RAYUWAR MACE BY RANO

Author :  RANO Category :  African Stories & Novels

Chapter   27 / 30

78K to 81K   out of 87.6K words

a saman chest dinsa ta dora fuskar ta tana murmushi k'asa-kasa, hakan da yayi ya haifar mata da kasala kwarai, kokarin tashi tayi daga jikin nasa ya sake rukunkume ta, ya manna ta da jikin nasa sosai yayi crossing kafarsa da tata waje daya, ya dago da ita a jikin sa ya jawo kofar motar ya rufe ta.

"Zaki rakani wani waje? Inaso naga kunshin da komai da komai, yadda zan ga nawa ya kamata na biya matar da ta gyara min ke."

" Ya Hadiza na jirana."

" Aina?"

" A gida, kasan gobe ne walimar."

" Gaskiya tayi hakuri, idan ba haka ba sai kawai mu wuce gida gobe sai na kawo ki walimar. "

" Wai,.. su Rauda su sakani a gaba kenan, yau da goben duk daya ne."

" Za'a min wayo, ni dai gaskiya a'ah, hakuri na ya kare. "

Shiru tayi bata sake cewa komai ba, yayi murmushi kawai ya fito ya koma wajen driver ya kunna motar suka bar layin. Wayarta ta ciro daga jakarta taga missed calls din Ya Hadiza, ta kirata tana ayyana me ma zata ce mata? Tana dagawa kuwa tace

"Asma'u shiru wai baku gama ba har yanzu?"

"Na'am, am ammm mun gama."

"Ok, bari Abbati yazo ya dauko ki toh."

"A ah ba sai yazo ba, mun taho ma amma wai zamu biya mu siya wani abun sai mu taho gidan."

"Oh toh shikenan sai kun dawo." Ta kashe wayar, kallon sa tayi shima ya kalleta yayi mata dariya

"Kin cika kunya, kice kin wuce gidanki kawai amma shine kike ta kwana kwana ko?"

"Ba zan iya ba."

"Da ma ni kika bawa na fad'a mata ai."

"Kamar gaske."

Tace tana dariya, dariyar ya saka shima ya maida hankalin sa kan driving din da yasan ko me yasha ba zai taba iyawa ba, shi din ma kunyar ce dashi kamar itan, a wajenta ne kawai yake ajiye kunyar a gefe shi kansa kuma be san dalilin da ya saka baya jin kunyarta ba sam.

"Your hand is very soft." Ya kamo hannun ya dora a saman geer, ya dora nasa akai yana murzawa.

"Me ake saka ma hannu ya zama haka ne? Kinji kuwa?"

"Uhum."

"I love it, I love everything about you in particular."

"Ka daina fasa min kai."

"Ba wani hyping, it's the truth, Alhamdulillah Ya Allah!"

Sautin murnushin ta kawai yaji, yayi murmushin shima yana jaddada godiyar sa ga Allah, yana kuma addu'ar samun nutsuwa da kwanciyar hankali a tattare da ita.

Office din nasa yau ma suka zo, yayi parking a daidai in da sukayi last, ya kuma kama hannun ta suka shiga ciki kamar wanchan lokacin amma wannan babu kowa kamar wanchan lokacin, bud'e kofar yayi suka shiga ciki. Ya kunna hasken office din, sai a lokacin ya ganta sosai, ya bud'e baki ba tare da yace komai ba, kamar wadda aka sauyata da wata ta daban, ga wani fresh da ya ga ta kara hade da wani shihirtaccen kyau na ban mamaki, be san lokacin da ya rungume ta tsam a jikin sa ba, ya dinga shakar kamshin jikinta. Ji yayi kamar zai zame a wajen, ya cikata yana rik'e hannun ta, ya bud'e wata kofa dake gefe a cikin kofar, suka shiga ciki. Dan karamin gado ne wanda be fi yaci mutum biyu ba a ciki, sai tarin wasu kaya a gefe kamar takardu ne ma suka fi yawa. Wajen gadon ya kaita ya zauna yana jawo ta saman kafarsa, ya zaunar da ita yana fuskantar ta, kanta a k'asa ta kasa bari su hada ido dan ta lura kamar akwai matsala a yanayin sa.

"Husnaaa." Ya kira sunanta cikin muryar sa me zurfi, kasa dagowa tayi ya sake kiranta a karo na biyu muryar sa na sake shigewa ciki sosai, dagowa tayi a hankali ta kalle shi tayi saurin sauke kanta k'asa ganin yadda fararen idanun sa suka shiga ciki sosai kamar wanda ya sha wani abu, gabanta ne ya hau dukan uku uku tunawa da tayi komai zai iya faruwa, bata manta kalar wahalar da tasha ba a hannun Adam duk da ta san ba zata taba shan irin ta ba amma kuma har ta gama zaman gidan Adam bata daina shan azaba ba, duk da nashi har da tsana amma ta taba karantawa wata macen har sai tayi haihuwar farko sannan take samun sauki, tsoron ta ne ya karo kokarin da taji yana shafa ta yana kokarin lallai sai ya saka idon sa a cikin nata

"Hakuri na ya kare Husna, I can't, I just can't! Ba haramun bane, ba laifi bane."

"Shikenan!" Ta furta zuciyar ta na tseren gudu, ta saddakar yau me rabata da Abdallan sai Allah, a hankali cike da nutsuwa da kamala ya shiga biyar da ita cikin salon sa me matukar kayatarwa, bata san lokacin da ta saki jiki ba, har ya samu nasarar maida ta kasan shi, yayi mata rumfa akanta yana hade bakin su waje daya, bayan ya gama furta mata kalamai masu ratsa zuciya.

A duk yadda tayi tunani ko hasashen abun ya wuce nan, soyayya ce me taushi da dadi ta danne duk wani ciwo da wahala da take tunani da hasashe, ba zata ce babu ba, musamman saboda gyaran da tasha na musamman amma kuma be barta ko da na sakan daya bane bare har hakan yayi tasiri a gareta, she's so gentle cike da charisma, full of energy amma ba na banza ba irin na Adam, a nutse yayi koman sa bakin sa dauke da addu'ar da annabi Muhammad SAW ya koyar damu a lokaci irin wannan.
Sannu yake ta faman jero mata babu kakkautawa, hade da saka mata albarka, tana kwance a saman kirjin sa hannun sa na zagaye da ita dayan kuma ya tura shu cikin gashin ta da ya wargaje yana tattaro shi, santsin sa da kamshin na shigar masa hanci. Sai da ya tabbatar ta dawo daidai sannan ya tashi ya nufi toilet ya hada mata ruwa me dumi sosai, ya zo yace ta taso,idonta a rufe da ya shigo dan wata sabuwar kunyar sa ce ta sake kama ta, har bata jin zata iya hada ido dashi , ga Ya Hadiza da tasan ta gaji da jiranta, da wanne ido ma zata fara shiga gidan su me ma? Za'a iya harbo jirginta wallahi, dan mara gaskiya ko a cikin ruwa gumi yake yi, bare iyayen da suka haife ka duk motsin ka sun san me kake nufi.
Da taimakon sa ta tashi tayi abinda yace din, ya tayata suka gama, kansa tsaye yake komai ko kunyarta baya ji, tayi ta jinjina hakan a ranta dama namiji in dai anan bangaren ne toh basu da kunya ko kad'an, kamar ba zai aikata ba, nan nan kawai yake da ita har ta gama ta saka kayan ta, ta dawo cikin office din ta zauna ta barshi a ciki, sai gashi ya fito rik'e da riga a hannu be saka ba, tayi saurin dauke kanta dan bata saba ganin namiji a haka ba, ko Adam iyakar ta dashi ya shigo yayi abinda zai ya kara gaba, yana lura da ita kunya taji, sai yazo ya tsaya a gabanta ya mika mata rigar yana marairace mata

"Help me pleaseeee."

"Um Um."

"Kina so mu kwana anan? Dan dama ni wallahi bana so ki koma."

Da sauri ta tashi zata karbi rigar ya rik'e yana girgiza mata kai

" Na ma fasa, anan zamu kwana kawai. "

" Dan Allah. "

" Zo ki kwanta ki huta sai gobe, ba zan iya fita yanzu ba. "

Ya juya ya shige ciki, tsaye tayi a wajen cike da tunanin abinda ya kamata tayi, shiru be fito tayi tunanin da gaske yake kawai sai ta bishi, ta same shi a kwance a gadon be kuma saka rigar ba.

"Please dan Allah."

"Um um, bacci nake ji, zo mu kwanta, inaso naji heartbeat din matata. "

" Dan Allah. "

Lumshe idon sa yayi yana tariyo abinda ya faru yan mintunan da suka wuce, murmushi ne ya subuce masa, ta kalli yadda yake murmushin sai ta samu kanta da murmusawa itama, tana tsaye sai da ya gama yangar sa sannan ya tashi yana mika mata rigar

"Samun kafin na chanja shawara."

Da sauri ta karba ta shiga saka masa, duk da ya kere ta nesa ba kusa ba a tsayi, amma babu yadda ta iya dan ba zata zo ta kwana ba saboda kunyar da zataji. Tana gama saka masa ya rungume ta yana jujjjuya su a dakin.
Da k'yar ta samu ya dauki car key dinsa suka fito, suka tafi. Ya tsaya ya siya mata dinner da wasu tarkacen kayan sannan ya wuce da ita gida. A kofar gidan ma sai da tayi da gaske sannan ya kyale ta, ya fito ya raka ta har cikin harabar gidan nasu, ya kama hannun ta ya saka mata kudi masu yawa

"Kudin kunshi da kitso, MD zai kawo drinks da safe, da sauran abubuwan da za'a bukata, da daddare zanzo mu wuce. "

" Allah ya kaimu, thank you so much, jazakallah bhi khair Allah ya kara budi "

Murmushi yayi mata yana me jin dadin addu'ar, ya amsa da Amin k'asa k'asa. Har ta juya ta soma tafiya ya tsayar da ita, ta tsaya tana juyowa, ya taho suka hadu, ya rankwafo zuwa daidai saitin kunnenta

"You are very sweet." Ya furta in a romantic voice and way, da sauri tayi ciki kamar wadda aka tunkuda, ya kyalkyale da dariya ya juya ya bar gidan yana shafa kansa, yana jin sa kamar wanda yake yawo a saman gajimare!




RM
   41

***Duk suna tsakar gidan wannan karon ma, dan duk a gida zasu kwana saboda shirye shiryen ranar goben, kamar wadda aka sarawa kafa haka taji, amma sai taga kamar basu fuskanci komai ba, sannu da dawowa suke mata dukka sai Ya Hadiza da ta dan harareta cikin sigar wasa tace

"Kika barni ina ta jira."

Bud'e baki tayi zatayi magana ta katse ta Kuma

"Jeki ajiye kayan kizo dan Allah, gwara a kitse kan kafin gobe dan ba lallai na samu damar yi miki ba."

"Wai kitso zakuyi Ya Hadiza!!?" Rauda tace tana waro ido

"Ba gwara a kitse shi ba, da ta barshi haka." Umma ta sako baki tana daga gefe tana duba sauran kayayyakin da aka siyo

"Allah gwara a bar mata, ai yafi yasha mai tayi parking din sa wallahi."

"Kufa kun fiya shiririta, kitson be fi umma?"

"Allah Umma gwara dai ta barshi haka daga baya sai tayi kitson."

" Ke Asma'u me kike so?"

" Zanyi daga baya umma." Tace da sauri dan tabbas a yadda kan nata ya koma sai duk sun harbo jirginta, shiyasa da Rauda tayi maganar taji kamar taje ta rungume ta saboda tsabar dadi.

" Ai shikenan, sai a barshi a hakan ai."

Daki ta mike ta shige da sauri, ta sauke ajiyar zuciya tana sakin murmushi, da ba dan Rauda ba da ta sha kunya yau, dan har lokacin a jike gashin yake da ruwa gashi kuma duk sun san da maganar gyaran kan zasu ce Ina ta samo ruwa akanta, toilet ta shiga da sauri bayan ta dauko hand-dryer dinta a cikin kayanta da Hidaya ta hade mata su waje daya, ta shiga da ita ciki dama rechargeable ce ta shiga busar da kan. Sai da ta gama sannan Hidaya ta shigo dakin ta ajiye abu ta fita, sauya kayan jikin tayi ta fito wajen su, ta samu sun koma cikin falon saboda wutar da aka kawo, tana zama wayarta tayi kara, Abdallah ne yake kiranta, da sauri ta kashe hasken wayar tana kallon su, sake kira yayi bayan wanchan din ya katse,

"Ki daga mana, ba kiranki ake bane!?

" Wata number ce take ta kirana, idan na daga sai ayi shiru shi yasa bana dagawa kawai."

"Ki sakata black list kawai."

Ya Hadiza tace tana cigaba da hirar da ta dauko

Text message ya turo mata jin bata daga ba

"Baby.. How are you feeling? Hope babu wata matsala ko? Take care of yourself.. xoxo"

Murmushi tayi kawai ta sake kifa wayar aka cigaaba da hirar da suka kusan kai dayan dare sunayi bayan sun gama kallon lefen Asma'un a karo na kusan uku, sai an gama sai a sake tuno kaza sai a sake budewa cike da yabawa, Rauda tuni ta sulale tayi bacci sai ita da Ya Hadiza, Ya Amina, Batul da Hidaya. Ita ta fara tashi dan gaba daya kawai daurewa take amma gabobin ta ciwo suke mata sosai, wanka ma take so ta fara yi kafin ta kwanta amma kuma bata jin zata iya, so kawai take ta ajiye hakarkarin ta a k'asa ko zata ji saukin jikin nata. Tana kwanciya bacci me nauyi ya kwashe ta, cike da mafarkin Abdallah. Babu wanda yayi mata maganar motar ta, yadda suke shirya dama sai da safe idan an tashi, bayan an yi breakfast sai kuma ayi breaking mata news din, Abbati ne gaba a tsara hakan umma dai bata ce komai ba a lokacin sai murmushi kawai da take cike da jin dadin yadda rayuwar Asma'un take sauyawa zuwa wani bigire na daban.
Da safe ta tashi da karfin jiki dana zuciya, ranta fes kamar an mata bushara da gidan aljanna, har yan uwan umman sun iso saboda tayin aikin abincin da za'a yi tun duku-duku sai karin ma'aikata uku da aka karo, tana nade akan gado tana kallon duk abinda yake wakana Hidaya ta kawo musu fanke da Lipton suka ci, sannan ta dauki waya ta masa reply din text din da yayi mata jiya da daddare.

"I'm fine, how about you?" Ta rubuta masa ta ajiye ta mike ta fita.
Yana tsaye kusa da Baba Alhaji da yake nuna masa wata takarda a harabar gidan text dinta ya shigo, cigaba da abinda suke yayi har sai da Baban ya sallame shi bayan ya saka hannu a takardun sannan ya wuce zuwa chan gate ya samu bencin da gateman dinsu yake zama ya zauna ya zaro wayar ya shiga message yayi mata reply yana daga kansa sama, sanyayyiyar iskar safiyar na busawa cike da wani yanayi da be taba riskar irin sa ba

"Alhamdulillah, thank for yesterday, kin biya ni har da kari ma, Allah yayi miki albarka ya barmu tare har abadah."

Sosai yayi relaxing a wajen har rana ta soma isowa in da yake, ya cigaba da shan ta kafin ta soma dukan fuskar sa, sannan ya tashi ya koma ciki ya hau shiryawa, dan so yake ya gama komai yau da wuri ya dawo gida, ana magriba zai je ya dauko matar sa ba zai jira ba, ba kuma wani zai wakilta dauko masa ita ba, shi kadai ya isa.

Dawowa dakin tayi da zumudin ganin reply dinsa, ta dauka tana karantawa tana murmushi, sai kuma ta lunshe idon ta, ta zauna tana sake maimaita text din tana tuno tsadaddun kalaman sa na jiya da duk in da ta motsa sune suke mata amsa kuwwa a kanta, bata san haka soyayya take da dadi ba sai a wannan lokacin da ta hadu da gwarzo tamkar Abdallan, wanda ita kadai ta san wannan bangaren nasa, idan ka ganshi a haka zaka rantse ko hannu aka saka masa a baki ba zai ciza ba.

***Sosai hidima ta kankama kan kace menene gidan ya kacame sai kaya kaya kawai ke tashi, tayi wanka ta saka wani lace me kyau golden da yellow, wanda ya haska ta sosai ta fito amayar ta sosai ba kamar bikin Adam ba, tun da ta fito tsakar gida mutane sukayi mata cha, kinyi kyau kinyi kyau. Murmushi kawai take har ta isa wajen da kanwar Umma Anty sadiya take a zaune, ta durkusa a gabanta tana mata magana sai ga Hajiya mama sun shigo da ahalin ta, wani irin sak tayi ganin Asma'un kamar wadda aka sauya ta da wata ta daban, bata jin dadin jikinta tunda Adam ya dawo gida dan ko lekowa be yi ba tun bayan dawowar sa bare yazo ya gaishe ta, sau biyu tana shiga gidan bata ma ganin sa sai Fido tace mata yana sama baya son hayaniya, abun yana damun ta har ciwo tayi amma haka ta hakura, kamar ba zata fito yau din ba ma amma ta daure sai kuma tazo taga Asma'un sai duk taji damuwar ta, ta karu da tunanin damar da ta kwace musu ita da Adam din, Allah yayi musu gamdagatar amma suka wofintar da ita har ta kubce musu. Kowa sai da ya lura a wajen da yadda take kallon Asma'un kamar ranar ta soma ganin ta, ita kanta Asma'un sai data tsargu da kallon ta shige dakin umma da saurin ta sai a sannan Hajiya Maman ta dawo hayyacin ta, ta hau wayancewa cike da borin kunya. Daki umma tabi Asma'un tace mata ta dinga addu'a saboda baki, ta amsa da toh umman ta fita ita kuma ta zauna a wajen da sauran sisters din umma suka cigaba da zaman su a dakin har aka zo lokacin walimar, dakin ta, ta koma ta sauya kaya zuwa wasu daban suka fita zuwa compound din inda aka gabatar da walimar, aka ci abinci aka sha abun sha sannan Anty Hauwa ta sake tunatar da mutane akan rayuwar aure da kuma hukunce hukuncen da suke kan mace wanda ya zama wajibi ta sauke nauyin domin samun rahmar ubangiji, daga nan ne kuma Abbati ya shigo mata da motar wanda ta shiga tsananin mamaki, Itace motar da ta nuna a ranar, duk da ya nuna mata da gaske yake amma bata ji a ranta cewa ta chanchanci mallakar hadaddiyar motar ba, har kukan dadi sai da tayi dan farin.

***Sabuwar shadda ce a jikin sa wadda tayi matukar dacewa da fatar sa, kansa babu hula ya ajiye ta a gefen sa, ya dauki turare yana fesawa MD ya turo kofar jikinsa sanye da wando 3quarter da riga armless, ta cikin mirror ya kalle shi ya cigaba da abinda yake yi yana kallon sa yana duba babbar rigar da ke ajiye a saman gadon sa.

"Are you for real!?"

"What?"

"Kai kadai zaka je!? Ba zan raka ka ba?"

"Bana bukata, ni kadai na isa."

"Allah sai naje, bari kaga." Ya haura ta saman gadon ya isa gaban wardrobe dinsa ya ciro sabuwar shaddar sa shima ya hau sakawa, be

27 / 30