Uwar Sadiku Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Sakina Category :  Complete Novels

Chapter   36 / 58

105K to 108K   out of 172.2K words

na nuna mata karya fure take bata  yaya.

Nan suka karasa wuninsu sai bayan magriba sannan Aisha ta tuko motarta ta dawo gida. Tana shiga ta mayar da gidan ta kulle don ta san babu wanda zai sake shigowa.
& & & &

Kwanci tashi har an yi sati biyu rabon da Abba ya nemeta, zaman gidan haka ita kadai ya fara damunta. Gashi anyi hutun makaranta don haka babu inda take zuwa sai dai kawai taje islamiyya ranar asabar da halidi sai gidan Hajiya.

Don haka taje ta tsara Yaya Zainab ta dauko Amira; tun da zuwa yanzu duk sun san matsalar da take ciki, Yaya Abubakar ne kawai basu gayawa ba. Babu yanda basuyi da ita ba a kan ta koma gidan Hajiya amma ta ki don haka ma aka kyaleta. Haka aka bata Amira tunda Amiran tayi candy yanzu sai jiran admission da takeyi wanda ko da ya fito Aisha zata iya daukar nauyin kaita makarantar da daukota.
Daga ita har Amiran ba fita suke a unguwar ba balle su hangi koda yaran ne, domin itama Amiran Aishan ce take kaita islamiyya a motar ta daukota.

A haka karshen wata ya kare tana ta sa rai taga an kawo mata cefane ba a kawo ba, don haka dole taje ta yiwo cefanenta da akayi albashi. Duk wani abu da suke bukata ita da Amira ta siyo ta ajiye musu.
_

Cikin farin ciki take gudanar da rayuwarta tunda taga aikinta ya kama, ko da wasa Abban Sadik bai sake maganar Aisha ba rayuwarsa kawai yakeyi kamar yanda ya saba kafin ya auro Aishan.

Idan akwai wanda take jin zai iya bata matsala to Rukayya ce; don haka ta ja mata kunne sosai kuma ta sanar da  yan uwan duk lokacin da aka ga Rukayyan ta shiga gidan Aishan ko kuma ta kula Aishan ko da a unguwar ne a gaya mata. Don haka ta san babu wanda zai yi maganar Aisha a gidan.
& & & ..

Zuwa yanzu abu daya ta sa a gaba; mota take so Abban ya saya mata irin ta Aisha ko kuma wadda ta fi ta Aishan. Ta riga tayi masa magana kuma ya amsa, ya dai sanar da ita bashi da kudi amma ta bashi wata biyu zai samu sai a siya mata.

Gaba daya yanzu yanda ta tsara haka Abban yakeyi. Ta kula dai kamar bashi da cikakkiyar nutsuwa amma wannan bai dameta ba tunda yana yi mata yanda take so.

Hannun Sadiku tuni ya warke, yana nan yana zaman jiran jarrabawar da zai maimaita tare da  yan ajin su Yusra. Tun da hannunsa ya warke Abba ya saka shi a makarantar da zai koyi computer kuma ya saya masa computer, sai dai bai je makarantar nan ya kai na wata daya ba ya daina zuwa.

Idan ya fita sai kawai ya wuce gidan su abokinsa wanda suke kira Kolo su yi ta shaye-shayensu a can, da yamma sai ya dawo gida. Duk lokacin da yake bukatar kudi sai kawai ya cewa Abban zasu sayi wani abu a makarantar computer ko kuma ya gayawa Mommy ita sai ta karbo masa kudin ta bashi ba tare da wani bincike ba.

Halin da Saddiku yake ciki yana sosa zuciyar Jummai saboda yanda take kaunar Uwar Saddiku sai dai ta kasa gane abinda ya sa ita Uwar Saddiku bata ganin yanda yaron yake canzawa. Ta san abinda ya faru da Rahma don tun daga wannan lokacin ma Rahma ta ja jikinta don haka itama Jumman kawai sai ta kau da kai tana yi musu addu a.
___

Ranar Lahadi ce don haka yana gida bai je aiki ba.

Yana zaune a falon sama wajen karfe uku na yamma yana kallon TV. Daga dakinta ta fito inda ta kwantar da Sumayya ta karaso ta zauna a kusa da shi. Ya dubeta yace

 Yar rigimar ta kwanta.

Tayi murmushi

 Uhm, ta kwanta ai in sha Allahu idan akayi hutu islamiyya za a sakata tunda ko babu komai ta kai shekaru uku. Yanzu haka ma ta iya karatun kowa ga surutun tsiya.

 Hakane, in Allah ya kai mu next session sai a koma bokon ma da ita.

 Ai ko da an taimaka min, aje can a yiwa Anti ko Uncle.

Suka yi shiru suka cigaba da kallon TV din kowa da abinda yake tunani.

Jimawa kadan tayi gyaran murya tace

 Yallabi wai ya batun mota tane, na ji shiru fa.

Cikin yanayi na kosawa yace

 To ai na gaya miki bani da kudi amma in sha Allahu kada ki damu kwanan nan za a saya miki kota.

Ta dan bata rai

 To gani nayi ai saboda mota sai binka nake kana wani ja min rai, kullum sai kace karshen wata amma in watan ya zo kuma sai kayi shiru. Ya dai kamata a duba don na gaji da yawo a motar direba kawaye suna yi min dariya gaskiya.

Cikin murya ta lallashi yace

 Kiyi hakuri za a saya miki mota kwanan nan.

Ta zumbura baki tana muskutawa

 Kullum haka dai kake cewa, ai shike nan. Idan ma kudin ne naga ga dayar nan da ta lalace a tsakar gida nace a hada da ita a sayar sai ka cika ka sayi motar.

 To ai motar da kike so a saya ta fi haka tsada, kada ki damu za a sayi mota. Ke dai ki kara hakuri.

Sukayi shiru na dan lokaci, jimawa kadan ta tashi ta fice ta nufi falon kasa.

Ya bi bayanta da kallo yana jijjiga kai.

Ta matsa sai ya siya mata mota kuma ga irin wadda take so; shi kuma a halin yanzu bashi da kudin sayen irin wannan motar.
Gashi a halin yanzu baya iya yi mata musu kuma baya son ganinta a cikin damuwa, wasu lokutan idan tace yayi mata abu har ji yake kamar an kuntata zuciyarsa har sai yayi wannan abun da take so zai ji daidai. Don haka yanzun ma duk inda kudi suke nemowa zai yi kawai ya saya mata mota.
& & & ..

Kayan electronics din da ya siyo lokacin da suka je Dubai da Aisha suna nan anata siyarwa, kokari yakeyi idan aka gama sayarwa ya hada uwar kudin da ribar ya sake komawa ya siyo wasu kayan. Yana jin dadin yanda cinikin yake tafiya domin akwai riba sosai, musamman da yake abokin kasuwancin nasa mai amana ne sosai.
& & & &

Ba wai dare ne yayi sosai ba amma da yake yanayi ne na sanyi yaran duk sun kwanta har an rufe gidan. Shima Abban yana dakinsa a zaune a gefen gado yana 'yan dube-dubensa a waya yayinda Uwar Saddiku take kasa tana kawar da abubuwan da suke a bude kafin ta je ta kwanta.

Sai da ta gama kintsawa tsaf sannan ta sameshi a dakin. Bayan ya amsa sallamarta ta kwanta a gefensa ta ja bargo ta rufe kafafunta.

Bata dade da kwanciya ba wayarsa tayi kara, ya amsa kiran sannan ya kara a kunnensa.

Daga inda take kwance tana dan jiyo wasu daga cikin abubuwan da ake fada a daya bangaren, bata ganewa amma so take ta gane don haka ta tattaro duk wata nutsuwarta ta kara mikar da kunnuwanta don taji me za a cewa Abban.

Tun da suka fara gaisawa ta gane abokin kasuwancinsu ne Alhaji Abubakar; duk da bata san shi ba dai amma ta saba da jin sunansa kuma ta san Abban yace shine yake masa jagoranci wajen sayar da kayansa da ya siyo daga Dubai.

Bayan sun gaisa Alhaji Abubakar din ya sanar da shi akwai wani Alhaji da yake son kayansa ya turo kudin kaya naira miliyan shida don haka Abban ya duba business account dinsa yayi confirming don mutumin zai turo a debi kayan gobe da safe. Ya kuma sanar da shi akwai wanda yake son kayan kallo da AC complete set guda biyu amma shi so yake idan ya biya yaransu suje su hada masa kayan a gidansa sai ya biya har kudin aiki. Sukayi sallama suka ajiye waya.

A take ya duba account dinsa ya tabbatar da shigar kudin, shi kansa sai da yayi murmushi da yaga kudin. Ya tabbatar ya shiga harkar nan da kafar dama kamar yanda Abubakar din yake gaya masa.

Ya kirawo Abubakar din ya sanar da shi kudin sun shigo don haka zai fito da wuri gobe don suje gidan da ya ajiye kayan a dauka. Sukayi sallama suka ajiye waya.

Ta dan muskuta a inda take tace

 Kayan dai ashe suna tafiya.

Cikin murmushi da sanyin jiki yace

 Alhamdulillah gaskiya babu laifi in Sha Allahu kwanan nan zamu koma Dubai din a kawo wasu kayan.

Kwanakin nan har fargaba yake idan taji yana da kudi domin idan ta ji haka zata dinga yi masa lissafin abubuwa yana siya har sai ta ga kudin nan sun kare.Yanzun ma wannan maganar da tayi zuciyarsa ta fara bugawa da sauri ya san zata ce wani abu don tabbas ya san sai ta ci kudin nan tunda ta ji su.

Jimawa kadan tace

 To ni dai gaskiya tunda an sami kudin nan a saya min motata in ya so daga baya ko ma menene sai ayi, kada a bar ni ina ta jira. Ya kamata ace kafin satin nan ya kare motata ta zo tunda dai kudin nan gasu nan sun shigo.

 Wannan ai kudin business ne ba da su za a saya miki mota ba, amma in Sha Allahu za ayi kokari.

Ta tashi daga kwance ta zauna tana harararsa

 Business din ya fi ni mahimmanci kenan? Ka ce ba kudi kuma yanzu ga kudi in dai anyi niyyar siya min mota ina jiranta next week gaskiya.

Ta dan shagwabe fuska ta zungureshi da hannu tace

 Ka ji.

 To to in sha Allahu kafin next week din za a siyo motar.

Ya amsa yana jijjiga kai.

Haka ta kwana tana farin ciki don ta san bai isa ya canza wannan maganar ba yayinda shi kuma ya kwana yana lissafi; anya kuwa Zahra zata barshi ya hada kudin nan ya sake yin business din, yanda take yiwa kudin gibi ya fara yawa.
& & & &
Tunda sukayi wannan maganar kuma sai ya zama kullum idan zai fita sai ta tuna masa da motarta.

Don haka bayan kwana biyar da yin magana an gama cinikin kayan an diba haka ya dauka a cikin kudin ya sayo mata mota irin ta Aisha sai dai ita tata ruwan gwal ce ba baka ba.

Office aka kai masa motar bayan ya gama biya, daga nan kai tsaye yace a kai mata gidan a bata mukullin; ya hada dan aiken da Malam Ali direba.

Suna fita ya kifa kansa a kan teburin da yake gabansa ya runtse idanuwansa; kwana biyun nan jin kansa yake a cikin wani mawuyacin yanayi amma ya kasa fassara yanayin. Komai ya daina yi masa dadi gashi zuciyarsa tayi kunci kullum yana cikin damuwa amma be san me yasa yake duwar ba, ga kuma yawan fushi da yakeyi na rashin dalili.
A waje daya ne yake jin dadi shine idan yana gidan Yaya Bello, don haka yanzu kusan kullum idan ya tashi daga aiki gidan Yaya Bello yake tafiya yayi zamansa suyita hira da Yaya har sai ya gaji sai ya fito ya koma gida. Yana kama hanyar gidan kuma zuciyarsa zata sake komawa cikin damuwa.
Bayan son sayen motar nan amma idan Zahra tace yayi mata abu wasu lokutan baya ma sanin yayi sai ya gama; motar ma a kan haka ya saya mata. Yana dai fatan Allah ya sa kada ta kawo wata babbar bukatar idan ta gama dokin motar, don baifi wata daya ba da ta saka shi a gaba sai ya bata dubu dari biyar ta kara jari kuma nan ma haka dole ya bayar.

Ita kuwa Zahra ana kai mata mota da ta yi masa waya ya tabbatar mata tata ce ta karbi mukullin mota ta fice, gidan Amina ta fara zuwa suka sha hira sannan daga nan ta wuce gidan Yaya Murja ta nuna mata motar sannan ta dawo gida.

Ta riga ta saba yanzu sai wajen tara na dare Abban yake dawowa gidan, tunda ta bincika ta tabbatar gidan Yaya Bello yake zuwa abun ya daina damunta.

Don haka yau din ma bayan sallar isha i suka zauna a falon kasa ita da yaran don cin abincin dare, suna ci suna hirarrakinsu wanda duk a kan motar Mommy ne.

Yusra ta dubi Mommy din tace

 Mommy ni dai don Allah ki sa Abban ya saya min waya, kinga mun kusa fara exam din amma shi yace dole sai mun gama exams. Kawayena duk suna da waya kullum ayi ta daukan hotuna babu ni ana min dariya. Kin ga Fathiyya Sulaiman ma iPhone ce da ita, don Allah nima ki sashi ya saya min iPhone tunda na ga kamar yanzu yana da kudi. Kin ga ma idan muka gama exam din ai an huta.

Tayi dan murmushi tace

 Ai nace za a saya miki kafin ki gama exam din kuma iPhone din za a saya, yanzu ki bari mu gani zuwa next week in sha Allah zai saya.

Ummi tace

 Mommy da Yaya Rukayya ma a saya mata wayar sai mu dinga yin game tare , ko Yaya Rukayya?

Sukayi dariya gaba daya, Rukayya tace

 Ai na san Abban ba zai taba yarda ba ni na ma hakura sai na yi candy din tunda Abba yace idan mutum yayi candy dashi za a je shop din ya zaba. Sai mu tafi tare ko Ummi?

Suka tafa.

Mommy tace

 Ai kuwa kin hutar da mu.

A dai dai nan Saddiku ya shigo, ko sallama bai yi ba yace

 Mommy na ga wata dalleliya, itace motar tamu?

Yusra tayi caraf tace

 Mommy kin ji ikon Allah wai motarsu; wallahi Mommy ki hanashi hawa motarki tun kafin a zo a kuma.

Mommy ta bata rai tana hararar Yusran

 Ki fadi alkhairi ko kiyi shiru, hatsarin irin wannan ba zamu sake ganinshi ba har duniya ta nade.

Cikin jin dadi yace

 Gaya mata dai Mommy, mota dai sai na hau sai dai dan bakin ciki ya mutu.

Yusra ta zumbura baki tana harare-harare yayinda Mommy tace masa

 Sannu sarkin fin karfi, to wannan motar ba ta hawanka bace iyakacin ka da ita kallo. Idan aka kwana biyu dai nayiwa Abban magana ya saya maka taka kaima.

Ya zaro ido ya matso kusa da ita

 Allah Mommy, gaskiya amma da kin gama burgeni. Amma don Allah Mommy dalleliya nake so kamar dai takin nan.

 Bari mu gani, ka maida hankali kaci jarrabawa kaga sai a ji dadin saya maka mota.

Kafin ya amsa suka ji shigowar Abban gidan bayan da Malam Sajo ya bude masa gate. Babu wanda ya mike da sunan yaje ya taro Abba sai Rukayya wadda ta mike tana fadin

 Ga Abba nan.

Ta fice da sauri.

A take Ummi da Sumayya suka bi bayanta da gudu suna oyoyo.

Jimawa kadan Rukayya ta shigo rike da jakar laptop din Abban da mukullin motarsa ta wuce sama, bata gama hayewa benen ba yashigo yana rike da hannun Ummi yayinda yake dauke da Sumayya.

Bayan ya amsa sannu da zuwansu yace

 Saboda motata ta tsufa shine aka saka min sabuwar mota a gareji aka koro tawa waje ko?

Tayi dariya tana mikewa tsaye tace

 Wallahi mantawa nayi, lokacin da nayi parking din ne da akwai rana shi yasa wai da naga mai wajen baya nan sai na dan fake ta a nan.

Ya wuce saman yana dariya yayinda ta tashi ta bi bayansa.
& & & .

Yanda ta kwana tana murna haka shima Saddiku ya kwana cikin farin ciki; motar ta burgeshi sosai ya san yanzu Shima ya wuce raini a wajen abokai. Duk da ta gaya masa ba zai hau mata mota ba amma ya ci alwashin sai dai ita ta hakura ta bar masa motar; kuma kamar yanda ta fada ko da ma ta sa an siya masa mota idan dai bata kai haduwar wanna din ba to sai dai idan ita ta hau waccan shi ya hau tatan.

Kafin ya kwanta bacci sai da ya yiwa abokansa waya ya sanar dasu an saya masa mota gobe ma da ita zai fito.

Ko da gari ya waye da wuri Abban ya fita bayan Malam Ali ya fita da  yan makaranta, shi kuwa Saddiku yana ta kaiwa da kawowarsa a falon kasa tare da Sumayya don ya cewa Mommy sai karfe goma zai tafi computer school dinsa.

Sai da ya bari ta shiga wanka sannan ya shiga dakinta ya dauki mukullin motar ya fice daga gidan.

Tana wanka ta ji an bude gate tayi zaton Malam Ali ne ya dawo don haka bata damu ba.

A lissafinta idan ta fito daga wankan ma fita zatayi ta je gidan Suwaiba sannan ta biya sahad tayi sayayya duk don ta kara dana motar; domin yanzu idan zata je unguwa ta daina gayawa Abba sai dai idan babu direba a gidan ta kan gaya masa don ya turo mata direba.

Sai da ta fito daga wankan ta gama shiryawa sannan ta fito daga dakin, tana fitowa ta sauko falon ta sami Sumayya a kicin wajen Jummai, bayan sun gaisa da Jummai tacewa Sumayya

 Ina Yaya naki?

 Ya tafi unguwa.

Jummai tace

 Ai ya fice Hajiya.

 To nima fitar zanyi, bari na karasa shiryawa.

Har ta kama kafar benen hawa sama ta dawo ta leka tsakar gida, babu komi a garejin Abba inda ta ajiye motarta. Take ranta ya

36 / 58