RAYUWAR MACE BY RANO

Author :  RANO Category :  African Stories & Novels

Chapter   22 / 30

63K to 66K   out of 87.6K words

tabani dan ni ba yar iska bace."



"I'm so sorry ba zan kara ba."



Ya kama kunnen sa ya rik'e yana so ya saka kwayar idon sa a cikin tata, rasa abinda zatayi tayi, kawai tayi shiru tana duban kasa, dan ta fad'a masa ita bazawara ce shine zai rungume ta kenan, mutane da yawa irin kallon da suke ma wadanda sukayi aure suka fito kenan, shiyasa ko mazan sun zo wajen su sai su bisu da maganar banza, bata zaci haka daga gareshi ba, amma kuma idan ta tuna duk mazan halin su daya, ba ka iya gane musu sai kawai ta sallama. Knocking akayi, kafin ya turo ya shigo hade da sallama.



"Amaryar mu."



"Uhumm." Tace tana sake yin kicin kicin da fuska dan ta lura ma bakin su daya



"Kinga yadda abu ya kasance ko? Al'amarin Allah kenan, babu yadda bata kasancewa. "



" Allah ya bada zaman lafiya da zuria dayyiba, I can't wait na ga na zama daddy wallahi, woo wa yaga Daddy Mudan. "



Harara Abdallah ya watsa masa yana rik'e kansa, surutun MD yayi yawa wallahi, a duhu ya sakata Dan bata fuskanci komai a maganar tasa ba,tunani ta shiga yi, ta tuna dazu wajen magriba Abba ya shigo ya sameta, ya tambaye ta idan har ta amince da Abdallan, tace masa eh, daga nan ya fice da sauri bayan yace wa Umma yana zuwa da bayani. Bata kaao komai ba, ganin basu dade da tafiya ba, daga nan kuma ta shiga sabgar gabanta dan bata ma fito ba saboda Adam yana nan. Muryar MD ta katse mata tunanin ta, ta kuma kara tabbatar mata da abinda take tunani ya faru



"Zamu shirya duk events din a satin sama in sha Allah, komai ake bukata ni za'a tambaya, please."



"Yayi toh, can you please excuse us?"



"Why not? Idan ma cewa kayi na tafi gaba daya anan zaka kwana kaga lafiya lou, idan kuma kayan ka ma zan kwaso maka ayi duk shirye shiryen kana nan shima daidai ne."



Kunya maganar ta bashi, yayi masa banza yana masa kallon zaka sani, shi dai MD dariya kawai yake yi , ita kuma Asma'u tsabar shiga ruduni ta gaza cewa komai, idan har maganganun MD din gaske ne, kenan aure aka daura mata da Abdallan, ji tayi kafafun ta sun mata nauyi, taji tana bukatar ta zauna dan har yar rawa jikin ta ya dinga yi, a wajen ta durkushe MD na fita, yayi saurin zuwa ya durkusa akan guiwoyin sa yana rik'e hannun ta



"Me yake damun ki!? Baki da lafiya? Wani abun ne?"



Girgiza masa kai tayi, ya sauke ajiyar zuciya yana sakin hannun ta da ya tuna tace masa bata so, kasa kallon sa tayi, ta dinga jujjuya maganganun a ranta, ba zata ja da hukuncin Allah ba, ba kuma zata bijire masa a duka abinda ya zaba mata ba, zata karbi duk wani zabi da hannu bibiyu, hzd ehakan ta tabbata yana cikin kaddarar ta, babu wanda ya sake magana a cikin su, tana durkushe a wajen shi kuma yana tsaye kyam a kanta yana nazartar yanayin ta, be san a wanne matsayi ta ajiye shi ba, dan yana ji da ganin kamar ba'a kyauta mata ba, kamar an mata garaje da ba'a barta ta tantance shi sosai ba, duk da yasan hakan ba zai zama matsala ba,kuma hakan zabin Allah ne.

Mikewa tayi bayan ta dau lokaci a durkushe sannan tace



"Kayi hakuri."



Be san hakurin me take bashi ba, amma sai ya samu kansa da jin dadi, ya daga mata gira yana sakar masa tsadadden murmushin sa, maida masa tayi tana sunne kanta k'asa kunyar shi na ratsa ta,



"Zo ki zauna."



Yace mata yana nuna mata gefen sa bayan ya zauna, ba musu ta karasa a nutse ta zauna da dan tazara kad'an a tsakanin su, matsowa yayi ya jone da jikinta har kafadarta tana gogar tasa, hannun ta ya lalubo ya rik'e cikin nasa yana dan murza su a hankali, yanayin bugawar zuciyar ta ya sauya nan take, ta dinga jin wani irin yanayi da bata taba fuskantar sa ba. Ta zata wata magana xasuyi amma sai taji shiru har ta dago da niyyar ganin abinda yake amma sai taga kawai ita yake kallo kuri, duk sai taji kunya amma shi ko a kwalar rigar sa., Sai ma sake tsattsareta da yayi yana kokarin lallai sai ya saka idon shi cikin nata, sun jima a haka kafin yayi ta maza ya daure ya cikata yana mikewa



"Bana so na tafi, but i have to, kar Abba yaga rashin hakuri na."



Shafa kansa yayi ya mikar da hannun sa zuwa gareta, ya mikar da ita tsaye suna fuskantar juna



"My wife."



Ya kawo fuskarsa daidai tata ta hanyar rage tsawon sa, dan tsaf zai sakata a cikin rigar sa ya boye ta, dago idon ta, tayi da niyyar kallon sa, sai yaga kamar tayi masa fari, wani yarrr yaji tun daga kansa zuwa tafin kafarsa, bakin sa ya kai kuncin ta s kasalance ya manna mata kiss, ta duka da sauri tana damke idon ta



"Ki kula min da kanki kinji?"



Bata iya amsawa ba sai daga kai da tayi alamar toh, cikin sakannin da basu gaza goma ba ya fice fit daga falon dan abinda yake ji zai iya sashi aikata abun kunya. Yana fita ya tarar da driver yana jiran sa, MD ya tafi shine ya kirashi yazo ya dauke shi, babu bata lokaci ya fad'a bayan motar ya ja suka bar layin.

Tamkar wadda aka dasa a wajen haka ta kasa ko da daga kafarta ne, wani feeling me matukar dadi ya dinga mata yawo, soyayyar sa me sanyi da tsayawa a rai, bata taba experiencing hakan ba, baa taba nuna mata so irin haka ba, shiyasa take jin ta kamar wata bakuwa, kamar wadda aka chanja ta da wata ta daban. Da k'yar ta ja kafafunta zuwa cikin gidan nasu, kunyar Umma da Abba na sake dabaibaye ta. Idon Umma fes akanta ta shigo, sai taga kamar umman ta kara mata haske akan hasken ta da ta Santa dashi, bata sani ba ko tsantsar farin cikin da ta hanga a cikin idon ta ne ya sakata ganin farin nata ba, zuwa tayi ta zauna a gefen Umman tana jan mayafin jikinta ta sauke shi k'asa.



"Umma ina Abba?"



"Ya fita sallah, inaga ko ya tsaya wajensu liman."



Sai kawai ta fad'a jikin Umma, ta dora kanta a kafar umman ta runtse idon ta, tana tariyo abinda ya faru yanzu.



"Nasan ba dan dare ba, babu abinda zai hana yan uwanki zuwa, amma nasan gobe da wuri zaki gansu, dan duk munyi waya kowa murna wallahi."



"Umma wai ya akayi haka ta kasance?"



"Al'amarin Allah fa, ke dai ki bar sha'anin aure wallahi."



Maida idon ta, tayi ta kulle tana jin yadda Umman take yabon abun, tana kuma kwararo addu'ar dacewar Asma'un da fatan nasara a komai ma, a ranta take amsa amin, tana saka ram samun nutsuwa da Abdallan, wanda a yanzu take jin kamar ya karbe rashin ta ya tafi dashi, kamar akwai wani gagarumin abu da take jin tana kewa. Daina jin maganar Umman tayi sai sama-sama, ta fad'a tunanin shi da hoton fuskar sa, sajen sa da quarter million dinsa shi yafi komai tafiya da ita. Samun kanta tayi tana murmusawa, ta mike daga kan kafar Umman ta fad'a daki yadda zata more tunanin shi sosai ba tare da wani abu ya katse ta ba, wayarta ta jawo da nufin kiran Rauda ta tarar da missed calls da yawa sai text message dinsa guda biyu, budewa tayi tana fadawa saman gadon idon ta kyam akan wayar dadin kamalan na ratsa ta



_"The first time we met, I can see that you and i are meant to be together... Your eyes were so gentle, your smile so true... You walked lightly into my heart, captivating and lovely to my mind. For you are my heart, my soul and my oneness. With you i know that I will find my completeness,my eternal peace of mind. You are the one I want to spend my life with. Both of our hearts will forever bond into all happiness, falls, pains and sorrows. I promise together we will meet tomorrow. I love you so much my wife."_ #

Juyi ta dinga yi a saman gadon ita kadai kalamansa na ratsa ta, wayar da ke saman kirjinta ta yi kara, ta dan zabura kadan dan tayi nisa a tunanin, Rauda ce, dagawa tayi cike da zakuwa tace



" Rauda."



" Wayyo...Yaa Asma'u."



"Wallahi da k'yar zan iya bacci yau, kinji yadda nake ji kuwa? Farin ciki kamar na ganni a gida wallahi,dan ma Umma tace kar muzo ne da tuni nazo

"



" Yau da goben duk daya ai, idan da rai da lafiya."



" Haka ne,ya kika ji? Nasan ya hadu ba karya wallahi, irin wanda ya dace dake ba wanchan ya Adam din ba, fari kamar farin kosai. "



" Ke ko? "



" Allah kuwa, dan Allah kice ina gaishe shi da kyau da kyau, da wuri zan faso goben nan ba zan tafi ba sai na ganshi. "



" Kyaji dashi dai, kije ki kwanta ki huta kinga ba ke kadai bace. "



" Tom, sai da safe.*



"Yawwa, sai da safe."



Tasan da wuri duk zasu zo, shiyasa ma ta katse Raudan sun hadu gobe ayi duk maganar ma da za'a yi, Hidaya ta kira nan ma sukayi magana sannan ta kira Ya Hadiza, ita ce ma suka dan dade suna magana, har ta soma mata maganar gyaran jiki da duk abubuwan da ya kamata, ita dai jin ta kawai take bata ce komai ba, daga karshe sukayi sallama tace sai tazo goben.





RM
   32

***Kansa ya daga bayan motar ta paka a harabar gidan nasu, akwai alamun hadari a garin yadda iska me dadi take kadawa, taune bakin sa yayi yana zura kafafunsa wajen, sai a lokacin yaga motar Aunty Fati daga gefen sa, fitowa yayi yana nazarin harabar gidan, kansa tsaya ya wuce cikin gidan ya haura corridor ya tura kofar, ji yayi an watsa masa abu a jikinsa,

"Congratulations 🎉."

Suka hada baki wajen fad'a, daya bayan daya ya dinga bin su da kallo, su hudu ne cif sai MD dake bayan su yana dariya, Aunty Fati ce ta fara mika masa flower sai Aunty Asiya ta bi bayanta, ta mika masa tana masa dariya, Amira da Ihsan ne a karshe

"Congratulations Yah."

Suka fad'a a tare, murmushi ya dinga sakar musu daya bayan daya, daga nan suka dunguma zuwa cikin falon in da Mom da Ammi ke zaune a kujera daya, wajen su ya karasa cike da matsananciyar kunya, ya duka yana gaida su, kowannen su farin ciki ne kwance a fuskarsa, cikin yanayin da ke nuna tsantsar farin cikin su.

"Ango kasha kamshi, baku ji wani kamshi ba wai da ya shigo?" Aunty Fati tace tana zama a hannun kujera kusa da Mom

"Irin dai kamshin ango." Asiya tace suka saka dariya,

"Sai muka ji daurin aure, saukinta ma akwai enough time na shirya komai, biki zamuyi irin wanda baa taba irin sa ba."

"Ai sati zamuyi Muna biki Aunty Asy."

Wani kallo ya watsa ma Ihsan din irin na waya saka dake, ta gimtse bakin ta, tana shiga taitayinta, dama ta zata yau daya dai zai bar su su dan sakata su wataya amma sai gashi yana ankare da ita tayi magana. Ganin haka ya saka Amira tsuke bakinta itama ta bar aunty Asy da Aunty Fati suke mishi maganar tunda sune daidai shi, duk abin nan yaki magana sai murmushi kawai yake idan sukayi magana, sun san dama ba yi zai ba, dan ma MD ya kwashe komai ya fesa musu da irin yadda yake narkewa a gaban Asma'un kamar bashi ba, dan har sun fara tausaya mata saboda miskilancin sa, ashe ashe ita ba haka yake mata ba.
   Lallabawa yayi ya gudu ya barsu suna ta fama, ya rage kayan jikinsa ya zauna yana jawo wayar sa, yayi broadcast message ga dukkan mutanen da yake ganin sun chanchanta su san da maganar auren nasa ya tura musu, sannan ya kashe layin dan yasan zasu kikkirashi. Baya jin rage ayyukan sa a yau, wata irin kasala yake ji da son kasance tare da ita, ko da ya dauko system din sai ya gagara komai, ya rufe ta ya ture gefe yana mike kafarsa ya jingina da jikin kujerar, sha daya da rabi saura yan mintuna ya duba agogon dake jikin allon wayar sa, Private layin sa da ba kowa ya san shi dashi ba sai family members yayi amfani wajen kiranta dashi, tana kwance rigingine tana duba sakonnin whatspp din ta wanda yawanci group din sai na Adam da yake mata kusan kullum sai uku ko biyar bata ma budewa sun taru sosai, shiga kansu tayi tayi marking ta goge su dukka sannan ta jefa lambar tasa a block list, ta koma wajen call log nan ma tayi blocking dinsa. Zata fita daga kai kiran ya shigo, ta duba time taga kusan sha daya har da kusan rabi, haka kawai sai jikinta ya bata shine dan babu me kiranta a wannan lokacin, dagawa tayi tana dan karata a kunnen nata kamar me tsoron abinda zata ji, muryar sa ta tsinkaya a cikin wayar yana mata sallama cikin tausasa lafazi,

"Baki bacci ba?"

"Umm?"

"Kina jiran na ko?"

Dunkulewa tayi waje daya daidai lokacin iska ta kad'a alamun tasowar hadarin gaba daya, wani sanyi ya shigo ciki ya iske ta, hade da wani irin mixed feeling akansa

"Tell me, me ya hanaki bacci?"

"Ba komai."

"Ba wani, tunani na kike ko?"

"Um Um." Tace ta k'asa bud'e bakin tayi magana

" Then tell me, me ya hanaki bacci."

"Kawai yaki zuwa ne?"

"Ni na sani, tunani na ya hanaki bacci,

"Kinga message dina?"

"Na gani."

Tashi yayi ganin yadda curtains din dakin ke dagawa ya daga yana kallon yadda hadarin ya hado sosai, hannun sa daya na rik'e da wayar dayan kuma ya zura shi wajen yayyafi kad'an kad'an na sauka akan hannun nasa, yana son yanayin damuna a rayuwar sa musamman ruwan dare, yana yawan kwatanta kansa da mai iyali a irin wannan weather din, sai da yaji ruwan ya soma karfi sosai sannan ya zare hannun sa, ya rufe glass din yana cigaba da wayar, har kusan sha biyu da rabi sannan yayi mata sallama shima ba dan yaso ba, sai dan ganin dare yayi. Alwala taje tayi, tazo tayi raka'a biyu kamar yadda ya umarce ta da zasu ajiye wayar, tana idarwa ta haye gado nan da nan bacci me dadin gaske, irin wanda ta dade bata yi irin sa ba ya dauke ta, bata tashi ba sai da Umma tazo ta tashe ta sallar asubah. Ita kanta umma ta lura da chanji a tattare da ita, da taje tashin ta, da yanayin da taga ta tashi. Kiran sa ne ya shigo wayar tana kokarin shiga toilet, ta dawo ta daga cike da zakuwa

"Kin tashi?"

"Eh."

" Na zata na sakaki makara, bari muyi sallah, bye."

Jallabiyar sa ya zura ya fito, ya kwankwasa ma MD kofa ya wuce yana jin motsin sa alamar ya tashi.





***Fido na zaune ita da Faiza Adam ya dawo, ya shigo ba tare da ya kalli in da suke ba, ya shige dakin sa ya rufo kofar, tashi tayi ta bishi, taje ta murda kofar amma sai taji ta a rufe, tsaki tayi ta hau bubbugawa tana kiran sunan shi

"Man ba zaka bud'e ba, wannan wane irin wulakanci ne?"

Yana jinta yayi banza kamar baya dakin, ta dinga bugu kamar zata zare amma ko gezau be ba, bare ya tashi daga ruf da cikin da yayi a saman hargitsattsen gadon sa da ya kwana biyu baa gyara shi ba. Kwafa tayi ta dawo wajen Faiza, ta saka mata ido tana kwashewa da dariya

"Saboda soyayya ta rufe miki ido, har kike ganin a kyale shi zai sakko ya kulali, ai wallahi in dai ba maganin sa kikayi ba a yadda yake hayakin nan tsaf zai dangara miki saki. "

"Yanzu ai na dawo hayyaci na, kije kawai ki same shi duk abinda ya kamata kiyi, ki biya ko nawa ne, sai ya gane ni ya wulakanta wallahi, aure kuma babu saki ko yaji zai gane kurensa. "

" Yanzu kike magana, da kin tsaya iyayi ai kallon ki kawai nake. "

" Shiga ki dauko wani abu sai na wuce yanzu ma, kinsan da zafi zafi ake dukan karfe. "

Tashi tayi ta shiga dakin ta, ta dauko mata kudi ta bata, ta tafi ita kuma ta koma kofar dakin nasa tana cigaba da bugu, bata ji takun tafiyar sa ba, sai kawai ji tayi ya banko kofar ya fizgo ta, ya zare belt ya shiga tafkar ta babu kakkautawa, sai da yayi mata shegen duka sannan ya watsar da ita a wajen ya haure ta ya fice daga gidan, be san in da zashi ba, kawai mota ya shiga ya dinga zagaye, sai chan dare sannan ya dawo gidan ya shige dakin sa, ido biyu sukayi tana zaune tana jiransa a dakin, yana shigowa tayi kukan kura da chakume shi, yadda tayi masa bazata ne ya bata sa'a a kansa, ta dinga kai masa duka da yakushi ko ta ina, kamar mahaukata haka suka koma a gidan, suka lalata abubuwa da yawa a dakin kafin ya rufo ta a ciki da key ya dawo falo ya kwanta. Kusan kwana tayi a tsaye tana dura masa zagi, yayi kamar be ji ba, tunda ya samu ya garkameta shikenan, ba zai iya da hayaniyar ta ba dan babu alamun zata gaji, shi kuwa yanzu ba ta ita yake ba, baya ma son ko ganin me kama da ita kuma yana jira ne da zarar ya samu kan Asma'u zai kada keyar ta, su dawo su ci zaman su da Asma'un cike da so da kaunar juna, duk abinda yake ita kawai yake gani ba zai kuma taba samun nutsuwa ba har sai ta dawo gareshi.
Da duku duku ya tashi ya fice daga gidan duk da ya daina jin motsin ta wanda yake kyautata zaton tayi baccin wahala dan ya jigata ta sosai bayan uban cizo da yakushin da ta yi masa, baya saka ran dawowa gidan nan kusa dan ba zai juri ganin ta tana

22 / 30