya kudurta ba zai shiga gidan ba sai dai ya tsaya daga haraba..
Bayan Mu'azzam ba wanda yasan zai je Abuja Jirgi ya bi zuwa can ranar wata Asabar da safe domin ko da sha ɗaya ta yi sun sauka a garin Abuja, a direshin ya nuna ma mai Taxi ɗin sai ga su har kofar gidan Marigayi Major Kabir Dabo dake anguwan Gwamrinpa.

Tsawon shekaru goma anguwar ba ta sauya masa a i do ba. Sannan gidan kan shi bai sauya masa, sama da mintina talatin ya na bakin get ɗin gidan  yana kokuwa da yanayinsa domin ji ya ke kamar a wancan lokacin ne da suka sauka shi da Mu'azzam kawai sai komai yake dawo masa daki daki kamar a lokacin yake faruwa ya yi tunanin ba zai shiga gidan ba, in fa ana son a samu masalaha har gobe ba zai daina ganin baƙin wannan gidan da mutanen dake cikin sa ba.
Wayarsa ya ɗauka ya kira Mimi abin mamaki wannan karon Mimi ta ɗaga wayarsa.

"Hello, na iso gani a kofar gida amman ki fito ba zan shigo ba."

Cikin yanayin maganarta tacce"Ni kuma ba zan iya fitowa ba, in ka na so in saurare ka sai ka shigo cikin gida."
A ransa sai ya ji daɗi da ya ji muryanta amman kuma yana tsoron wani abu da sauri ya ce" Kada ki sake ki shirya wani abu, domin na ga alaman kin sakani cikin dangin ku bangaren abokan wasan ki."
Dariya ta saki mai kayatarwa kafin ta ce"Kar ka damu, yi ma megadi mgana ka ce kai baƙo na ne."
Daga haka ta katse wayar ba karamin jarumta ya yi ba. Har sai da ya kai zuciyarsa nesa sannan ya iya tun karan get ɗin ya buga megadi ya leko sai ya ga yau kam ba Soja, wani dattaijo ya gani bayan sun gaisa ya ce masa ya zo wajen Mimi ne sai ya buɗe masa kofa ya shiga amman sai ya ce ya jirasa bari ya shiga ya sanar musu.

Yana bin haraban gidan da kallo, ba sojoji ba motoci ba iko ba komai sai haraban gidan wayam, Rayuwa kenan yana nan tsaye ya na kallon abun kamar yau yake faruwa Sanye yake da manyan kaya har da hula saboda Sumar kansa ta yi yawa kuma bai je ya rageta ba.
Megadi ya dawo ya ce Hajiya ta ce ya shiga ciki, kamar yace a'a sai kuma ya bi shi a baya shi ya yi masa jagora har cikin falon Gidan da ba abin da ya sauya a sanin da ya yi masa a baya sai dai an samu sauyin abubuwan dake falon.
Duk yadda ya so ya zauna kasa zama ya yi kawai ya yi tsaye hannayensa goye a bayansa ya na jinsa kamar akan ƙaya
Ita kuma Mommy tana cikin ɗakinta tana fa waya da Mimi domin ita ta kira ta ta ce Aji na waje ta saka a shigo da shi.
Mommy cikin faɗa ta ce"Au kin ma san zai zo shi ne ki ka saka kafa kika yi tafiyar ki?
Mimi ta marairaice kafin ta ce"Ni fa ban sani ba, yau yake gaya min."
Mommy ta san karya ne. Rana Tsaka shekaranjiya ta ce Kano za ta je gidan Dr da ta hanata sai ta yi mata karyan kwana biyu za ta yi ta dawo, kuma daman sun yi waya da Hajiya ta san da labarin zuwan shi can gidan da ta kira Alhaji Hamza ta yi masa mganar tun dai ya zo ya neme sa a sansanta lamarin shi kuma sai ya ce har yanzu bai zo gabar da nake so ba, in har yana son Sasanci tsakaninsa da Mimi ya san in da zai same shi.

Mommy ba ta fito ba sai da ta kira Asmau a waya dake ɗakin ta ta ce ta fita falo ta kai ma mijin Mimi ruwa da lemu a falo. Da to ta amsa mata sannan ta saka lulluɓi ta fita falon ta ganshi tsaye kamar yana kan ƙaya ba ta taɓa ganinsa ba sai sau ɗaya a wajen Kwallon da aka yi amman ta gane shi.
Cikin girmamawa ta gaishe shi ya amsa sau ɗaya kafin ya ce"Ina Mimin?
Sai ta yi shuru cikin mamaki kafin ta kalle shi cikin mamakin shi bai san Anty Mimi na kano ba ne?
"baka sa ni ba? Anty Mimi ba ta nan ta tafi kano."
Mirmishin gefen baki ya yi kawai domin in yace zai ɓata ransa ya rantse ds Allah sai ta raina kanta ya yarda ma kansa Mimi tana masa wasa da tunani da hankali.
Kitchen ta shiga ta haɗo masa lemu da ruwa da kofi saman faranti sannan ta kawo masa falon ta ja center table ta ijiye masa, Juya ya yi zai yi tafiyarsa sai ga Mommy ta fito Allah ba domin ta kira sunan shi ba so ya yi ya ficewarsa har shi za a yi ma Iskanci.

Dole ya dawo amman tsabar kamar akan ƙaya yake bai ko cire sahu cikin takalmin da ke kafarsa ba, daga gefe ya tsugunna ya gaishe da Mommy kadahan Kadahan ta amsa itama cikin yar sakewa kaɗan.

"Sannu da zuwa. Ba ku yi waya da Mimin ba ne? Ba ta nan tana Kano gidan Dr."

Kawai sai ya samu kanshi da cewa ya kira ta bai same ta ba, kai tsaye Mommy ta ɗaga wayarta tana faɗin" Bari na kira ta, ka zauna a kan kujera mana nan ma ai duk gida ne."
A ransa ya ce ban ga gida anan ba amman a fili sai ya yi shuru kansa na kasa ya ji Mommy na faɗin" Ya ce wayarki ba ta shiga, ga shi ku yi mgana amman ki tabbatar da kin dawo yau ko gobe."
Daga haka ta miƙe ta isa har in da Aji yake ta miƙa msaa wayar hannunta ya amsa ita kuma sai ta koma ciki lokaci ɗaya tana kwalama Asma'u kira.


"Wai ke a tunaninki wahala kike son ba ni?
Uhm ba za ki iya ba ni wahala ba Fatima, sai dai mu wahalar da juna."

Mimi ta yi yar dariya kafin ta ce"Sorry fa, na je duba matar ɗan'uwana ne."
"Da izinin wa kika tafi?
"Da izinin mijin da zai sake ni kwananan mana."
Baki ya buɗe kafin ya yi mgana ta yi saurin cewa" Shi ya ce in na ga dama na wuce  Abuja ma shi ya sa na tafi."
Kai ya jinjina ba tare da ya yi mgana ba Daga can bangaren ta ce"Ko za ka ƙariso kanon ne? Wlh ina gidan Dr."

Kasa ma mgana ya yi, domin ba shi da abun cewa dakyar ya samun bakin cewa" Ki sani dai akwai nauyin igiya uku a kanki, duk wani abun da za ki yi na saɓa ma mijinki Mala'iku suna rubuta miki, gwara ma ki sani ba ni kika yi nawa ba kan ki kika yi ma wa."
Daga haka ya kashe wayar kawai ya yi shuru ya na furzar da iska daga bakin shi,Da gaske ne Mimi ta fara bashi Wahala, da niyarsa ya yi tafiyarsa amman Mommy ta hana shi tafiya ta ce sai ya tsaya yq huta ya ci abinci sannan,  kuma kamar an rufe masa baki sai ya kasa yi mata Gaddama haka ya zauna a falon gidan su Mimi a ɗaɗare. Har Asma'u ta gama yi masa lafiyayyan fride rice da naman kaza an yi Pepe. Da farko ya so ne ko ruwa bai zai sha ba sai ga shi har abincin sai da yaci daman da yunwa ya fito ko karyawa bai yi ba. Ya kusa ma yin abun kunya kaɗan ya rage abincin sai daga baya ya riƙa jin haushin kansa.

Karfe biyu da wani abu ya baro gidan, Mommy ta jaddada masa Mimi za ta dawo kuma da kanta za ta dawo da ita gombe,  duk da bai wani saki jiki ba amman shi kan shi ya yi mamakin kanshi ko a tarihi bai ɗauka kafarsa za ta kara taka wannan gidan ba, sai ga shi a karo na biyu ya dawo saboda Mimi. Airport ya je ba jirgin gombe dole ya nemi hotel ya kama ya kwana da safe ya samu jirgin Gombe zuwa sha biyu na rana yana gidansa kwance yana tunanin Yadda zai yi ma Mimi rashin Mutumci in ta dawo ba dai shi za ta wahalar ba jiya ba har tana tura masa sako.

"Ya gajiyan tafiya? Mommy ta ce yau dai Aji ya ci abincin gidan Major Kabir Dabo. Na yi mamaki ƙwarai amman na ji daɗi. My ex husband."

Ko ba Ex ba haka ya rika maimaitawa shi kaɗai, wata zuciyar ta ce ko dai ta samu wani da take yi masa haka?
Zabura ya yi cikin ta shin hankali, saƙo ya tura mata tunda ba ta ɗaga wayarsa.

"In na sake ki kina da tabbacin akwai wanda zai aure ki ne a bazawara?

Tsakanin saƙon shi da nata mimtina huɗu ne ta turo masa da amsar da ya kusa barazanar yafiya da numfaahin sa.

B"E, mun daidaita da shi,  kai kaɗai yake jira mganar shi ta je wajen Daddy. Ya na sona sosai domin tun kafin na aure ka ya so ni, sai na zaɓe ka a tunanina kana sona sai daga baya na gane cewa na yi rashin masoyin ƙwarai da kaina na neme shi na bashi hakuri. Saboda haka ka sani aurena da kai ya ƙare Mansoor.
Ina jiran takardan saki na."
Fatima Kabir Dabo.

Wannan saƙon na Mimi kaɗan ya rage bai kashe shi da ranshi ba,Allah ne ma ya sa kwanan shi na gaba. Da gaske take yi ta nemi wani namijin? Lalle akwai ƴaƙin duniya na uku matukar akwai wanda ke ganin matarsa da sunan so.





*Janafty*


[9/8, 19:53] Auntyna: *INZB3006*

*INZ IS A PAID BOOK PAY N500 FOR REGULAR OR 1K FOR VIP SECTION. VIA 0007468217 ZAINAB INUWA TAJ BANK,*
*09069067488*

https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC

No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba.

*BAYAN KWANA HUƊU*

A cikin kwana huɗun da suka shuɗe duk a daddafe Mansoor ya yi su, duk yadda ya so ya fushi da Mimi kamar yadda ya so a farko tun bayan dawowar shi daga Abuja saboda ta ba shi haushi. Sannan tunda ya fahimci wahala take son ba shi ko ta yi ramako dalilin haka ya so ya share ta ya fita batun ta ya ga dai ƙaryan tsiya sannan kuma ya ga iya gudun ruwanta, shi ba ita ta fi ba shi baushi ba sai Iyayenta da suka zama tsoffn kawai suna kallon ta tana yawo gari gari da auransa a kanta amman a ka rasa mai tsawarta mata, ko ma me ya faru ai bai ce ya sake ta ba, ita ta ga dama ta yi tafiyarta shi kuma lokacin ransa ya ɓaci ba zai iya tsayawa yana ba ta hakuri.

Amman tunda ta tura masa saƙon wai

10 / 49