ABUNDA KE BOYE

Author :  NONE Category :  African Stories & Novels

Chapter   4 / 88

9K to 12K   out of 262.2K words

mairo tana tambayarta lpyarta tanayi tana hada mata da addua masu karama Inda basai angaya kasan tamkar uwa taawure take kallon hajy mairo

bawani alakar jini me yawa bane atsakanin su,saidai kuma kawun taawure wato alhj mamman me gareji daya rasu da jimawa wanda anan anguwar tudu yake zama shine mijin hajy mairo na biyu, mijinta na farko a kano yake, suna da yara maza har hudu shima din rasuwa yay, aurenta na biyun kuma bata haihu dashi ba sabida shekaru yaja kuma dake auren nata dashi bai jima ba ya rasu da ciwon cancer, toh a ahannunta taawure tazauna harsaida tay aure, duk wani abu dake tafe a rayuwar taawuren ta sani duk dama batawani shiri da juma, ko kodan jininsu bai hadu ba anma bashi yahana
take rikeda lamarin taawure da yaranta a tsakani da Allah ba.

hira sukayi na yaushe rabo da kuma abunda ya faru awajen wasan gasa, kmr kullum yauma juma yasha caccaka awajen hajy mai tuwo dan tsani irin zafafa al'adar jahilci dayakei akan iyalansa, can dai data gaji da mitan sai kuma tahau kara ma taawuren karfin gwiwa akan batun karatun yaranta sabida malaman nasu nayawan cewa dukansu suna da baiwa na musmn.

hira me tsayi sukayi akan yadda inayar tafi kwarewa akan karatun addini harma ana kwatance da ita a tudu, ayanaah kuma daga dukkan alamu bokon nan dai yafi dauke mata hankali, har dare yay nisa suna hira salla ne kawai ke tadasu, nan ma taawure ta sanar da ita cewa har tsawon wata uku suna nan tudu kafin nan juma ya dawo. da kyar suka rabu taawure ta koma dakin kusa da zaure da ake ware mata intazo da yaranta, ta samu anayah tay bacci akan cinyar addanta inayah wace ke zaune akan dadduma tana kkrin shafe mata nasi da falaki da ayatul kursiyu ajiki dan ta samu kariya. sabida kunyar haihuwar fari dake tsakaninsu hira kadan sukay da taawure kafin suka kwanta da niyyar washe gari sassafe duk zasu fada cikin harkokin gabansu na kasauwanci da kuma karatu.

washe garin ana kkrin zaa kiran sallan asubahi sassanyar sautin bitan karatun qur'ani da inayah take zubawa acikin yanayin kwarewa ne ya farkan dasu daga bacci. zaune take agaban fitila ta rufe kanta da zani, da wani irin farin ciki da zumudi ayanah ta diro daga gadon baccinta itama taje tay tsarki da alwala awaje snn tazo ta zauna daf daf kusa da addanta tana karanta musu suratul Duha itama nan ta jonata sunayinsa tare.

tsabar sanyi da dadin muryansu d ayadda suke karatun fuskokin su cike da murmushi da dumbin son da suke ma juna atake atake kwayar idanun taawure ya cuko da ruwan hawaye mai tattare da rauni da kuma tsantsan alfahari tareda farin ciki mai sanyaya zcyar kowata uwa.

saida suka kai har suratul mutattafifin snn aka kira sallah, nan suka mike duka sukayi ibadar su, suna gama azhkar na safe sukayi gaisuwa, tuni inayah dake ita tana da zafin nama tayo waje tafara shara tana kimtsa tsakar gidan.

ayanah kuma dake tana da rauni da tsoron sanyi ta tsaya tana gyara cikin dakinsun, bayan ta gama ne ta zauna bisa tabarma tanadan bitan dan gyarrarkin da inaya ta mata akan sallah. taawure kuwa tuni ta kwashe toka a murhu ta fara daura kunu da dumame, kafin kace wani abu gidan yayi fess, ya kuma dauka da qamshin kunu da dumame. da tsananin farinciki ganin sun gama komi hajy mai tuwo ta fito duk aka gaisa cikin raha, aka ci abinci akayi dam kowa yay wanka kafin ma'aikatan hjy me tuwo suka fara zuwa ana shirin wucewa shago, taawure bataje
kasuwa ba, yaranta biyu suna kammala saka uniform dinsu ta saka su agaba sukeje har makarantarsun ta biya sauran basuka da ake binsu na karatun ayanaah both islamiya da bokon duka snn ta musu sallama ta dawo gidan ta samu duk su hjy mero me tuwo har an wuce wajen sana'a, itama tattara nata kwaryan nonon tay ta wuce cikin gari saidai daga tadanyi shiru sai taji zcyarta baya mata dadi, dan har ynxu gani take kamar fa mugun bakin da juma yay ma yayanta akan karuwanci hala zai iya kamasu. dakyar da addua snn abun ya lafa mata. rayuwar su mai tsafta sukeyi a tudu, ayayinda kowa cikinsu yake cigaba da sanaarsa yaynta kuma sun balain jajircewa wajen karatu. inayah dake da 12yrs tana aji biyar na firamare dake a aji biyar din zata tsaya, qur'ani kuma saura mata shafuka shida ta hade haddar izu sittin, fiqhu, sira, hadisai, da tauhidi, duk saida ta kwarance sosai, asali ita bata da wani aibu face zuciya da taurin kai da Allah ya zuba mata. ita kuma ayanaah yanxu ne ma take kkrin kaiwa izu talatin a qur'anidake tafi saka ilimin bokon aranta, babban burinta shine ta dawo me ilimin bokon sosai dan tay kudi takai addanta da mamanta makka, she is soo frail nd innocent, duk dama mutanen tudu suna yawan nuna mata favouritism da fifiko sabida tafi addanta kyaun fuska amma hakan bai taba raba kansu ba, they love each oda deeply and immensely dan ko tafiya suke ahanya haka zakaga suna hira sosai suma alkwaru ma juna kullum kuma hannunsu makale da juna. inayah ke yawan koya ma ayaanar ilimin lissafi (mathematics) da bitan islmiya dake tay nisa. mahaifiyarsu taawure kuwa sosai take kara saka ido akan duk wani motsin su da kuma tarbiyansu, hakanan rayuwarsu ta kasance yau da gobe komi ya lafa suna zamansu anan acikin tsananin kwanciyar hankali da nishadi a anguwar tudu....

idan kinason cigaba da samun posting kibi shafukata 👇🏻

*AREWABOOKS*
*@SURAYYAHMS*

*WATTAPAD @SURAYYAHMS*


*WASAP CHANNEL ND GROP: SAVE MY NUMBER 08060712446 TO BE ADDED*


#SURAYYAHMS
#COMEBACK SERIES
2024/2025
[22/10, 19:03] Ányà Bá’kó̄̄̄ M.: _ABUNDA KE ƁOYE...._
_Love And scandal💕_
*_Arewabooks@surayyahms_*


⏯️4️⃣
No. 1 Al-Mansur Crescent, G. A. Extension, Nasarawa GRA, Kano.

kano tumbin giwa koda mai kazo an fika, dan haka kar kasha mamakin cin karo da anguwanni na zallan "old money" prestige, wato jikakkun masu kudin ɓoye ba ƴan fafar siyasa ko yan cirani ba, asalin kudi me amsa sunansa ake batu wato kudi marar hayaniya, mutane masu takama da karfaffan shahara, 'muƙami, da kuma power na juya uban kowa ahannunsu..

anguwace shiru babu hayaniya face yar shimfidadden titi me tsananin tsafta inda ko da mota ya wulga sai dai kaji wulgawar tashin tsunsaye daga dogayen bishiyoyi da suka kawata wajen gabaki daya. tsaka tsakiyar anguwar ba can can ciki sosai ba Wani tanfatsetsen gida ne kirar ginin masu saka guntun wando da hular malfa irin 3rd century british mansion style din nan wanda ko dison fenti babu ajiki, transitional multi million dollar mansionce mai dauke da both modern and traditional outlooks daga ciki har waje.

Kangon gidan da tsawon gaske, dan ance kafin ka yi toxali da asalin cikin muhallin sai ka shirya
shirgegen automated bakar drag gate ne ya katange shi mai gaba daya, akan ginin waje aka fafe wani waje me kyau snn aka rubuta _Al-Mansur Residence Est. 1972”_ da ruwan duwatsu. Babu wani mahaluki dake son wulgawa tanan wajen kasancewa shikansa layin an masa suna ne da wann me gida.

gida ne da ya mugun shahara sabida tsari marar tarkace dan kusan ince kominsa a kiyasce yake tundaga kan su muamala, da zumunci, da gogayya da jama'a da yamai dashi abun gujewa domin kare darajar arzikinsa da sunan gidansa, Iya zagawar ka anan Ba kowani lkci zaka iya cin karo da motsawar kofarsa ba..

asalin sunan me gidan shine _Alhaj professor zayyanu al-mansoor._ Shi ba jinin sarauta bane, ba kuma dan siyasa bane ko dan kasuwa, kawai dai Hakimtaccen bafulatani ne daya matukar tara dukiya da power na sawa ayi ko abari sabida baiwa na ilimi da daukaka da Allah ya riga ya basa. jajirtaccen namiji ne dayake da key importance a harkan siyasa duk da baya shiga cikinta, sune gaggan share holders da ake hada akai dasu adora mutum akan matsayi ko mulki, he is very well connected to the gorvemnt aides daga russia, france, har america. yana da wani irin karfi ne a internationl relations da gulf business, he has this elitic access to the high profile officials na duniya both international security, politics and organisations .

shi babban professor whose major was in international relations nd financial tech. haka zalika yanada manya manyan charitable foundations ko ince money loundering firms in disguise da ake zargi sune hanyar dumbin arzikin dayake dashi, ta wayann manyan charity foundations dinsa yana iya loundering mugayen kudade ma mafias, drug lords, oil executives, da gaggan kusosin masu kudi a kasashen waje kai harda shahararrun barayi. sai yay maza ya gina manyan fin. tech firms akasashe ana masa running tech businesses sabida kauda zargi da kuma kauracewa binciken masu kakale.

Duk dama cikakken bafulatani ne musulmi daya fito daga babban gida a arewa, shi sam baiya son fiye hidima wa addininsa sabida tsabar ilimin boko da wayewarsa dake irin gurbatacen wayewan nan ne.

su maza hudunsu mahaifyarsa hajiya mairo mai tuwo ta haifa da mijinta na farko daya rasu anan kano wato alhaji al-mansur makarfi, babban dansu na fari _Dr. Al-mustafa almansur_ shima ya rasu, bayansa sai shi _prof. zayyanu da twin brother insa bappa zaidu_ , sai autarsu _uncle muhammad_ .

prof zayyanun ma shikadansa Allah yay ma ƙazamin arxiki acikinsu, amma bai taba taimakon kirki wa uban kowa acikin yan uwansa maza ba, hasalima ya raina uban kowa, yadda yake murza jiji dakai da iko zaka dauka ko shine babba agidan musmn da mahaifinsu alhaj mansoor makarfi yake fifita shi sosai tun kafin ya rasu

toh bayan rasuwar babban wansu Dr almustafa da kuma rasuwar mahaifinsu almansur makarfi da kusan shekara guda sai snn hajy mairo ta sake yin aure acan can anguwar tudu, ta auri alhaj maman me gareji, akan aurenta na biyun ne prof zayyanu yayi fushi da ita harma ya fita a hanyarta dan dama bawani shiri sukeyi ba
..hajya mai tuwo yar gaskiya ce, sam sam bata son abunda zai raba kawunan yayanta shiyasa bata kaunar irin mugayen halin danta zayyanu duk da dumbin arxikin da yakeji dashi.

kwance tashi zuriar Al-mansur makarfi ya zama babban Ahali antara surakanai ga jikoki, Babban wansu marigayi al- mustafa ya rasu ne yabar matarsa, fatimatul mardiya(Ammi karama). da yaranta biyu, "Ibaadur-rayyan,(Ibaad) da kanwarsa safiya ya girmeta sosai dan tun tana ciki baban nasu ya rasu.

sai bappa zaidu shima ya auri matarsa anty raihanatu, shiya fara aure agidan wanda yasa ake ce ma anty raihanatun Ammi babba matsayinta na farkon surkuwan gidan. suna da yaransu uku Maheer, na biyun kuma ya rasu, sai mace ummu kulthum, Dake prof zayyanu din twin bro dinsa ne, shima yana zaune da da matarsa hajiya Dr. Hamida shettima amma shi bai samu haihuwar ta dadi ba..

sai karamin cikinsu uncle mohammad anacemai uncle moh
ya aure matarsa anty safeera achida yar gidan tsohon minister of agriculture, suna da babban dansu mujaheed duk dama he is the youngest, da kanwarsa shima ana ce mata sultana.


within all this years shide prof zayyanu abu daya ya nema ya samu dakyar wato haihuwa, dakyar da wahala ya samu one and only dotersa wato "zainab Arifah al-mansur" kusan a bazata tazo duniyar nan, bayan har prof ya fara cire rai ga batun samun haihuwa tareda matarsa hajya hamida shettima da yake mutuwar kauna sabida halayarsu iri dayane zak zak yadda baison taimakon addini da mutane hakanan itama take

tunda ya same haihuwar zainab- Arifah saiya dauki son duniyan nan yadora ma kyakkwar yarsan, kai duk wani burinsa na duniyan nan akanta yake karewa dan ji yake kmr ba'a taba haihuwa ba sai akansa, as his only child he gives her everything, yarsa yar hutu ce da ko spoon bata iya dagawa ba, kai tun tana karama aka raineta da vibes na ego da arrogance amma bana jahilci ba kaidai akwaita da fi'ili da shegen manyance, she lead a very stylish life,extremely spoilt nd pampered, zainab arifah sangartciya ne na bugawa a jarida ita kullum masu aikine a zagaye da ita ana kulawa da ita sosai dan ko hanyar kitchen din gidansu bata sani ba bare tasan me akeyi aciki.

komi na duniya tana samunshi awajen babanta, dan shine mafi kusanci da ita, yar hutu yar qwal take awajensa, just one thing he demands frm her is total obedience.

kuma ahaka ya raineta tana masa tsananin biyayya, like abject obedience bata iya saɓa masa ko kaɗan. zai iya kashe kowa ya binne komi akanta amma batun biyayya tsakaninsu kusan dolene.


Duk wani shikashikan sangarta da lalacewa sanadiyar so da gata Zainab arifah tana dauke dashi, saidai ita ta dan bambanta da iyayenta wajen son danginta, tana jiji da kanta but she is full of life, clumsy, nd so intelligent, tana iya sake fuska da kowa saidai akwaita da mugun rainin wayo da iya maganan banza.

damacan marigayi kakansu almansoor makarfi shiyafara raba kan yayan nasa yabi ya wargaza xumunci tsakaninsu musmn wajen nuna fifiko akan prof zayyanu gashi abun na kokarin binsu har kan ƴaƴa, saidai kuma babban dansa marigay al- mustafa sosai yay bakin kokari wajen hade kansu tun kafin ya rasu, arayuwa koda kowa zaiyi zuciya da irin walakncin prof zayyanu shide sam baiya rabuwa dashi, duk cikinsu yafi masa nasiha akan zumunci koda bada kudi ba, ya zamana dai anatare tunda uwansu ɗaya ubansu ɗaya kar kudi ya raba zumunci.


ahaka har Allah ya dauke ransa, kullum wa'azin dayake musu kenan. saidai kuma yana rasuwan, sake auren da hjy mairo tay a tudu yasaka profesor zayyanu ya kara barranta kansa da su shikuma bappa zaidu yana da dan banzan kamewa bai fiye son hayaniya ba, dake ma prof yasan bamai gaya masa yaji ynxu daga shi sai twin dinsa bappa zaidu kuma yanxu sune manyan gidan uncle moh dama asalinsa bai fiye son shirgin matsala ba.

andau tsawon lokaci ana tafiya ahaka kowa na kulawa da manyn hidindimun rayuwarsa dana yaransa, iyaka dai sanadiyar samun yarsa zainab arifah ne har ya zamana ynxu yadan sassauto har ana dan kokarin zumunci dashi sama sama duk dama har yau babu mai cin arzikinsa ta dadi sai ta bashi ko ta hnyr cin mutunci.


anan cikin anguwar nasarawa extension g.r.a prof zayyanu almansur yake zama da hadaɗdiyar matarsa hajiya hamida shettima da yarsu Zainab arifah and whole street is named after his resident,sabida kudi da power yasa kaf familyn al-mansur ma shi ake cewa Kawu babba, sai twin dinsa bappa zaidu shikuma anfi ganin girmansa da dattakonsa sabida shine yafiye daukar nauyi da damuwar kowa ynxu, yana zama ne kusa da GRA kano, gidan murtala. shi ma babban ma'aikacin gwamnati ne dan yakai matsayin Bank Director kuma yana da businesses dinsa a kasuwa, shi duk dama baiyi sa'ar mata ba, yana hidima ma yaran yan uwansa da kuma mahaifyarsa sosai, yanxu haka ma ya gina babban gidan abinci me shegen kyau ma zamani a can kasuwa musmmn dan mahaifyarsu hjy mairo mai tuwo, yana jirane duk sanda ta bar can tudu tazo cikin kano zai barta ta cigaba da gudanar da sana'arta na abinci anan tunda abunda take so kenan, shi mutum ne meson jininsa duk da baqin halin matarsa ammi babba bai hana ya ɓude kofar gidansa ma kowa da kowa ba.

koda babban wansu Dr al-mustafa ya rasu, yaso ace shine kawai yay jarumta ya aure matar yayansun wato anty fatima da ake cewa (ammi karama) sabida kamilar macece mai kyan hali kyakywan gaske kuma marainiya, yaso ace a dakinsa zata karasa rike marayun yayanta wato Ibaad da safiya har suyi aure, saidai inaaa.. tuni babban surkuwan gidan wato anty raihanatu dake ma itace aka fara aurowa tana mugun ji dakanta anacemata ammi babba tadaga hankali ma kowa tabi bokaye da malamai har saida ta hana yuwar komi.

sosai anty raihanatu ta tsane anty fatiman har bata iya boyewa, kamar kishiyarta haka take kallonta duk dama tay nasarar hana bappa zaidu aurenta, sau da dama taso talaka mata sharrin zina dan kawai akoreta a ahalin sabida wann uban kishin datakeji aranta nacewa haryau idon bappa zaidu yana kan ammi karama shiyasa ma aka nace ta zauna agidan akan yaranta har saita samu mijin aure..

sanadiyar yar wann hatsaniyrsun yasaka aka raba musu gida, ammi karama (anty fatima) da yarta safiya suna zama ne a can family house inda uncle moh da matarsa anty safeera da yaransa biyu suke nan zaune acikin anguwar rijiyar zaki. sashenta daban nasu ma daban sai babban self-con asama shima anbari ne ma hajy maituwo sabida hutun weknds da zumunci da duka jikokinta.


shikuma ibaad yafi zama ne a karkashin bappa zaidu, tare da cousins dinsa maheer da kulthum, toh dake hajy me tuwon ma acan gidansa aketa tsammani zata zauna duba da yafi kusa da kasuwa, yasa gidansa yake da girma sosai dan yariga ya mata babban flat aciki ga kuma sabon motarta na zuwa shago daya gina mata a kasuwan anata jira dai ta dawo.

kusan al'adar gidan ne duk weknds kawai ake dan tarkartowa duka azo cikin family house dinsu na rijiyar zaki domin hutu da kuma karfafa ziyara da zumunci, uncle muhammad ne dama aka bari anan wanda shi ne autanta kuma civil engineer ne, kowani wknds shi yake amsar kowa da kowa cikin aminci da fara'a da tausayi he is deir young nd happy uncle moh, still thriving in his career sabida political connection da iyayen matarsa suke dashi yasaka yana samun kudi sosai shima ba lefi dan shi baida matsala ko kadan.


idan anzo family house na rijiyar zaki ne ibaad yake samun cikakken ganawa da mahaifyarsa ammi karama, ita kuma ammi babban ko da sunzo family house din tafison harka da matar uncle moh wato anty safeera duk dama ta girmeta sosai amma itadin tana da sisterly connection da hajy hamida shettima sabida anty safeerar yar masu kudi ne kowa yasan babanta ya taɓayin minister, infact da ita kawai hajy hamidar take magana a dangin miji, anty raihanatu kuma dama akwai dan uban maganadisun gulma da kwadayin abun duniya kullum dai tana mugun son taga tana raɓuwa dasu babban burinta baifi dataga anware ammi karama ba.

ya kasance awajene anty safeera zainab arifah take sauka inta sace jiki da driver tazo ziyarar itama, tun jikokin gidan alhaj almansur makarfi suna yan kanana ake gudanar da xumuncin

4 / 88