Uwar Sadiku Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sakina Category :  Complete Novels

Chapter   9 / 58

24K to 27K   out of 172.2K words


Itama Aishan yana shiga ya sanar da ita gobe da yamma zasu je gidan Hajiya da su Zahra, don haka da gari ya waye yana fita office ta kama hidimarta don tayi sauri ta gama. Ya riga ya gaya mata sai bayan masallaci amma duk da haka tana gama aikinta wajen sha biyu ta sa hijabi ta nufi gidan Zahran.

Babu kowa a gidan sai ita kadai da Jummai wadda take share tsakar gida, tun a nan suka gaisa da Jummai ta wuce ciki.

Tana zaune a falo tana ta faman latsa waya tayi sallama ta shiga bayan ta amsa mata. Da fara arta ta karasa ciki ta zauna a kujerar mutum daya.

 Ina kwana Mommy.

Sai da ta kalleta ta gatsine fuska sannan ta amsa da kyar

 Lafiya kalau.

Sukayi shiru na dan lokaci, ita Zahra ta cigaba da duba wayarta kamar babu mutum a wajen yayinda ita kuma Aisha take mamakin wannan tsare gidan da muzuran da ake mata. Ta yi dan gyaran murya tace

 Uhm, Abban Sadik yace zamuje gidan Hajiya da yamma shine na leko mu gaisa. Idan kun shirya ko yara suyi min magana sai mu tafi.

 To.

Ta mike tsaye tayi mata sallama ta fice, ita kuma tabi bayanta da harara harda kwafa saboda kishi.

Ta tsani ganin matar nan, gashi dai an ce bazawara ce amma kamar budurwa. Kuma ta zata Malam Sule direbanta ne ita kadai amma za ace su wani hada fita.

Ta ja tsaki ta cigaba da abinda takeyi.
& &

Sai wajen karfe hudu saura sannan Zahra ta shirya, ita da yaranta gaba daya banda Sadik, domin shi yace ba zai je ba. Suka fito gaba daya suka shiga mota, har Yusra zata shiga gaban mota Mommy tace ta dawo baya. Don haka suka shiga bayan motar gaba daya, ita da Yusra, Rukayya, Nana da kuma Ummi duk da wajen zaman Ummi bai kai na mutum daya ba.

Yusra ce tacewa Malam Sule

 Malam Sule ka tsaya a kofar gidan matar Abba da ita zamu tafi.

Suna fitowa yayi parking a gate din Aisha ya latsa honk, ya juyo yacewa Yusra

 Ko kirawo mana ita zakiyi.

Mommy tace

 Kayi mata honk din zata fito ko kuma ka buga mata gate.

Yanayin da tayi maganar ya sa babu damar musu don haka kawai sai ya fita ya buga gate din, bugu daya ta bude. Cikin girmamawa ta gaisheshi tace

 Bari na dauko jakata a shirye nake.

Ta koma cikin gidan shi kuma ya koma mota ya zauna.

Jimawa kadan ta fito ta mayar da gate din ta rufe ta karaso jikin motar ta bude ta gefen da Yusra take zaune tare da sallama tana fadin

 Yaya Yusra dan matsa na zauna, ko Nana ce zata koma gaba sai mu zauna a bayan.

Dukansu suka kara babbakewa Yusra ta banka mata harara yayinda Rukayya ta sunkuyar da kanta, Mommy tace

 Basa shiga gaban mota.

Ta kallesu da mamaki sannan tace

 Umm, to ku dan gyara sai na shigo mu zauna nan duka.

Mommy tace

 Gurin ba zai isa ba ai baki gani bane, ki zauna a gaban mana ke.

Mamakin Aisha ya karu, kafin tayi magana Malam Sule yace

 Ina ga ai ko Ummin Abban aka miko nan ai wajen zai isa Hajiya.

 Malam Sule, ka san dai Yallabai baya barin yara zaman gaban mota ko? Ta shiga gaban kawai muje in ba haka ba ka kaimu sai ka dawo ka kaita.
A tunzure tayi maganar don haka Malam Sule yayi shiru.

Aisha ta dan ja baya, nan da nan Yusra ta ja kofar motar ta rufe yayinda Mommy tace

 Mu tafi.

Ya tada motar ya leko ta taga yacewa Aisha

 Ranki ya dade yanzu zan dawo in Sha Allah.

Yaja motar suka barta a nan tsaye tana mamaki.

Ta juya zata koma gidan sai kuma tayi wani tunani; yanda taga yanayin matar nan bata jin zata bar Malam Sule ya dawo kuma idan taje bata san me zata fada a can ba idan kuma ya dawo bata je ba bata san irin sharrin da za tayi mata a wajen maigidan ba. Ta riga ta san gidan don yayi mata kwatance kuma a bakin titi ne, don haka ta juya ta nufi titi, nan da nan ta sami motar haya ta bisu.

Zuciyarta har tafasa takeyi saboda takaici, ya za ayi ta shiga gaban mota da direba bayan ga yara. Ko da ma yaran ba zasu shiga gaban motar ba idan suka mammatsa bayan motar ma zai ishesu har ita. Amma saboda an shirya sharri da wulakanci ace ta shiga gaban mota, kuma a ja mota a tafi a barta.

Nan da nan ta isa gidan, kafin ma tayi tambaya ta gane domin ta hango motar Malam Sule a kofar gidan, ta sallami mainmota tana juyowa Malam Sule ya fito daga motar yana rage tsawo

 Ranki ya dade tahowa kika yi? Don Allah kiyi hakuri, Hajiya ce tace na jirasu idan na mayar da su sai na taho dake.

 Babu komai.

Ta wuceshi ta shige cikin gidan.

Suna zaune a falon Hajiya ana ta hira.
Hajiyan tana zauna a kasa ta mike kafa su kuma Zahra da yaran suna zaune a kewaye da ita, sai Anisa wadda budurwace 'yar wajen Yaya Saratu sai kuma yaran Bashir kanin Abban Sadik din su biyu; Fawwaz da Nawal.

Sai hira akeyi yara suna kaiwa da kawowarsu.

Tuni Mommy ta riga ta yi musu bayani cewa Aishan ce tace bazata biyo su ba sai dai a kaisu a dawo a kaita don ba zata hada tafiya da su ba. Take Hajiya tace a gayawa Malam Sule kada ya koma wanda dama Mommy ta riga ta gaya masa. Zancen suke mayarwa ta shigo, Hajiyan ce ta amsa sallamar ta, ta karasa ciki jikinta babu kwari saboda kallon da akeyi mata.

Ta wuce ta zauna daga gefen Hajiya inda yake da dan sarari, cikin sanyin murya ta gaida Hajiya wadda ta amsa mata kamar a fusace.

Jikinta ya kara sanyi sosai, don haka ta gyara zama ta sunkuyar da kai tayi shiru tana wasa da yatsunta.

Suka cigaba da hirarrakinsu kamar babu ita a wajen, don Anisa ma ko gaisheta bata yi ba. Nawal da Ummi ne kawai suke kulata da yake ta dan ja su da wasa.

Ba ta dade da zama ba Hajiya ta tashi ta shige daki, tana shigewa Mommy ta fice ta koma tsakar gida inda Hindu mai aikin Hajiya take zaune a tabarma ta zauna. Kafin wani lokaci duk sun fice sun barta ita da Rukayya.

Ita kanta Rukayyan so take tayi mata magana amma ta kasa, bata jin dadin yanda ake mata amma ba zata iya yin komai a kai ba.

Jimawa kadan Mommy ta cewa Hindu ta yiwa Hajiya magana zasu tafi. Ba jimawa ta fito ta wuce Aisha da Rukayya a falo ba tare da tace komai ba ta karaso tsakar gidan. Suka taso gaba daya sukayi sallama da Hajiya, nan take Rukayya ta fito Aisha na biye da ita itama tayiwa Hajiya sallama.

Sai da Hajiya ta bata rai sannan ta amsa, ta kauda kai. Yara suka wuce Mommy na biye da su tare da Anisa don ta yi musu rakiya. Aisha ta bisu a baya tana shafa jakarta, kudi ne dubu goma a ciki ta kawowa Hajiya amma bata ga fuskar bayarwa ba don haka kawai ta bisu suka fice.

Suna fitowa Yusra ta shige gaban mota Mommy da sauran yaran suna kokarin shigewa baya Aisha ta wucesu ta karasa bakin titi. Suka bita da kallo, Malam Sule ya yunkura zai bita Mommy tace

 Mu tafi kawai.

Cikin sanyin jiki ta ya koma ya shiga motar ya zauna.

Tana tsayawa kuwa ta sami mota don haka kafin ma su juyo ta shige mota direba ya ja.
Mommy ta dubi Anisa wadda take tsaye rike da hannun Nawal tace

 Kin gani ko? Ko kallo bamu isheta ba saboda ta raina ni. Ai shike nan.

Ta kama baki tana jijjiga kai
 Wallahi na gani Mommy, ai kuwa sai na gayawa Hajiya.

Sukayi sallama suka kamo hanya.
& ..

Aisha tana zama a bayan tasi din da ta shiga kwalla ta fado mata. Wannan wane irin sharri ne, kallon da ake mata a gidan Hajiya ta tabbatar wani sharrin Zahra tayi mata. Ta kula da yanda bayan sun fito Yusra ta zauna a gaban mota wato ta zo su tafi, ita kuma tunda ita ta kawo kanta to ita zata mayar da kanta shi yasa ma ta wuce su.

Har taje gida zuciyarta tana tafasa saboda takaici, da yake tana shiga gidan akayi magariba sai kawai ta yi Sallah sannan ta zauna tana tunani; ita kuma wannan nata salon kishin kenan? To haka zasuyi ta zama kenan? Lallai akwai aiki.
-----

A al adarsa kusan kullum idan ya taso daga aiki sai ya biya gidan Hajiya ya gaisheta, haka zai zauna suyi ta hira har sai dare yayi sannan ya wuce gida. Duk da yau bai taso da wuri ba haka ya wuce gidan Hajiyan don ya san gobe asabar da jibi ba lallai ya samu yaje ba tunda suna da meeting da gwamna kuma ya san sai dare.

Bayan sallar isha i ya shiga gidan, bayan sun gaisa da Hajiya da mutan gidan, ya zauna suna hira. Wajen karfe tara da kwata ya duba agogo yace

 Bari na tafi Hajiya, dare ya fara yi.

 Hakane.

Suka dan yi Jim, har zai mike Hajya tace

 Yusufa ita wannan am???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?aryar taka me yasa bata da kunya ne?

Mamaki ya kamashi yace

 Hajiya! Wani abu tayi ne?

 To na zata Sule direbanka ne kuma kai kace ya kawosu tare da Zahra?

 Eh, hakane. Basu zo bane?

Ta tabe baki

 Sun zo mana. Amma yarinyar nan don rashin mutunci wai ba zata biyo Zahra su taho a mota daya ba sai dai Sule ya koma ya daukota ya kawota da ban.

Mamakinsa ya karu

 Ah! To garin Yaya? Kuma fa tare nace su taho gaba daya.

 To haka dai sukayi, sai da Sulen ya kawosu ni kuma nace kada ya koma shine ta biyo motar haya ta zo ita kadai kuma ta shigo tana yiwa mutane gani-gani. Da zasu tafi ma kuma haka, Anisa ma tana kallo yarinyar nan ta wuce Zahra da yaran a mota ta hau motar haya.

 Ikon Allah!

 Ki zo ki tarar da mace da mijinta kice ba kya son mu amala da ita? Dama shi yasa tace ka raba musu gidan?

 Ba haka bane Hajiya, watakila dai akwai wata matsala& '

 To gaskiya dai ya kamata ka taka mata burki, idan tana sonka to ta soka da iyalanka.

 Bari naje gidan, in Sha Allah zan dau mataki a Kai.

Suka dan kara hira Hajiya tana jaddada masa lallai ya dau mataki, daga baya yayi mata sallama ya tafi.
& &

Ranshi yayi matukar baci, wannan wane irin wulakanci ne Aishan tayi kuma ta rasa ma a inda zatayi sai gaban Hajiya. Idan ta san ba zata hada tafiya da Zahra ba me yasa ba zata gaya masa ba; to don me ma zata ce ba zata hada tafiya da iyalansa ba? Ya kasa gane meye dabarar hakan da ta aikata, don kuwa ya san Hajiya ba zata yi mata karya ba.

Kafin ya isa gida dare ya yi don haka sai ya fara tsayawa gidan Zahra tunda ba nan zai kwana ba idan yayi musu sallama sai ya koma gidan Aishan inda zai kwana.

Ruwa kawai ya sha da yake yaran ma duk sun yi barci, ya zauna a falon kasa itama ta zauna. Bayan ta sake yi masa sannu da zuwa ya dubeta yace

 Wai me ya faru ne da kuka je gidan Hajiya?

Kamar bata gane me yake nufi ba tace

 Na me fa?

 A ah, Hajiya tace min ba tare kuka je ba. Me ya faru ne?

Ta gatsina baki

 Uhm, to mun dai fita mun tsaya a mota Malam Sule ya buga mata kofa ta fito ina zaune a bayan mota taki shiga tace wai ya kaimu sai ya dawo ya kaita, bata fadi wani dalili ba don ni ko gaisheni ma batayi ba. Haka dai muka gaji da tsayuwar nace mu tafi tunda yamma tana yi, da muka je kuma Hajiya tace Malam Sule ba zai dawo ya dauketa ba, can kuma sai muka ganta ta zo a motar haya. Da muka fito dawowa ma kuma haka, bata ko kallemu ba ta wuce ta hau tasi don haka muma muka taho.

Ya kalleta yana mamaki da takaici

 To wannan wanne irin wulakanci ne haka?
 To ai ta gaya maka bata son zama damu, sai ka daukar mata nata direban ka bata.

Yayi shiru yana takaici, ta riga ta san zugarta tayi aiki don haka ta gyara zama tayi shiru. Jimawa kadan yayi mata sallama ya tashi ya nufi gidan Aisha.

& & ..

A zaune ya sameta a falo tana kallon TV, yana shiga falon ta mike da fara arta tana yi masa sannu da zuwa. Babu walwala a fuskarsa ya amsa, ya wuceta ya ajiye ledar burodi a kan dining table ya shige daki.

Ta kula da yanda yake a fusace don haka bata bishi ba, ta tsaya ta gyara abincin da ta ajiye masa a kan dining table sannan ta bishi dakin.

Tana shiga shi kuma ya gama shiryawa, ya wuce ta gefenta ba tare da ya kalleta ba.

Ta tsaya a nan ta sunkuyar da kai; tabbas ta san an gaya masa karya da gaskiya shi yasa zai shigo yana cin magani. Ta share kwalla ta bi bayansa.

A dining table ta sameshi yana cin abinci, sai ta wuce ta zauna a gaban TV ta cigaba da kallonta. Bai dade ba ya gama cin abincin don bata jin ma ya koshi ya taso ya dawo inda take, ko kallonsa bata yi ba har ya zauna.

 Aisha.

Ya kirawo sunanta a fusace. Bata amsa ba ta juyo ta dubeshi.

 Me ya sa baki bi su Zahra kun tafi gidan Hajiya ba kika tafi a motar haya?

Ta kara bata rai

 Sun shiga bayan mota ita da Yara, nace su matsa na zauna tace wajen ba zai ishemu ba, nace to Nana ta koma gaba sai na zauna ni a bayan. Tace yaranta baza su shiga gaban mota ba sai dai ni na shiga, ni kuma naga da aurena, ina matarka kuma na shiga gaban mota da direbanka ai ba daraja. Shine tace ya kaisu ya dawo ya kaini, ni kuma kafin ma ya dawo na hau tasi na tafi.

 Ni ba haka aka gaya min ba, kuma bana jin Zahra zatayi haka tunda yaran ko makaranta Sule zai kaisu suna shiga gaba. Kuma a dawowa me yasa baki biyosu ba tunda a lokacin Anisa tace Yusra gaba ta zauna.

Ta riga ta fuskanci inda zancen ya dosa don haka cikin halin ko in kula tace

 Saboda ban san irin shirin da suke dashi ba a dawowar shi yasa kawai na dawo ta hanyar da na tafi.

Suka yi shiru na dan lokaci, sannan daga baya yace

 Aisha! Bana son fitna irin wannan, saboda na raba muku gida ba zai yiwu kice ba zaki hada mu amala da Zahra da yarana ba. Shekaru wajen sha bakwai nake zaune da ita ban taba samun matsala da ita ba, gaskiya ba zan dauki irin wannan ba.

Ta hadiye malolon da ya tokare mata makoro tace

 Ai baka taba yi mata kishiya ba sai yanzu ku& '

Ya katseta

 Ni dai na gaya miki gaskiya ba zan dau wannan ba, yanzu Hajiya sai fada takeyi saboda abun da kuka yi.

 To ai na gaya maka ba laifina bane, ka bincika kafin ka yanke hukunci.

 Mtsewww! Ni dai na gaya miki don kin sa na raba miki gida da iyalina ba wai yana nufin ba zakiyi mu amala da su ba, kuma kece karama dole kiyi hakuri ki bita idan wata sabga ta hadaku. Wannan din ma kuma zan bincika kuma zan dauki matakin a kan mai laifi.

Ya mike ya shige daki ya barta a nan.

Ta bishi da kallo tana murmushin takaici, har ya shige ya turo kofa.
Wannan shine a doke ka a hanaka kuka; ita aka yiwa wulakanci amma ita ake zargi tayi laifi. Ai kuwa ko me zai yi sai da yayi amma bazata taba daukan laifin da ba nata ba.

Ta riga ta gama shirin kwanciya bacci domin kayan bacci ne ma a jikinta, don haka itama ta mike ta kashe wutar falon ta wuce dakinta ta kwanta.

Ba zata iya binsa dakinsa ba don bata son zama da mutum idan yana jin haushinta; ko waye shi, kuma bata ga laifin da ta yi masa ba balle ta bashi hakuri. Ta kashe fitila ta kwanta bayan tayi adduointa.

Sai da ta kwanta sannan hawaye ya kwace mata; fadan da yazo yana yi mata ya fi bata mata rai a kan abinda Zahra tayi mata don ita za a iya cewa kishi ne. Amma shi ya zo yana gaya mata dole ta kula iyalansa; kenan ma har yanzu ita bata zama iyalinsa ba kenan? A haka har bacci ya kwasheta.

Tana jinsa ya fita masallaci da asuba, itama ta tashi tayi sallah ta sake komawa, sai wajen karfe bakwai sannan ta fito ta shiga kicin. Nan da nan ta soya doya da kwai ta

9 / 58