Author : NONE Category : African Stories & Novels
magana bane, kituna dake kawai na dogara dan ranar da mahaifinku yasan nasakaku kuna karatu a tudu zai iya kasheni ko ya batar dani, innari kece mini, nasan zaki zama karfina anan gaba, nasan koda na mutu kece kawai zaki iya rike ayanah tsakanin ki da Allah koda bana duniya, in nabari yaxo ya tsine miki yau ni aka cuta duniya da lahira, kawai kije ki cigaba da karatunki a tudu, nayi miki alkwari bayan ya huce daga fushinsa, zanzo saida nono wata sati zan dawo dake gida, snn nayi alkwakri wnnan karon da kaina zanzo da anayah tudu itama ta cigaba da karatunta acan naji ance anyi mata nisa kudin natan ne bangama tarawa ba. tun kan innari ta amsa idanunta ya cika da ruwan hawaye ganin yadda jikin mahaifiyrsu yake bari sosai yanayinta cike da fargaba me ban tausayi da tsanani.
marmaza taawuren ta warware bakin zaninta ta ciro kudi da basu fi dari biyarba ta damka matasu duka a hannu tace" kirike wnn inkinje tudun kice ma goggo mei tuwo ina gaisheta, har da ma malaminku. ki kula da kanki Allah hokku barka am. inayah ta kasa cewa komi ganin yadda hankli da jikin mahairfyrsun gabaki daya yarikide dukkan hanklinta atashe yake sai leke leken waje take da tsoro daga ganinta kasan tana mugun tsorone kar ace juma ya dawo ya iskesu anan atare dqn bakaramin son yaranta takeyi ba.
hawaye kwalli daya ya sauka idon inaayah musmn da ta daga ido ta kalli mahaifayarsun snn ta kalli ayaanah dake kan kwance a tabarma ta kanannede kanta bata iya ko da motsi sabida jikon da aka bata tasha tuni ya sakata bacci..
tawuree na jan hannunta da kyar dai ta iya dauke idonta akan yar uwarta suka fice waje suna sauri sauri haka ta rakata har gaban babban rafi ta turata bisa hanyar tudu, ita kuma ta damke kayanta snn ta falfala da gudu tabi jejin, saida taga tay nisa snn ta dawo gida
taqumi tay ta zauna kurkusa da ayaanah dake kan bacci wasu maqudan hawaye na zuba mata ahnkli cikin tunanin safetyn yarta inayah, harcan saida aka kira sallan magrib snn ta tashe anayah sukayi marmaza sukayi sallolinsu suka ci abinci wanda dede lokacin ne aka taso daga wajen wasa...
fitila me kwai kawai ta kunna musu tay shiru tanajin ayanah tanata bitan karatun da addarta inayan ta koya mata game da sallah , tun suna zaune acikin dar dar din ganin shigowar juma gidan har dai suka hakura.
washe gari da asuban fari sukejin labarin cewa ashe baram baram aka tashi a filin wasa, sarkin buzaye dakansa yay jawabi akan tarbiya, yana mai kafa misali da rashin kunya da kuma tarbiya irinna inayah dahar ta karbi sanda a hannun namiji a filin wasa, dan haka tun anan juma maharozau yayi zuciya, sabida ance masa ya haifa musu y'ay'a mata marasa amfani ga cigaban kauyen snn kuma bai iya tarbiyatan dasu ba, acewar sarkin fulani in har innari ta sake musu tsaurin idon karban sanda a hannun namiji a fili zai saka matasa maza su giciye ta.
wayannn furucin yasaka juma tsananin fushi, bai dawo gidan sa ba ya wuce jeji dan tsabar zafin zuciya ma akan wata bishiyan mangwaro ya kwana
jin hakan bakaramin kara tsorota taawure yayi ba, dan tafi kowa sanin mugun zuciya da tsananin rashn son kaskanci irinna mijinta juma. dan da a raina mazantakarsa ko aci mutuncinsa a fili gara a maresa a fuska.
Juma Maharouzo ba asalin ɗan Dajin rini ba ne. Kakanninsa sun fito ne daga ƙauyen Maharouzo kusa da iyakar Tamesna wato yankin da ke tsakanin Nijar da Arewa maso Yammacin Najeriya.
Sunan “Maharouzo” ma ya samo asali daga tsohon harshen Tamasheq wanda ke nufin “ɗan ƙura, mai ƙarfi a ƙaura”. ance Kakan kakansa bbn malamin addini ne wanda yayi suna wajen tafsiri da bayar da fatawowi musmn ga ƙauyukan kan iyaka amma babansa kuma jahili ne dake bautawa al'adarsu. yaki neman ilimi ne saboda kakan juman adacan ya ki shiga cikin yaƙin sarakunan Fulani a lokacin jihadin Shehu, sai aka koreshi da iyalansa daga garinsu. Sun yi hijira, suka shigo cikin karkarar Katsina duk ba'a kyale su ba, daga nan suka ratsa zuwa Rini inda aka basu ƙaramin fili don su zauna, Saboda haka shida ya taso sai baibi tafarkin ilimi ba har ya haifi babban dansa juma a maharazou cikin jahilci da tsananin son al'ada..
Juma ya taso ne da ɗan tsakanin ƙabilu biyu, akwai al’adun Hausa fulani a jikinsa, amma shi asalin Buzu ne tsatson su na Tuareg har a halayyarsa. shi mutum ne mai ɗaukar hankali koda bai yi magana ba, Fuskarsa tana da faɗi, idonsa yan dede masu zurfin haske, daga saman Goshinsa akwai wani dogon tabo mai layi guda biyu wanda labarin tabon nan shi kansa yana da ban aljabi, dan ana cewa a lokacin ƙuruciyarsa ya tsallake dajin mutuwa lokacin farautar wasu macizai, wasu kuma sunce yabuge kansa ne da itace wasu na cewa alamar ruwan gadon hatsice daga kakanninsa shiyasa noma ta amshesa
Dogon mutum ne mai lafiyayyen kafadu masu faɗi, gashin kansa baƙi, gashin gemunsa kuma ya fara tsufewa. a sutura Ya fi son dogon riga mai launin ƙasa ko shuɗi, da rawani mai kauri wanda yake nadawa fiye da yadda maza kauyen suke yi, shi baida hakuri sam, kuma zuciyarsa akusa take, babu abunda yakeso aransa kamar al'adarsa, babu kuma abunda yafi ci masa tuwo a kwarya kamar haifan yaya mata dayayi, dacan sai kaga kamar yana mutuwar son matarsa taawure amma tunda ta haifa masa mata banda wutar tsana da tsangwama babu abunda ke shiga tsakaninsu. already ya hana yaransa komi na nishadi, da amfani, daga aikin gida, talle sai kiwo, baya basu kulawa, ko ciwo suke an haramta musu shan maganin da addini ta amince dashi, saidai uwarsu ta jika musu magani na asalin malamn gargajiya susha, snn ba a karatu kowani iri a gidansa, ya hana zuwa asibiti sabida shi asalin al'adarsu ba jahilcin garin yake bi badon komi ba sai dan kawai yaga shima ya zama me fada aji snn ya samu shiga a fadan sarakunansu both fulani da buzaye ana darajashi kamr sauran zaratan maza.
Kamar ko wani zagowar shekara yauma al'adarsu ta bikin gangamin gwaninmta baima Juma maharazou dadi ba. tun safe taawure taje jejin tana rokonsa, hakama wasu Maza abokansa Wanda sukadan damu dashi a garin sukazo babu irin rokonsa da basuyi akan yay hakuri ya sauka akan bishiyan nan ya koma gida ba amma inaaa, yaki magana da kowa yay zuciya harda abinci.
wasa wasa saida ya kara kwana washe gari taawure ta fita tanabi gidan dattijai tana magiya dakyar akazo aka tallafosa ya hakura ya sauko ya koma gida, yunwa duk ta watayashi sanda ya sha kuna yay wanka ya dawo hayyacinshi, tsabar zuciya haka bai magana da kowa agidan ba, har saida da yazo yaga babu wulgawar innarin agidan snn ya dan sake ransa, dama kuma mugun tsoron sa ayaanah takeji bata sakewa suhade ido ko su hade hanya in zata gaishesa da sanyin asuba take fitowa ta bi taawure itama haka za ta durkusa ta sunkuyar da kai can kasa a kofar turakarsa tay shiruuu koda taawure ta gaishesa daga nan waje ya amsata cikii ciki, ita shiru takeyi inbe amsata ba kuma komin jimawar da zatay a tsugune haka zata kasance har sai ya fito daga dakin ya ganta snn take iya tashi tabar wajen.
#SURAYYAHMS
AYI SHARING idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata
*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*
*WATTAPAD @SURAYYAHMS*
*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*
#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
#SURAYYAHMS
[22/10, 19:02] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*
⏯️3️⃣ Duk zafin zuciya da taurin kan inayah tsanar dayake mata baikai wanda yake ma Ayanah ba, dan akanta ne yafara samun rugujewar burinsa na samun ɗa namiji sabida shi dakyer ma yake iya samun haihuwa. a kauyen mutane da yawa sun haifi mata a fari saidai abinda yake biyowa baya maza ne, shima sosai yaci burin ace ayanaah tafito masa a matsayin ɗa namiji sai kuma ta fito mace kyakkwan gaske kuma me dauke da ciwo na raunin zuciya wanda saida aka sha wahala ma kafin ta rayu.
ranar koda aka cemai mace aka kara haifar masa tsabar bakin cikin dayaji aransa ko daukarta as a baby a hannunsa bai taɓayi ba,he despises ayanah ryt frm the very minute she was born dan haihuwarta ya jawo masa ababen gori bana kadan ba shiyasa har yau kuma baijinta aransa dan banda hantara, tsawa da tsananin dokoki babu abunda ke giftawa tsakaninsu.
yau shekaranta goma amma bai taba amsa gaisuwarta ba, kowani safe saidai tabiyo bayan mahaifiyatta cikin nuna biyayya haka zatazo ta durkusa masa abakin kofar turakarsa ta tsunkyar dakai kasa tay shiru bata kuma tashi awajen har saiya fito yaganta duk dama tasan bazai taba ce mata uffan ba.
bayan kamar sati da faruwan komi taawure tasha baqar walaknci da baqar magana a hannun juma kafin ya sassauto ya hakura har ya fara shirin tafiya zuwa boaden kasar niger saida sabbin buhunansa na hatsi, yana da akalla buhuhunan kayan noma kala kala yakai buhu dari da ashirin banda yan kananan abubuwa daya tara.
kullum matarsa taawure dake tay karatun allo sosai ita take tayasa lissafin irin uban kudin da zai samu duk dama baiya bata ko asi, dan gani yake tunda ita ta taba yin karatun addini me zurfi hala zata cuceshi
abinci kam kowani iri ne yana sakar musu suci su koshi amma bayan haka sisinsa basa ci. sanadiyar yar lissafin kudin datake tayashi sukeyinsa a kwana biyu yasa hartaci nasarar kawo masa batun yafewa innari, ranar haka ya zage ya gaggaya mata bakaken maganganu masu tsanann zafi da ciwo wanda ko wacce uwa bazataso taji an furta su akan yayanta ba, ya mata gorin tarbiya, yace mata yana ji ajinin jikinsa cewa watsatsstsu karuwai kawai ta haifa masa ba ƴaƴa ba, wanda yake da yaqini cewa sune zasu kawo zubewar duk wani kima da darajarsa a duniya.
sam maganan nan bai ma taawure dadi aranta ba dan bataso yay musu wnn mummunan bakin ba
hakanan tay hakuri sabida ya yafe kuma ta shawo kansa har ya amince akan inayahn zata iya dawowa gida, maganarsan ya mata ciwo aranta amma tanada yaqinin cewa Allah bazai tozarta ta ba tunda har tanata kkrin neman ma yaranta ilimin addini dana boko aɓoye in sha Allah bazasu taba zamowa karuwai watsatssu ba.
duk dama ta aminta da mutanenta na can tudu amma koda juma yay ma yaranta wnn mugun bakin sai kawai tafara jin kamar tafiso ace ita dakanta ne ta tarbiyartan da duka yaranta agabanta kafinsu samu mijin aure basai sunje university ba duk ma babban burinta kenan.
satin nan gabaki daya haka ta tasa ayanah agaba suka hau shirya madara, da kindirmon nono da fura da kwan zabbi masu kyau da yawa, sunata Allah Allah lkci yay juma ya wuce kasuwancinsa a bodar niger dan suma suje nasu kasuwancin a can tudu.
kwanaki basa karya yau kwana sha biyu shaf da gama hidima gangamin jarumai juma da abokanansa duk sun gama shirin tafiyarsu can boadern niger kasuwancinsu da suka sabayi ko wata shekara.
ranar da zasu wuce tun da asubahin fari na farko lkcin waje baigama washewa ba taawuree ta fito daga turakarsa da lullume tare da daurin kirji tanadan murmushi me sanyi tuna irin darensu na jiya.
mijinta juma yana iya walakanta ta akan komi amma daga zarar anzo maganar saduwar aure baya iya boye dumbin soyayyr dayake mata aransa dan bakaramin dadin ta yakeji akan gadon sa ba, albarkan niima da dandano dake kumshe a jikinta yana kawo masa wata iriyar cikakken gamsuwa da nitsuwa a duka sassan jikinsa tareda dadi marar misaltuwa, ruwa me tsafta ta hau zuba masa a babban butan karfe wanda take tsammnin zaiyi wankar tsarki dashi tanay tana murmushi badon komi ba saidan amince mata dayayi akan basai ta zauna anan ba, zai saka musu mai gadi inyaso itama tazauna acan anguwar tudun tay kasuwancinta na saida kwai da nono har saiya gama nashi cinikayyar ya dawo. hakan kusan babban alfarma ya mata.
lissafin wata ukun da zaiyi a boda tay, tasan kafin nan ya dawo ta samu kudi me yawa na kulawa karatun yaranta hala har ayanah tay nisa akaratunta itama.
babu yabo babu fallasa juma ya gama shirinsa komi ya fito, ta rakosa har waje yay kyau sosai yasha baƙar rawani, wanda yau da ace bai kara jadadda mata mugun harsashen dayakeyi gameda da tarbiyan yaransu ba da sai tace cikin dadin rai suka rabu amma inaa saida ya kara jadadda mata cewa yanaji ajikinsa cewa yaransa kaf karuwai ne...
haka ta dinke zafin maganar aranta har sukayi sallama dashi snn ta dawo gidan, bayan kamar kwana daya da tafiyarsa mai musu gadin rugarsu ya taho, ita da ayanah kuma suka shirya suka tattara kayan cinikayyarsu da kayan sawansu suka kama hanyar anguwan tudu ayayinda zuciyar taawure ke cike da tsananin damuwar irin mugun baki da fatar tabarbarewa da juma yake ma yarantan aranta. ayanah kuwa murna takeji anata ran tana Allah Allah taga har su isa anguwar tudu dan ta saka yar uwarta inayah a kwayar idanunta.
Basu da isa cikin anguwar tudu ba sai can can gabanin sallahn magriba sabida biye biyen wasu kananan anguwanni dake bisa ahanya da táawure tay domin saida nono da fura dan ta samu ta cike shauran yan kudaden makaranta na ayanah da ake binsu bashi, suna samun kudaden su suka doso masaukinsu, sun iso kofar gidan goggonta Hajy mairo metuwo lkcin duk sun galabaita sakamakon tafya me nisa da suka sha musmn ma ayanah dake fidda nunfashi sama sama sabida wann ciwon raunin zucya datake fama dashi..
Anguwan tudu kamar bariki ne, is more busy and civil Kamardai wajen kazo nazo ne amma dake yana nesa da garin kano duk kabilu irinsu hausawa, buzaye, katsinawa, kanurai, iyamurai, da fulani asalin irin kauyawan ne ke cin kasuwancinsu anan kowadai yana harkan gabansa .
adaf da gidan sarkin kasuwar tudu gidan goggon taawure yake,
dake shahariiyar Me sana'ar saida Abinci ne agarin, hatta bako inka tare shi a hanya kacemai gidan hajy maituwo zakaje zai iya nuna maka shi kai tsaye dan ta balain shahara wajen iya sarrafa abinci da abun sha kala kala da kuma saidawa, lafyayyar hajiya ce shekarunta ya dan jaa amma tay karatu wayayya ce, tun zuwa makka na naira dari hudu tajeta ta sauke farallinta yakai sau biu zuwa uku, tana da ma'aikata dake aika a rumfar abincinta dayawansu yan mata ne datake daukar nauyin karatun su, sai maza dake mata gadi da sauran abubuwa kmar aika da aikin karfi, itake rufa musu asirinsu kaf ta zame musu tamkar uwa da uba.
Tun a kofar gidanta suka sauke kayansu akansu, taawure na tafiyarta a hnkli cikin tsantsar nitsuwar dake tattare da yanayinta na mace mai kamala wanda babu shakku ko dar dar atattare da ita.
Tun a zauren farko take buga sallama cikin nutsutsaiyar sauti yarta ayanah na biye da ita har suka wuce can ciki ta Inda masaukinsu yake bata fasa sallamar ba, ayanaah kuwa tuni ta bude randa ta hau gwangwadar ruwan sanyi wai koda nunfashinta zai dawo dede, Adaf lokacin inayah ta idarda bitan karatunta kenan tana daga xaune akan wani darduma ta fara jiyo motsi tareda sallamar taawure, da wani irin sauri ta fito tun basu gama hade ido da ummanta ba ayanah ta jefar da kofin ruwan ta daka tsalle da murna ayanayinta ta taho da gudu ta rungume addanta inayah sosai, ahnkli inaya tace "annayo? baki washe ayanah tace naam adda na muma gamu ai munxo tudun. inaya tafara dariya tace" aito shannunku., tun basu gaisa ba ayanah tahau kkrin cikata da surutai musmm ma labarin samun karashin sauran kudin makarantarta da sukayi kan hanya wanda atake yasaka zuciyar inaya yay dadi da sanyi dan tasan tunda har anayah tana cikin tsananin farinciki to hala komi ya daidata ne harma awajen mahaifinsu juma
Tanakan murmushi ta janyota jikinta sosai tana share mata zufa tana cewa"toh ya isa haka anayo, Zo muje can wajen ki wanke sawunki kikalle yadda kikay futu futu da kura kamar delu me wasan kasa..anayah da bata wani damu ba sai washe baki takey yanayinta me cike da xumudin ganin addanta ga kuma batun komawrta karatu dan bakaramin son karatun boko takeyi ba.
suna kkrin barin wajen taawure tabisu da sanyi kallo tana dan murmushi har ta kusa cikin falon goggontan cikin nitsuwa
Hjy mai tuwo dake kwance bisa kujera da jikin tsufa tadan miko kanta cikin sauri tana amsa sallaman taawure adan rikice amma dake tanada shegen mita yasa bata gane muryanta bugu daya ba, Wani Caraf ta yatsina fuska tace 'ohni yau naga takaina waye kuma haka da yammaci tun bamu ci na dare ba? Kode sabbin masu saida abincin nan ne suka dawo zasu sakani agaba da mita akan kudi...ohh ni Yau mairo naga takaina Waye ne kam... shigo daga ciki mana..ke innari zoki dubamin
Gyara zamanta tayi akan kujerar tana dada gyara mayafinta akafadunta, sashenta Babban self contain ne amma na ginin laka me karfi da aka bi jikinsa da siminti yay fess fess duk da ba a fentashi ba, ciki da falo ne me dakuna biyu, ta kakkale koina da brown leda carpet da kujeru kananan seti da tv dan madaidaici da wooden center table iri daya da brown cupboard dinta datay wani irin jeren kwanukwanta akai.
Jim kadan saiga bullowar taawure cikin falon, gabanta gadi fuskarta dauke da Wani dattijuwar Murmushi wanda tun daga yanayin shigar ta Kamala yasa hjya mairo kara bada hankulanta akanta da sakin fuska tahau mata maraba har idonta na tara ruwa.
kullum taga taawure sai taji wani irin tausayinta aranta sabida asalinta yar gata ce da rayuwar maraici ya juyata ta dawo abar tausayi.
"ooo taawure? ai sekice min kece kika lankayo sawun kafafunki kikazo, toh sannu da da zuwa lale maraba da xuwa.
taawaure nata sakin murmushi har ta nemi Waje ta zauna Adan dofane feeling so uncomfortable da irin kallon kurilla da hajy mai tuwo ta ke jefa mata. zuciyarta ne ya shiga mata Wani irin zafi ganin yadda taawure take kkrin dawowa kamar wata sokuwa kamar batay ilimi da take gidan ubanta ba..
Gaisuwa suka somayi
Irin gaisuwan Nan na darajawa da kuma kimantawa gwanin burgewa, hajya