Uwar Sadiku Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sakina Category :  Complete Novels

Chapter   37 / 58

108K to 111K   out of 172.2K words

baci; wato Saddiku sai da ya fitar mata da mota kenan?
A fusace ta dawo cikin gidan ta haye sama, tana shiga dakin ta dauki wayarta ta fara kiran lambar Saddiku. Ta kirawo shi ya fi sau goma amma bai dauka ba, don haka dole ta hakura ta zauna tana ta faman cika tana batsewa. Gashi Malam Ali ma baya nan balle tace masa ya kai ta.

Wuni guda Saddiku bai dawo gidan ba sai bayan magriba ya dawo; hakan ma don Abba ya hanashi kaiwa dare a waje ne ya dawo. Ko da ta taso masa zata yi fada tsayawa yayi yana mata muzurai yace mata jarabawa yayi a makaranta shi yasa bai dawo da wuri ba. Haka tana ji tana gani ta hakura.
__

Sati biyu da sayen motar nan ta Zahra kuma ta saka shi a gaba da maganar ya sayawa Yusra waya. Ko da Saddiku yaji ana maganar wayar Yusra shima sai ya sayar da tashi wayar yace ta fadi. Don haka Mommy ta sa Abba a gaba saida ya sayi waya iPhone guda biyu kowacce kusan dubu dari da saba in.
__

Kwanci tashi Aisha tana lissafi yau wata shida rabon da Abba ya leka gidanta, duk wata hanya da zata bi don taga tayi magana da shi abun ya ci tura. Duk wanda yake da alaka da ita ko ta waya baya iya samun Abban a waya.

Idan Abba ya tashi biyan kudin hayar gidan Aisha na shekaru biyu yake biya, ita bata ma sanin lokacin da yake biya domin kafin lokacin ya gama wucewa zai turawa Jibrin kudin kawai ya biya.

Shekararsu ta hudu kenan da aure yanzu shekara ta hudun zata kare don haka lokaci yayi na biyan kudin hayar.
Tun ana saura wata biyu shekarar ta kare Jibrin yake neman Abban, idan sun hadu sai yayi ta zullewa yaki saurara maganar. Daga baya kuma sai ma ya kasa samunsa waya, idan kuma yaje nemansa duk abinda zai faru ba zasu hadu ba. Masu gidan kuma duk da sun san Abban amma sun saba ba shi yake biya ba Jibrin ne don haka suke ta faman yiwa Jibrin din tuni.

Sosai ya shiga damuwa domin ya tabbatar karkari su kara wata biyu zasu sa Aisha ta fitar musu daga gida su sa wani, tunda neman kudi suke da gidansu. Shi kuma gashi bashi da kudi balle ya biya kuma ma saboda me zai biya?

Haka yayi ta kokarin ganin Abba amma basu hadu ba gashi yanzu ko ya kirawo Abban wayar bata shiga. Baya son yaje gidan Aishan kuma tunda bai saba zuwa ba a zata wani abu. Sai a hankali ya tuna ya taba kai matarsa wajen Aishan lokacin tana amarya, don haka yana komawa gida ya sameta ya karbi lambar Aishan da niyyar gobe idan ya shiga office sai ya kirawota domin gara ya sanar da ita koda tashi ne ta tashi ba sai an zo an yi mata wani tozarci ba; don ya kula masu gidan sun fara jin haushi.
__

A halin yanzu jarrabawa dalibansu sukeyi don haka malaman da basu da aiki su kan zauna a gida suki zuwa makaranta. Haka itama Aishan tayi, domin tana kai Amira makaranta sai ta dawo gida.

Zaman da take a gida ga damuwar Abba ya manta da ita ta kusan wata bakwai ya fara damunta; don haka ta biya kudi aka koya mata yanda ake yin mayafai na zamani kuma nan take ta sayi injin stoning da sauran kayan aiki ta fara yi.

Yau din ma da taki zuwa aiki zama tayi a gida ta yi wasu mayafai da aka bata aikinsu guda shida.

Tana cikin aikinta wayarta tayi kara. Kafin su gama gaisawa ta gane muryar duk da bata tabbatar ba. Yana yi mata bayanin kansa ta fara tambayarsa matarsa da sauran iyalai. Bayan sun gama gaisawa yace

 Amarya ya mutumina, yana kusa kuwa?

 A a baya nan ina jin yana office.

Ya danyi jim yace

 Aisha wato akwai  yar matsala ne.

Nan yayi mata bayanin halin da ake ciki game da kudin hayar gidan da take ciki.

Bata taba wannan lissafin ba don haka bayanin nashi ya shammaceta. Ta dan yi jim sannan tace

 Um. Don Allah kace su dan yi hakuri zuwa gobe zan kirawo ka in Sha Allah kafin nan munyi magana da shi.

Sukayi sallama suka ajiye wayar.

Ta dawo jagwaf ta zauna a kan kujera dining table.

Ita ta manta ma cewa a gidan haya take; gashi yanzu babu yanda zatayi taga Abba sai ta hannun Zahra wadda ta san idan banda tozarci babu abinda zata yi mata.
To kuma ta san idan ta bari tabbas masu gidan zasu zo ne su tasheta; ita kuma tayi alkawarin ba zata bar gidan nan ba har sai wannan tsafin da Zahra tayi ya karye domin ta tabbatar yanda take addu a da sadaka lokaci kawai ake jira.
Ta tuna bata ma san nawane kudin hayar ba don haka ta dauki waya ta kirawo Jibrin din ta tambaye shi. Ya sanar da ita wancan karon dai dubu dari biyu da hamsin aka biya amma yanzu sun ce dubu dari uku za a biya.

Suka ajiye waya ta cigaba da tunanin mafita.

Yaya Abubakar ya kamata ta gayawa domin zai iya biya mata, sai dai ta san shi yanzu zai ce ta tashi daga gidan don tun da yaji labarin yake so ta koma gidan Hajiya. Sai da Baffa yayi masa magana yace ya bari abi komai a hankali domin shima ya sa ana addu a, kuma tunda Aishan ta nuna ita zata zauna bai kamata a raba ta da gidan ba har sai komai ya warware. Don haka ta san yanzu idan taje masa da wannan maganar kamar tana tuna masa ne.

Ta muskuta kadan a inda take zaune.

To yanzu ya zata yi; ai duk inda ma kudi suke dole ta nemosu tazo ta biya kudin hayar nan don ba zata bar gidan ba har sai Abba ya dawo hayyacinsa.

Gashi yanzu cefane da kula da gida ya koma kanta duk ita takeyi; lokacin da Abban yana zuwa kuwa ko man motarta bata taba saye ba, da zarar tace babu mai zai turo direbansa ya dau motar a ciko mata tanki; haka yake mata har wancan lokacin ma da ya kasa shiga gidan bai taba fasawa ba.
Amma yanzu komai ita takeyi, hatta katin wutar NEPA duk ita take siya ga subscription na TV da sauran cefanen gidan. Yanzu kuma gashi an ce mata kudin hayar ya kare; tabbas dole ta nemi kudi.

Ta fara jiyo kiran sallar la asar don haka ta mike; gara tayi sallah sai ta wuce gidan Zahida suyi shawara tunda yanzu sai karfe biyar zata je ta dauko Amira daga makaranta.

UWAR SADDIKU

Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)

33

Zahida tana kallonta ta tabbatar da matsala; bayan sun gaisa ta dubeta tana dariya tace

 Me kika kunso ne bakinki yake motsi haka?

Tayi dan murmushi tana mamakin yanda Zahida take iya fassara duk wani motsi nata tun kafin ma tace wani abu, ta gyara zama tace

 Hida akwai matsala fa.

Nan ta gayawa Zahidan abinda yake faruwa ta kara da

 Yanzu ban san yanda za ayi ba, kinga dai albashi na yanzu duk a kan cefane da kula da gida suke tafiya. Wallahi sai caji kaina yake.

Ta dafa cinyarta

 To ke Yaya Aisha ki koma gida mana, ya za ayi ma ki biya masa kudin haya? Ki tashi ki basu gidansu ki koma gidan Hajiya tunda idan ya dawo hayyacinsa ya san inda zai sameki.
Ta jijjiga kai, tace
 Ba zaki gane ba Hida. Ai na gaya miki ko zan bar gidan nan to sai ya dawo hayyacinsa; kin san matarsa cewa tayi wai tana bani shawara na koma gidanmu, idan na tafi ai bukatarta ta biya kuma in Sha Allahu bata isa ba. Ina nan sai karyarta ta kare.

 Hmmn! To ko Yaya Abubakar zaki gayawa?

Ta kama haba tana zaro ido

 Wa! Wannan ai kadan yake jira ya murdewa auren nawa wuya saboda takaici, ba zan gaya masa ba wallahi.

Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan Aishan tace

 Ni kin san me nake tunani? Account din da nake tara kudin hayar gidan zoo road ina da kudi sosai a ciki, duk da kudin kinga ni da su Abdallah ne. Da na yi niyyar ba zan taba account din ba sai nan da shekaru kamar goma lokacin Abdallah ya gama secondary watakila ma ya gama jami an, amma dai inaga a ciki zan biya.

 Kinga kuwa Abdallah yanzu ma zai shiga secondary din. To amma ai zaki iya yin hakan mu gani, Allah yasa dai kada abun ya dauki lokaci. Kuma ma kafin Abdallah ya gama secondary din inaga zaki samu ki mayar da kudin sai kiyi abunda kika tsara da su.'

 Uhm, hakane.

Haka suka karasa hirarrakinsu bayan sallar la asar Aisha tayi mata sallama ta wuce ta dauko Amira daga makaranta sannan suka koma gidan.
& & & .

Bata son Jibrin ya san itace ta biya kudin hayar don haka sai da ta bari washegari taje banki ta turawa mai POS kudin, daga baya ta turawa mai POS din account number din Jibrin din shi kuma ya tura masa kudin.

Bayan ya biya kudin ya tattara rasit din da sauran takardun biyan kudin ya bayar aka kai mata, ta karbi takardun ta adana.

Haka rayuwar Aisha ta cigaba, tun tana lissafin rabonta da Abba har ta daina rayuwarta kawai takeyi.
__

Kwanci tashi har lokaci yayi; duk yanda Sadiku ya so Abba ya canza masa makarantar da zai sake zana jarrabawar WAEC da NECO ya ki don haka dole ya hakura ya shiga cikin  yan ajin su Yusra.

Tun kafin a gama jarrabawar Sadikun suka hada baki da Yusra suka saka Mommy a gaba da magiyar so suke idan jarrabawa ta fito Abba ya kaisu Dubai ko Malaysia. Don haka ta saka Abban a gaba, kuma da yake sai yanda tayi da shi ba tare da wata matsala ba ya amince.

Musamman ya nemi agent wadanda sukewa mutane hanya zuwa kasashen; duk wani lissafi an yi masa kuma an bashi zabin jami oi biyu a Dubai daya a Malaysia. Kudaden da aka lissafa masa suna da matukar yawa; ba wai ba zai iya biya bane to amma abu ne da za a dinga biya duk shekara. Gashi yau saura abinda bai fi shekaru biyar zuwa shida ba yayi retire. Duk wasu kudi da ya tanada don yayi business Zahra ta cinye; domin idan tace yayi mata abu baya iya musa mata, ita kuma gani take kamar daman kudi ya tara don haka da ta fadi abu daya yayi sai ta fado wani. Tun tuni yayiwa kudin business din illa don shine ma dalilin da ya sa ya kasa komawa Dubai din, tun Alhaji Abubakar yana masa tuni har ya gaji ya kyale shi. Yanzun ma kuma da take maganar a kai yara Dubai karatu ragowar kudin business din zai kwashe ya kaisu tunda registration din farko yana da tsada sosai.
& & & & &

Kamar yanda ya saba kwanakin nan idan damuwa tayi masa yawa gidan Yaya Bello yake tafiya ya samu ya huta su yi hira domin a can baya samun wata damuwa, yau din ma bayan ya tashi daga aiki can ya nufa.
Tun safe yake lissafi a office din domin kansa har ciwo yake; a yau ne ya kamata ya biyawa Yusra da Sadiku kudin wata jarrabawa da suke bukatar su rubuta kafin tafiya kasar Dubai karatu. Sai dai har yanzu ya kasa tsayar da tunaninsa guri guda duk da dai ya amsawa Zahra.

Wajen karfe biyar saura kwata ya shiga gidan, nan take Karima ta bude masa falon baki ya zauna. Bayan sun gaisa ya tambayeta yaran tace suna islamiyya. Yace

 Yayan bai dawo daga kasuwa bane?

 Ya dawo, kayansa kawai ya ajiye ya tafi masallaci ina jin hira ya tsaya a can.

Ta fice daga falon domin kawo masa ruwa yayinda shi kuma ya kashingide domin ya jira dan uwan nasa.
Bai dade da zama ba Yaya Bello ya shigo gidan da sallama, nan take ya shige falon wajen dannuwan nasa.

Ya fahimci dan uwan nasa yana da damuwa amma sai dai duk wata dabara da zai masa don yaji cikinsa ya gagara. Duk da yana gani kamar wata fitnar ce mata suke masa a gidan tunda dama masu mace sama da daya basa rasa irin wannan abubuwan, don haka sai ya kyaleshi kawai yana yi masa addu a. Domin ya kula idan ya cigaba da takura masa to lallai zai iya daina zuwa gidan ma.

Bayan sun gaisa da Abban ya kwalawa Karima kira yace

 Kawo min furata mu sha ni da dan uwana.

Ba tare da bata lokaci ba ta kawo damammiyar furar tare da kofuna.
Suna shan furar suna hirarrakinsu na duniya.

Jimawa kadan Yaya Bello yace

 Ina Saddiku kuwa? Yana dai yin jarrabawar ko?

 Yana yi.

 To ma Sha Allah, Allah ya bada sa a. Ai jiran ya isa haka idan ba ayi wani abu ba sai kaga yaro ya kama shiririta. Ga Hauwa u nan itace  yar ajinsu yanzu har ta shiga level 2 a Bayero.

 Hakane Yaya. Shi din ma ai shi yayiwa kansa shirirta kuma uwarsa ta goya masa baya.

 Ai ka san sha anin mata sai a hankali, sai kasa ido sosai.

Sukayi shiru na dan lokaci.

Jimawa kadan Abban yace

 Yanzu ma wai so suke a kaisu Dubai suyi Jami an a can.

Yaya Bello ya tashi zaune daga kashingidar da yayi ya dubi Abban yace

 Dubai kuma? To kai kuma sai kace me?

 To Yaya ne me zance, sun hada kai da uwarsu sai faman magiya sukeyi.

 Wannan ma zance ne wanda bai kamata ka saurareshi ba, tarbiyyar nan mai wahala san?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? nan ka dauki yaro dan shekara goma sha ka mikawa duniya. A a ni ban yarda da wannan shirin ba. Da su da uwarsu tunaninsu duk ai iri daya ne idan ka barsu zasu kai ka su baro ka ne. Ga jami oi nan muna da su a nan cikin garin Kano harda ma na kudi, ka zabi wadda zaka iya ka saka su. In ya so shi Saddiku idan ya fito da sakamako mai kyau sai a tattare kudi a biya masa ya tafi Dubai din yayi degree na biyu, ita kuwa Yusra ai kaga mace ce sai abinda hali yayi, tunda ko kafin ta gama Allah ya fito mata da miji aure za ayi mata.

Ya jijjiga kai

 Hakane Yaya.

Jimawa kadan yace

 To ai uwarsu ta matsa ne Yaya.

 To ai ba saurara mata zakayi ba, idan Kuma tsoronta kake ji ni sai na zo gidan na sameta. Amma yara babu inda zasu je gaskiya, kuma musamman shi Saddikun wanda nake ta gaya maka sai ka kara sa masa ido.

 Hakane Yaya, in Sha Allah an bar wannan maganar tunda kace haka, ko babu komai kuma zancenka gaskiya ne.

Haka suka gama hirarsu Saida sukayi Sallar Magriba sannan Abba yayi masa sallama ya kama hanya.
& & & .

Tunda suka rabu da Yaya Bello yake neman hanyar da zai sanarda Zahra ya fasa kai su Saddiku Dubai karatu amma ya rasa, ya dai sanarwa agent din da yake masa aiki cewa ya fasa. Har sati ya zagayo bai sanarwa Zahra ba sai dai kawai shi a zuciyarsa ya yanke ba zai kaisu din ba.

Ranar Lahadi ce lokacin yara sun tafi tahfiz sai Yusra da Saddiku wadanda kowannensu yana dakinsa.

Yana zaune a falon sama yana kallon TV yayinda take kasa tana yiwa Jummai bayanin aiyukan da zata yi mata a gidan. Bayan ta gama bayar da bayanin ta haye falon saman ta shiga da sallama, bayan ya amsa sallamarta ta karasa ta zauna a kusa da shi tana fadin
 Barka da hutawa.

 Yauwa.

Dukansu suka mayar da hankali kan kallon talabijin din da take gabansu, jimawa kadan tace

 Uhm, jarrabawar su Yusra ta tafiya Dubai din an saka ranar ko har yanzu shiru?

Ya dan muskuta ya dubeta yace

 Oh, ashe fa ban gaya muku ba Yaya Bello yace ma a barsu a nan in ya so duk wanda ya gama degree dinsa na farko da sakamakon mai kyau sai a kaishi Dubai din yayi degree na biyu. Ai na ma sallami agent din ina ga su fara a nan BUK.

Ta kalleshi cikin bacin rai

 Yaya Bello kuma? To yanzu don Allah yaushe ya fara zaba maka abinda zaka yiwa yaranka? Shi da ba shi zai biya musu kudin makaranta ba. Kuma sai da aka gama magana ni da yara duka mun gayawa dangi zasu tafi Dubai karatu kuma sai kazo ka fasa.

Cikin halin ko in kula yace

 To sai ki gaya musu sai sun gama first degree zasu je Dubai din, tunda kin ga dai ai ba zan saba maganar Yaya Bello ba ko?

Ta gyara zama ta ja tsaki

 Wannan ai sai ya koma bakin ciki, don mutum ba zai iya kai yaransa ba sai ya hana a kai na wani? Gaskiya sai ka sake shawara don wannan ai mayar da aiki baya ne.

Ya gyara zama ya fuskanceta

 Ban tara kudin da na isa Yaya Bello yayi min bakin ciki ba kuma bana taba jin zan taba yi, kuma yana da damar ya yanke hukunci a kan dukiyata ko  yayana. Sai dai idan hukuncin bai yi miki ba ki sameshi kiyi masa magana.

Ya tashi ya shige daki ya turo kofa.

Ta bi

37 / 58