Author : NONE Category : African Stories & Novels
shida maheer da ibaad ammi babba ce kawai bata biyosu ba haka duk yaran suka rusuna sukayi gaisuwa akaci abincin cikin lumana da jin dadi, sede tunda mujaheed ya zauna banda tunanin maganan mamansa akan ayaanah babu abunda ya cika mind insa, saidai bai sano ba ayadda yakekan satar kallonta da wann burin aransa hakanan ma ubansa yake sakawa aransa aboye....
ana kammala cin abinci ba akira masu aiki ba su ayaanahn kawai ammi karama ta umarcesu akan da su kwashe komi sukai kitchen wa masu wanke wanke.
Dukansu hudun haka suka tashi suka kwashe saidai haryanxu safiya ce kawai agidan batama ayaanah magana snn koyaushe suka hade ido sai ta watsa mata harara mai zafi.
yaran suna watsewa ammi babba ta karaso tasako jan abaya ta caccaba fuskarta da kwalliya tazo ta gaida hajy mairo, nan aka bar zallan manyan gidan tare da zallan yara mazan kawai a tsakiya
da mujaheed, maheer da ibaad kowa kansa na kallon kasa ayayinda bappa zaidu yay dan fadakarwa da jan hankli akan karfafa zumunci da kaunar juna, shide uncle moh baiya cewa komi sai dai yay noding
har hajy mairo ta fara mata magana..itama nasiha ta musu me ratsa jiki, acikin salo mai sanyi tahau tunashesu yadda mutuwa ya ɗeiɗeita rayuwar yarta taawure nd how she is forced to run away witout her kids, tana magann tana kallon ammi baba tana cewa "Duk wata macen data walakanta yaran wasu a duniya toh tasani itama wata rana zata iya mutuwa tabar duniyan nan, kuma bazata taba sanin awani hannu yaranta zasu fada ba ..
duk dai ta gama wa'azinta tace musu tasan duk ita ce mai daura musu nauyi amma suyi hakuri duniyan nan ma nawa take da zaka zuba ido yaran wasu su lalace... duk dai ta musu waazi akan akula da taimakon juna da kuma mutanen waje. acewarta Allah ya basu daukaka da arziki ne badan su ci sukadai ba dan haka dolene su hada hannu ataimaka ma alumman dake neman taimako awaje.
duk wann wa'azika masu dumbin shiga jiki da akeyi a baibai ammi babba take fassarasu aranta.
take takawo tunanin ko har ammi karama ce takai gulmanta awajen hjy mairo wanda har yasaka aketa mata habaici akan yadda ta rike ayaanah .ita kadai sai hararar kowa takey, guilt nata cinta acikin zuciyarta har hajy mairon ta gama waa'zinta bappa zaidu da uncle moh suka fita duba wokers estate din atare dan su duba lfyar baƙin hajiya kuma dama sun saba sukanje ziyara da suka saba zuwa ran sundays wajen wasu tsofin manyan aminan mahaifinsu dasuke raye hr yanxu.
wasunsu sukai musu sadaqa wasu kuma masu mulkine da dukiya sune ma sukekan bude musu hanyar samun businss connection kala kala, dan haryau dan uwansu na ciki daya wato prof zayyanu babu ruwansa da taimakon uban kowa acikinsu inbawai a bashi zai musu taimakon ba.
ficewarsu bada jimawa ba ammi babba tabi anty safeera sashenta har uwar daki suka shiga bata zaunana ta dinga masifa tana zage zage tana tambayar anty safeerah wai ta gaya mata gaskiya kawai ko fatima takai gulman ta ne hajy mairo ta dage da wa'azi akan tausayi da taimakon yara da marayu tana kallon ta kamar da ita kadai akeyi..
babu bayanin da anty safeerah bata mata ba amma taki sam tace dole dole ammi karama ce tay reporting dinta, ahaka har saida anty safeerah taji dukkan wasu labarin kaf rashin mutuncin da ammi babban tama ayaanah
baki bude ta dinga kallon ammi babban jin wai har ankoret daga gidan miji duk akan ayaanah daga hmm sai hhmmm take amsa mata hirar dashi.
mujaheed da maheer suna dakin ammi karama sunakan mata kwadayin abinci, iyaka ibaad ne kawai akabarsa da hajiya mairon asashenta suna zaune su biyu
bayan har sun gama fadansu da suka saba, ya mugun hade ransa yahau zare mata ido yace mata shide kar ta sake kiran sunansa acikin mutane tanacewa wai ayaana matarsa ce dan bayason abunda da zaina jawo masa kananan magana da raini agidan nan
ita kuwa ko ajikin ta da masifarsan amma ta tubure iyaka ma tsokanarsa take kan karayi tana cewa bazata ma bashi auren ayaanahn ba koda kuwa yazo yana so daga baya
..karshe shiru kawai ya mata tanata tsokanarsa, har sai da dataga kamar bazai biye mata ba snn ta kyabe baki ta mike ta shiga dakin baccinta ta dauko wani takarda tana zuwa ta bashi snn tace masa taawure ne ta rubuta masa wasika ta aiko musu ranar da zasu taho.
Ajiyan zuciya ya sauke cikin dedeta makansa nitsuwa kai tsaye ya bude wasikar yay shiru yana karantawa har saida idanunshi ya tara ruwan hawaye bai daga ido akai ba harsaida ya gama karantawa tass
yafi 2 min idonsa na kallon rubutun harsaida yagama shanye ruwan hawayensa ciki snn ya nade takardan ya jefa aljihun wandonsa yay shiru baikuma ce komi ba.
hanklin hajy mairo duk ya tashi tabi ta zuba uban tagumi takuma kuresa da ido tanata jira taji ya hau mata bayanin abinda yake cikin wasikan dan ta samu na fashewa da kuka sai taga ko kallonta baiyi ba.
duk iya ture bakin datake baiko kulata ba face ma kara hade ransa da yay
kkrin mikewa yay kmr zai fita tarigasa mikewa da muryan raki tana cewa "a'a ah ah haba rayyanu meye haka, wai tafiya zakayi bamu gama magana ba? da wani irin deep voice yace "wani magana? tace maganan wasika manaz yanzu fisabillah sai inma dakon sako tundaga tudu kazo gabana ka karance shi tsaf shine kuma ni bazaka gayamin abunda kuke ciki da surkuwan naka ba.?
hmmm, to yau naji ikon Allah, nida yata taawure za'a nuna min izza akanta to ai kayi a banza, ni dakake ganin nan taawure fa bata boye min komi. cikin katseta yace"toh ai nasan da hakan ne yasaka bazan gaya miki ba, kodama can rainin wayo ne yasaka kikeso nakara miki bayani akan abunda already kika sani?
tace o, o oo..nide bance maka nasan wanann ba wnn ai tsakaninka ne da ita da yarta amma tunda bazaku sakani aciki ba ai shiknann dama ai naga ka iya raino..basai na tsoma maka baki ba.
komawa yay ya zauna yana kallonta yace "babu abunda zan gaya miki. maganin me son gulma kenan, bake kince dole saikinji kome ba?to wallah bazakiji wnn ba.
a mugun masife ta kalleshi toh ni karka dakeni wallah gidan ƴayana nake saina saka suma shegen duka..
yay karamin tsaki cikin saka serious tone yace yaushe xaki fara fita shagon naki.."tagumi tay kmr bazata amsashi ba tace" nan da sati biyu zuwa uku dan zaidu yace min ya gama komi, a cikin satin nan ma nakeso muje da du safeera da fatima da yaran nan sai muga wajen..da muryan kuka tace Allah dai ya ma zaidu da muhammadu albarka yaran nan suna dawainiya dani...
har zata kara fashewa da kuka yatare ta da masifa yace "haba ke kuwa hajiya ya isa haka mana kefa kinfiyeson kuka kina cikamin kunne wallah..
regardless of masifan daya matan ta kara fashe masa da kuka har takama bakin xaninta tana matse hawayenta dashi tana cewa toh shikenan sai bazan sakaalbarka wa yara ba? amfanin auren wuri kenan, inace kwanan kaima aka maka auren wurin a can majiya haka kazo kasani agaba saida aka kwance auren nan, amma da ba akwance ba danan da wasu yan shekaru yaranka zasu tashi suma su saka maka da dumbin alheri irin wnda zaidu yake min sai asnn zaka san menakeji araina yanxu
...kallonta yake kamr xai hadiyeta da harara ahnkli yace toh naji, sun kyauta, saiki mana shiru ko?
babu musu ta share hawayen tare da makalkale wuya tana kallonsa murya gwanin tausayi da salon yaudara tace ayya rayyanu yanxu bazaka gaya min abunda yake cikin sakon nan na tayaka kuka ba?inafa kallonka da gefen idona yadda kayi kifi kifi da idanu kmr zakay kuka kaima..
cikin lumshe ido da budewa yace bazan fada ba kinaji ko?kedai abu daya nakeso kimin ynxu, kinga session na schll yay nisa duk exms zasu fara upper week kuma ana bada hutun sati uku ne kawai. ki kira yarinyan nan pls kuyi magana akan karatunta, intana da wani matsala dake damunta tagaya miki saike kisanar dani dan wallah nasaka a schl taje tay wasa harke ma sai kinji ba dadi .
....da wani irin masiffafen ido ta tsaresa da harara baki bude tace ikon Allah toh wallah karya kakey rayyanu, baka isa ba kace harni bazanji dadi ba, akan me? ubana ne kai? kaifa
duk wani muguntan ka ya kare akan yaran nan amma ni mairo yar gidan malam nafi karfin ka.
mikewa tsaye yay yana kyabe baki har saida ya tsaya snn ya kalleta da gentler tone yace hajiya i am serious abt this, pls u need to have this cnvrsation with her as soon as possible, ni bazata gayamin wasu abubuwan dake yawan damunta aranta ba, amma nasan ke xata iya gaya miki komi kinsan kuma bazaiyu bata gama warwarewa daga grieve ba atura schll.. ask her throughly dan Allah...kinji yar kyakkwan hajiyata?
yadda yay maganan da salon sanyi da yaudara yasa ta amsashi batare da gardama ba haka kuwa har yafice a sashen bai gaya mata abunda yake cikin wasikar ba.
******
bayan kamar kwana biyar kusan duk wani doki da marmari da akey na zuwan hajya ya fara gushewa, ayaana tun tana dar dar agidan har soyayyar datake samu ta kowani angle inta juya yasa ciwon ta ya fara mancewa da ita cos ever since ta dawo family house is always fun nd lovely moments.
haryau anty safeera tana mata kirki sosai tanajin dadi da suke kwana da kulthum a dakinta. musmn ma da taga ammi karama batace komi ba ta kyalesu, sabida ita kanta ammin tanasone ayaana ta zama tana cikin companyn yan uwanta mata da zasuna debe mata kewa. acikin mazajen gidan maheer ne kawai ta lura kamr ya canza mata kadan, dan insunzo gidan gaisawa kawai sukeyi talura kamr anan gidansun yafi bada kulthum kulawa amma bata wani damu ba cos mujaheed is all over her ever since dat day daya ganta kowani safiya shiyake xuwa ya tashe su bacci, tun yanakiranta da "softie" bata amsawa har ta haqura ta fara amsashi sabida tsabar son wasansa da saukin halinsa da kirkinsa da yadda taga har safiya ma tana balain son sakewa da mujaheed din sosai.
kullum da yamma yana zama a falon su haka dukansu zasu fito su mamayeshi suyita masa surutu yana basu game suna bugawa yanamusu kyautar kudi
gidan was fun for ayaanah, ga samun kulawa ga soyayyar kowa da kowa, wanda har saima taje wajen hajy mairo ne take iya tunowa da raywarta na baya, abu daya ne kacal ke yawan tada mata hankli,wanda shine in arana bataga ibaad yaxo gidan ba, amma daga ance mata yaxo kuma toh shikenan sai taji sanyi duk dama baifiye son janta jikinsa yanxu kamr dacan ba.
cikin kwanakin nan babu yadda anty safeera batay da uncle moh akan batun saka fuskar ayaana akan brand inta ba amma yaki mata sam, saima bata kudi dayayi me uban yawa wai saidai tayi investing wajen kara bude wani wajen koyarda makeup sabida idan su ayaanan sun kara girma shidakansa ma xai biyata kudi tana koya musu yadda ake kwalliya da saka kaya.
ita duk bata dau hakan akomi ba murna ma tay dake taji duk kudin goro yay ma yaran bai ware ayaanan ita daya ba,
daga cikin ransa kuwa tanadi kawai yake kanyi makansa yana so lallai safeera tazama itace zata koya ma future wife dinsa kwalisa da kwalliya irin wanda ta iya sosai. ita kuwa tunda ta caske kudi tabi ta mance da zancen fuskar ayaanah and she focuses on building the brand ,in ya tashi yay suna shikenan sai ta fara bude classes din kamar yadda ya fada.
time to time su ibaad suke xuwa ammi babba kam tun ranar da aka musu nasiha taji haushi bata kara zuwa ba kullum kuma hanklinta tashe yake dake kowani safiya ya zama kamr dolene ya zame ma mijinta yana zuwa family house yana duba mahaifyarsa, ita babbann dsmuwarta ba gaisuwar bane baifi yadda zaina kallon fuskar fatima kullum da safe inyaje gidan ba
ahujajan tafara tunanin yadda zatay maza maza adawo da hajiya gidanta, tunda akwai sashe na musmn da ake mata agidan itama
ranar da hajy mairo ta cika kwana bakwai da dawowa birni dukan matayen gidan suka shirya sukaje aka dudduba sabon shago
luxurious traditional local food spot ne da aka narka naira wajen kerashi yayi shegen kyau harma fiye da yadda kowannensu yay tsammani. akwai sashe sashe, da food nd drink compartmt kala kala inda ake saida abincin gargajiya a zamanince, dana zamanin ma da kuma inda akeyin chops da local drink harda tea spot ga wajen barbaque..
sabbin maai'katanta kowa da sabon unform dinsa dark blue nd white colour, iyaka manyan wokers din sukanxo ayita prep ma kananan harda su ruthy acikin wanda ake horasu, duk dai anata shirye shiryen budewa tare da grand openin ceremony next week sunday, sun bada kudade a manyan SM blogs anata musu social media makerting promotions da sauransu, ga office din ceo hajiya mairo me tuwo babba harda lumtsa luntsan kujerun zama, waje dai masha Allah, kowa yay mata murna suka dan dauke hoto as usual ammi babba ne kawai acikin matan bata zo wajen yau ba
dakyar ruthy ta rabu da su ayaanah sabida sukadai kawai ta sani a kano ynxu, duk tabi ta damu musmn ma dataga ayaanahn harta samu masu debe mata kewa sosai. tun anan tay ta rokon ayaana akan taroki hajiya kawai suyi aikin restaurant din atare, wanda tun ayaanah tana ja baya hartace mata xata ma hjy magana
da yamma suka dawo gida can bayan angama cin abincin kowa ya watse ya kwanta
sassafe bayan sunxo gaisuwa ayaana taxo ta lafe ajikinta tanamai sanar da ita yadda sukay da ruthyn akan aikin restaurant..
hajiy tace au har kin gama warkewa kinaso kiyi aiki ko?? da sanyin murya tace mata "ai satin nan sulthana zata tafi gidansu, kuma kulthum tana xuwa makarnta data zauna ita daya gara itama tana zuwa shagon.
cikin kyabe baki hajya tace toh ayaanaj nide bazan hanaki aikin nan ba amma fa dolene sai in ibaad yaxo nagaya masa ya amince.. sabida kinga ahannun mu dukanmu ni dashi uwarki ta mikawa amanar rayuwarki ban isa na yanke miki hukunci nikadai ba.
ayaanah tay shiru batace komi ba, itama hajya tay gum bata gayamata sakon ibaad din ba dan aganinta ai tunda ayaana ta fara tunanin aiki a shago to hala taji lafyarta kalau kenan.
ranar asabar na satin ma zagowa hakanan kowa yaxo family house wekdns yauma asashen anty safeerah zainab arifah yau ta wuni, wani irin xpensive human hair taje ta saka mai tsayi kuma baki kirin irinna ayaanah dan itama tay kyau ta burge kowa dan har ynxu batasan cewa gashin kan ayaanahn natural bane ta dauka duk fixing mata shi akayi dan ta kara kyau
taxo da jiji dakanta saidai tunda taje dakin mujaheed taga gifts din expensive turare da watch data bawa ibaad duk sune akan madubin MJ sai taji ranta ya sosu sosai abun bai mata dadi ba
gashi bata iya boye emotions dinta ba kusan wuni tay dashi
a dakin tana jero masa hilimin complain akan attitude in ibaad musmn yadda yake basar da ita, snn duk abunda ta bashi sai taga yay kyauta dashi
sosai mujaheed ya tausaya mata ganin tana maganan har tana hawaye, gata da wani irin raini dan gane take kmar ai bawani shegen ratan shekaru bane tsakanin su da ibaad din dahar yake jan mata aji haka sosai, shikansa MJ yaji babu dadi, dan harga Allah dayasan cewa special lovers gifts ne atsakanin su kuma ibaad ya dauka ya bashi da bai karba ba
babu irin lallashinta da baiyi akan ta karbi abunta shi baiso ba cikin jin tafi karfin tay kyauta adawo mata dashi taqi sam tace masa ya rike kawai hala rabonsa ne
wkends din gabaki daya bai ma zainab arifah dadi ba gashi yau bata samu cikakken dman magana da ibaad din bama bare ta nuna masa bacin ranta har yamma yay aka watse kowa ya wuce gida
washe gari sunday gidan yay wani irin shiru lokacin kowa yana dakinsa duk any sallahn su ayanah kam har ankoma bacci.. at around 6.30am ibaad yazo gidan, bappa zaidu ne ya aiko sa ya kawo ma ammi karama wasu files daya mata aikin review akai na foundation inta, har ya shigo gidan babu wanda ya sani kai tsaye yana zuwa sashenta ya samu bata nan da sauri ya dawo sashsn hajya mairo yakuwa samu suna zaune suna shan shayi atare sunata hira kamar uwa da ya.
ibaad yay sallama da ladabi ayanayinsa ya tsuguna ya gaishesu snn ya miƙa mata aikan tareda ce mata yana sauri zai koma gida bappa yace yaje yadawo yanxun nan.
duk da ya ambace hakan bai hana hajya dakatar dashi ba.
tace sam ya zauna tunda su uku ne anan zata musu magana ne akan rayuwar ayaanah
adan dolensa ya nemi waje ya zauna duka suka zuba mata ido tanata kame kamenta wai tana jin tausayin rayuwar ayaanah kai harta fito mai fili da maganan cewa ai ayaanah tace mata tana son tay aikin restaurant da su ruthy.
duk tay tunanin dayake mata tambayoyi cikin lumana akan hakan agaban mahaifyarsa bazai masifeta bane
tunda ta furta masa cewa aima batama ayaanah zancen schll din ba ya hade rai ya hau balbaleta yace kawai tace masa zata daure ma ayaanah gindi takiyi makarnta taje mata talla sabida abunda ta saba dashi kenan acan
yayita mata masifa tay shiru tana ta kallon uwarsa koda zata saka baki ammi taki cewa komi ta kyalesu
duk bayaninta yaki ji ya bata ransa yace sam bai Amince da zancen nan ba, kuma kartama kara cewa ayaanah zata mata aiki a restaurant kawai karatu zatayi, snn inhar ayaanah taki yin karatun toh wallh shi dakansa zaikai kararta wajen su bappa zaidu zaice itace ta zuga yarinya tay tallaa taki yin karatu...yana masifar hajiya mairo duk bakintan nan haka tay shiru ta zuba masa ido
irin seriousness dayasa ka akan maganan har saida taji dama bata gaya masa haka ba, da kuma haushintan ya kama hanyarsa ya fita bata sake ganin kafarsa a gidan ba.
ata fanninsa kuwa daren ranan tunani kawai yay