Uwar Sadiku Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sakina Category :  Complete Novels

Chapter   35 / 58

102K to 105K   out of 172.2K words

ta sanar da ita halin da ake ciki. Tace

 Ai da kin gaya min tuntuni, kin manta ne da Hajja. Akwai wani yaji da zata baki da kuma turare, wallahi in kikayi amfani da shi to sai dai kawai nace kema ki shirya don zai yi ta aiki ne daga ya juye zai sake laluboki. Ba zai ma sami sukunin wanka ba. Bari nayi mata waya, ko da yake kema ki kirawota na san gobe da safe zata iya kawo miki.

Nan take tayi mata sallama suka ajiye waya ta kirawo Hajja, tayi mata bayanin duk abinda take so ita kuma tayi mata alkawarin gobe kafin azahar zata kawo mata kayan aiki.

Ta ajiye wayar tana murmushi.

Sai yanzu ne ta sami natsuwa, fatanta kawai kada a sami wata matsala musamman idan Abban yaki bata hadin kai. Amma dole ne tayi iya yinta saboda ba zata yarda Aisha ta rabata da mijinta ba, gashi yanzu kiri-kiri ta fara janye mata hankalin yara. Tana mamakin abinda ya sa Rukayya take son matar nan duk da dai ta san karshenta a wajen kwanan da take zuwa tayawa za a bata abubuwan da zasu saka a mallaketa.
Tabbas dole ta mike tsaye ta raba Rukayya da matar nan.

Tana matukar son Rukayya tun lokacin da ta haifeta kuma har kawo yanzu, duk cikin yaranta babu wanda yake kama da mahaifiyrta kamar Rukayya, domin da ta haifi Rukayyan ma sunan mahaifiyar ta taso sakawa. Sai dai lokacin da aka haifi Rukayyan Abbanta ya tafi aikin Hajii don haka Yaya Bello ne a kan komai, shi kuma bai yi shawara da kowa ba ya saka mata Rukayya. Wanda Abban yace hakan yayi, don haka suna ya bita. Shine saida aka haifi Ummi aka sa sunan mahaifiyar tata.

Duk da haka Rukayyan tana fara girma dabi unta suka koma kamar na babanta. Ga saukin kai da hakuri, komai zata ce ba komai bane, ga rashin wayo. Sai kuma ya zama ta fi shakuwa da Abban saboda ya fi sauraronta fiye da Mommy din.

Amma yanzu duk abinda ta gani a tattare da Rukayya gani take Aisha ce take sakata don haka ta yi shirin dole sai ta rabasu ko ta wane hali.
---------

Ranar asabar tun kafin azahar Hajja ta kawo mata abin da ta bukata; wani gari ne dan kadan wanda tace mata gaba daya zata juye masa a miya sannan kuma da wani turare wanda zata shafa a jikinta dai-dai inda zai dinga shakar kamshin saboda kamshin turaren zai dinga kara kunnashi koda ya gama biyan bukatarsa. Sannan kuma ita kanta aka bata kayan da zata yi amfani da su saboda kada ta gaji.

Yana matukar son couscous da miyar alaiyahu wanda ita kuma bata son couscous din, don haka ma bata yawan yin couscous. Amma yau da yake da akwai abinda ta shirya sai ta dafa masa couscous din da miyar alaiyahu wadda ta sha kifi da nama duk don ta badda kama.

Wajen karfe takwas da rabi na dare bayan ya dawo daga sallar isha i ya raka Rukayya gidan Aisha don ta tayata kwana kamar yanda ya saba. Kafin ya dawo ta riga ta jera abincin a kan dining table. Bayan ya zauna ta zuba masa abincin ta ajiye sannan ta wuce kitchen ta zubo indomie din da ta dafa domin ta ci, ta zauna a kujerar da take gefen tasa. Ya dubeta yana dariya

 Yanzu fa sai kice indomie ta fi couscous din nan dadi ko?

Tayi dariya

 Ai ko ban fada ba ma haka ne, wallahi ni ban san me kike ci na dadi ba a cikin couscous gara nayi ta cin indomie.

 Allah sarki, kin bar dadi fa.

Haka ya cinye couscous din nan yana ta faman yi mata surutu har sai da ya kara.

Bayan ya rufe gidan ya dawo ya zauna a falon sama tare da ita suna hira yayinda Sumayya da Ummi suke wasanninsu.

A al adarsa sai wajen sha daya na dare yake kwanciya amma yau tun wajen karfe tara ya fara neman dalili, sai dai Sumayya ta ki yin bacci. Don haka ya dubi Mommy yace

 Bari naje idan kin shirya kya sameni a dakin, naga mutuniyar taki yau hira take ji.

Yana shigewa ta bi bayansa da dariya domin ita ta fuskanci abinda ya tasheshi da wuri don tana kula da yanda yake ta wasu muzurai da wasu mutsu-mutsu.

Sai da ta gama yangarta ta gama nata yi lokacin wajen karfe sha daya, ya gama zakuwa ta yanda shi kansa mamakin abinda ya janyo masa hakan yakeyi sanna ta shigo dakin. Tana shiga dakin kuma ta yarda zaninta a gefen gadon da yake kwance ta tsiri wata kaiwa da kawowa. Ta shiga bandakinsa tayi brush, ta fito ta kama zarya kamar mai neman wani abu a daki. Sai da ta tabbatar ya gama zakuwa sannan ta kashe fitila ta kwanta a kusa da shi. Tana kwanciya ya fada mata kamar wani mayunwacin zaki.

Tun sha biyun dare suke abu daya amma ya kasa gamsuwa, ko da ya gamsu kafin ya tashi sai kuma yaji yana bukatar kari. Tun yana jin dadi har ya fara mamaki saboda bai saba samun irin haka ba. Watakila dai zai iya tunawa ya sami shigen hakan lokacin da ya dinga kasa yin komai a kwanan Aisha, sai dai a wancan lokacin ba kasa gamsuwa yake ba sai bayan ya gamsu sai ita Zahran ta kara laluboshi. To ko dai yanzun ma wani abun Zahra ta bashi yaci a abincin dare. Haka ya cigaba da hidimar nan yana yi yana tunanin da safe tabbas sai ya binciki Zahra.
Sai can gefin asuba wani bacci mai nauyi ya dauke shi, tunda ta duba taga yayi bacci kuma ta tabbatar baccin nasa yayi nauyi sosai sai ta zare jikinta ta fice daga dakin; domin itama ta gaji duk jikinta ciwo yakeyi.

Sai da aka idar da sallar asuba a masallaci gari ya fara wayewa sannan ya farka daga bacci.

Firgigit ya tashi zaune, ya janyo wayarsa ya duba lokaci yaga shida saura kwata. Yace

 Subhanallah.

Ba zai iya tuna lokacin da ya makara sallar asuba ba koda kuwa bashi da lafiya, nan yayi addu a ya sauko daga kan gadon ya fada bandaki.

Har ya idar da sallah yana mamaki, sai dai ya kasa tuna mamakin me yakeyi, ya kasa tuna abubuwan da suka faru a daren jiya. Yana nan zaune a kan daddumar har kwakwalwarsa ta fara gajiya da kokarin da yakeyi ya tuno me ya makarar da shi sallar asuba amma ya kasa. Bacci kawai yake ji don haka ya tashi lokacin ya fara jiyo hayaniyar yara suna shirin tafiya tahafiz, ya koma kan gadon ya kwanta bacci ya kwasheshi.

Sai wajen karfe goma sannan ya fito, zuwa lokacin ta riga ta jera abincin safe a tebur. Nan ya zauna ya gama cin abincin, bayan ya gama ya fice ya tafi gidan Hajiya.
--------

Tunda suka dawo daga Dubai sai yanzu ne ta huta ta dawo dai dai duk wata gajiya ta rabu da ita, don haka tun asuba da ta tashi ta sa Rukayya ta tayata suka gyara gidan tsaf, har inda ma bata gyara ba tunda ta dawo. Karfe tara saura kwata Rukayya tayi wanka ta shirya ta fice don tafiya tahfiz, tayi mata sallama a kan sai an kwana biyu tunda ta san yau Abba a nan zai kwana.

Ko da taga Bai shigo ba da rana ta san gidan Hajiya ya wuce duk da ya saba yi mata waya ya sanar mata in ya wuce Amma yau shiru. Ta dai San sai dare zai dawo.

Ragowar abincin da ta dafa da safe shi taci da rana, sai bayan la asar sannan ta tuka tuwon shinkafa da miyar agushi. Tana saukewa ta ci ta koshi sannan ta zuba musu na dare a flask ta jera a table.

Ana yin sallar Magriba kamar yanda ta saba tayi wanka ta kunnawa gidan turaren wuta, nan da nan kamshi ya karade gidan. Ta shirya ta dawo falo ta zauna tana jiran shigowar maigidan.

Karfe tara daidai na dare NEPA suka kawo wuta don haka ta mike ta kunna TV, ta kalli agogon bangon taga lokaci. Tana mamakin abinda ya sa har yanzu Abba bai shigo ba; ya saba wuce karfe tara bai shigo ba amma indai zai yi haka to ana yi sallar isha i yake kiranta ya sanar da ita ba zai shigo da wuri ba. Amma yau din bai shigo ba kuma bata son kiranshi musamman idan ta san yana gidan Zahra.

Ta zauna ta dauki remote ta fara canza channel tana laluben abinda zata kalla.

Ta cigaba da kallo duk da hankalinta ya kasa kwanciya kuma ta kasa kiransa. Wajen karfe goma saura yunwa ta fara damunta don haka ta tashi ta zubi tuwonta ta zauna ta fara ci. A hankali take cin abincin don haka ta dauki lokaci kafin ta gama. Bayan ta kai kwanon kicin ta hado shayi ta dawo ta zauna, ta dauki wayarta ta duba lokaci; karfe goma da minti goma.

Hankalinta bai kwanta da wannan rashin kiran nata da bai yi ba don haka ta daure ta danna masa kira. Haka ta dauki lokaci tana ta faman kiransa amma wayar bata shiga, kamar dai yana wajen da babu network.

Mamakinta ya tsananta don bai gaya mata zai tafi kauye ba ko wani waje da babu network. Haka ta hakura ta ajiye wayar ta zauna tana ta wasi-wasi.

Tana nan zaune har wajen karfe sha biyu saura bai shigo ba kuma bai kirawota ba gashi wayarsa ta ki shiga. Zabi daya ya rage mata taje gidan Zahra ta tambaya, to amma gaskiya bata son shiga gidan nan ko da rana balle kuma da tsohon daren nan. Tana da lambar wayar Zahra amma bata taba kiranta ta dauka ba, don haka ma ta hakura ta daina kiran.

To yanzu wanne zata yi?
Idan zuwan ne ma ita ba zata iya fita waje yanzu ba. To amma ai tabbas da da wani abu da zata ji; to kenan lafiya kalau zuwa gidan ne ba zai yi ba ko me?

Ta mike tsaye ta fara zarya a falon, sai da ta gajib ta zauna ta sake duba agogo; karfe sha biyu da rabi.

 To me yake faruwa?

Ta tambayi kanta a fili.
Cikin karfin hali ta sake kiran wayarsa, amma ko shiga bata yi ba kamar dazu.

Bata da wata mafita illa ta kirawo Zahra, a kalla ko da gaya mata tayi cewa yana lafiya shikenan sai ta kwantar da hankalinta ta rufe gidan ta kwanta.

Nan take ta lalubi lambar Zahran ta buga.
& & & &

A al ada da rana yake canza gida idan ya gama kwanan???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? mace, idan ya ci abincin safe shikenan kwanan sun kare sai an sake kwana biyu.

Ranar Lahadi a gidan Aishan ya kamata yaci abincin rana amma sai ta ga bayan ya dawo daga gidan Hajiya ya shigo yace mata ta sa masa abinci zai zo ya ci. Ya shige dakinsa ya barta tana neman taka rawa saboda murna. Ba ma ce mata yayi ta dafa masa abinci ba kawai yi yayi kamar dama a nan ya saba cin abincinsa kullum. Nan da nan ta shiga kicin ta zubi masa abinci ta sa a table.

Nan ya wuni bai sake fita ba kuma bai nuna alamar zai tafi gidan Aisha ba.

Dare nayi ta gabatar da abincin safe suka ci suka kwanta kamar yanda suka saba. Fari tas take jin zuciyarta saboda dama tana bakin cikin raba kwanan da yake musu da Aishan.

Shabiyun dare ta gota ta farka daga bacci, yana kwance a gefenta yana bacci. Bata son ta tasheshi don haka ta dauki wayarta ta haska don ta dubo yara. Ta shiga dakin su ta tashi Ummi ta sakata a fitsari, ta gyarawa Sumayya kwanciya da yake ita diaper ce a jikinta. Ta fito daga dakin kenan wayarta ta fara vibration, ta kalli screen din wayar tayi dariyar mugunta sannan ta amsa wayar ta shige dakinta.

A tsakiyar dakin ta tsaya don ba so take wayar ta dauki lokaci ba, bayan sun gaisa tace

 Dama Abban Sadikne bai shigo ba kuma na kirawo wayarsa bata shiga shine nace ko lafiya.

Tayi murmushi mai sauti ta bata amsa

 Lafiya kalau, yayi bacci.
 Um, t& .

Bata saurari abinda zata fada ba ta cigaba

 Kema ina baki shawara kije kiyi baccinki, idan dai mininane Yusuf uban Sadiku to bazaki sake jin duriyarsa ba. Ya manta dake ya goge babinki a rayuwarsa, ko da me kike takama kuma ya fi karfinki, duk lokacin da kika gaji sai ki tattara kayanaki ki koma gidanku. Kuma don Allah kada ki sake kirana a irin wannan daren muna kwance da mijina.

Bata saurari amsarta ba ta katse wayar , ta kashe fitila ta koma dakin Abban tayi kwanciyarta zuciyarta cike da jin dadi.
& & & ..

Mutuwar tsaye Aisha tayi a nan inda take, bata san me take ji ba; mamaki ne ko kuma takaici. Kafarta ta fara kasa daukarta don haka ta zagaya ta zauna a kan kujera ta dafe kai. To wannan maganganun na Zahra me suke nufi?  duk lokacin da kika gaji sai ki tattara kayanki ki koma gidanku .

Ta muskuta tace

 Ikon Allah!

Kwakwalwarta ta kasa jeranta tunaninta, don haka kawai ta runtse idonta tana maimaita

 hasbunallahu wa ni imal wakil.

Ta jima a haka kafin ta bude ido, ta kalli agogon bangon wanda ya nuna karfe dayan dare da minti biyar.

Duk da bata gane me yake faruwa ba amma dai ta san ba zai zo gidan ba, ko da zai zo to ta san tabbas ba yau ba. Don haka ta mike ta sakawa kofar gidan kwado ta rufe ta kashe fitilun ta shiga dakinsa da niyyar kwantawa. Har ta saka kayan bacci sai kuma ta koma bandaki ta dauro alwala; babu yanda za ayi tayi bacci bayan wadannan maganganun da Zahra ta gaya mata.
Sai da ta dauki lokaci tana Sallah sannan ta bi da addu oi, tayi karatun kur ani sannan ta kwanta.

UWAR SADDIKU

Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)

32

Ko da gari ya waye ranar litinin ce don haka Aisha bata ma tsaya jiran wani abu ba ta shirya ta wuce makaranta; sai dai kawai wunin ranar a cikin wasi-wasi tayi shi. Haka ta wuni tana kiran layin Abban ko shiga wayar bata yi har ta gaji ta hakura. Bata san abinda zata yi ba bayan wannan don haka ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido wata kila zuwa kwana biyu a sami mafita.

Abu daya ne yake firgita ta idan ta tuno abubuwan da suka dinga faruwa a lokacin da yake kasa shiga gidanta; bata son ta yarda wani asirin aka sake yi yanzun amma dai tabbas biri yayi kama da mutum
& & & ..

A hankali har gashi an wayi gari yau Juma a, ko sau daya Aisha bata ji daga Abba ba kuma bata sa shi a idanunta ba.

Kamar yanda ta saba duk ranar Juma a in ta tashi daga makaranta gidan Umma take wucewa don taje wajen yaranta to yau din ma haka tayi. Ana tashi ta wuce ta dauki su Abdallah a makaranta sannan suka wuce gidan Umma. Suka baje kayansu Anti Uwani ta shiga hidima da su.

Can bayan sallar la asar sai ga Zahida itama sun zo da yaranta harda maigidanta wanda bayan ya gaida Umma ya fice ya barsu a can sai dare zai dawo ya daukesu.

Suna zaune a dakin Anti Uwani ita da Zahida suna hirarrakinsu Aishan tace

 Kin san wani abu Zahida, ina jin fa mutuniyarki tayi sabon boka.

Ta gyara zama tana zare ido

 Kai Jama ah wannan Yaya taki ba dai himma ba! Allah ya sa dai bata taba ki ba.

 Ni ai na rigata na ce Allah kuma Allah ya sani bani da niyyar cutar da ita don haka Allah ba zai bata iko a kaina ba in sha Allah, mijinta dai ta taba.

Sukayi shiru na dan lokaci Zahida tana rike da bakinta tana kallon Aishan, jimawa kadan Aishan ta cigaba, ta bata labarin abinda ya faru sannan tace

 Yanzu dai maganar da nake miki tun lokacin rabona da shi don ko waya nayi masa bata ma shiga ban san me yake faruwa ba.

Zahida tace

 Ke Yaya Aisha, to ke yanzu haka zakiyi ta zama? Kamar wata wadda take zaman kanta.

 Ina addu a, kuma na gayawa malaminmu a islamiyya ya bani wasu addu oin da na sihiri duk ina yi. Kawai dai shima Malam din ya gaya min sai na yi hakuri na cigaba da addu ar kada na kosa.

 To ai sai ki dawo gida tunda kinga can kina zaune ne ke kadai, ki dawo nan in ya dawo hayyacinsa sai ki koma.

Tayi gajeran murmushi tace

 Kin san Allah Zahida, ba zan bar gidan nan ba ina nan a cikinsa. Abinda take so kenan ace na bar gidan, ina jin ta kasa sakashi ya sakeni shi yasa ta bullo da haka kinga idan na tafi ai daga nan sai na nemi saki ko da akotu ne. To wallahi ina nan ko da me take tsafi sai naga karshensa, ita halittar Allah kaskantaciyya ta rike ni kuwa Allah Azza wa Jalla shi kadai na rike don haka na san abun nata na lokaci ne. Da ni da ita shege ka fasa!

 Kai Aisha nifa wannan abubuwan sun fara bani tsoro, to ai sai a gayawa Umma ko addu a nei ayi. Ni zaman ma nake ji ke kadai kamar wata mara gata.

 Na san dole zan fada amma na kara bawa abun lokaci tukunna, amma in sha Allahu sai

35 / 58