RAYUWAR MACE BY RANO

Author :  RANO Category :  African Stories & Novels

Chapter   11 / 30

30K to 33K   out of 87.6K words

ko zaka iya fad'a mana abinda ya faru har ka daga hannu ka dake ta."

" Duka? " Yace sai kuma ya kalli Umar ya dauke kansa da sauri

" Eh duka, mahaifiyar ta da dan uwanta sun tarar da kai kana dukan ta, shine muke son sanin dalilin hakan. "

" Ita ta tunzura ni, na dake ta ai, magana nayi mata ta tashi ta hada min breakfast tace ba zatayi ba, ta hau zazzagi na, shine ni kuma na sake ta."

" Zagi? Wanne irin zagi kenan? "

Kafin ya bud'e baki Mama tayi karaf tace

" Zagi dai kowanne iri ai sunan sa zagi, ni kaina na san abinda ku baku sani ba, akan faduwar da tayi wanchan karon, duk a dalilin yana bin ta akan hakkin sa ne ya saka ta wannan faduwar saboda ta tsani ta hada inuwa waje daya dashi. "

Maido da hankalin sa yayi kan Mama, yayi murmushi yace

" Asabe ban tambaye ki ba, amma naga alamar kamar kin fi Adam sanin matsalar gidan sa, sai ki sanar damu abubuwan da kika sani. "

" Ga Asma'un nan a tambaye ta ai, idan ba hakan ne ya faru ba, dan har Umman tasu nayi wa maganar amma ta nuna ko in kula akai, kuma da kaina na tambayi Asma'un ko Adam din ne ya sakata faduwa amma tace min a ah, duk wannan abun Adam yayi hakuri ya zauna a haka da ita, amma shine har Umar yana da damar da zai shiga har gidan sa ya dake shi, saboda ya taba yar gwal. "

" Ko akwai hukuncin duka a musulunci? Irin wanda Adam din yayi wa Asma'u?"

Juya zancen tayi zuwa wani daban, Abba ya girgiza kai yana cike da mamakin Maman.

" Toh duk ba wannan ba Asabe, kinsan a sanadiyyar dukan da Adam yayi wa Asma'u har da barin ciki da tayi? "

" Ciki? "

Tace tana zaro ido, sai a lokacin ta kalli Asma'un, sai tsoro ya kamata ganin yadda fuskar Asma'un tayi, tana masifar son jikoki dan bata da su, musamman ta bangaren Adam din, amma shine har akayi cikin har ya zube bata san dashi ba, da ta san dashi ko kuda ba zata taba bari ya hau kan Asma'un ba, bare har wani abu ya sameta. Tayi nisa a tunanin ta, duk basuyi aune ba, sai tsinkayar muryar Adam din sukayi a tsakar kansu, muryar sa cike da izza da rashin mutunci yake furtawa

"Na saki Asma'u saki uku!"

Wani irin zillo Hajiyar tayi ta rafka salati tana kwala kiran sunan sa, tuni har ya suri takalmin sa yayi hanyar barin gidan, duk suka bishi da kallo Abba ransa fes, fuskar Umma tamkar gonar auduga, ita kuma Asma'u hawaye ne ya gangaro mata a saman kuncin ta, ba wai hawayen bakin ciki bane, hawaye ne kawai da ba zata iya tantance na menene ba, ta dai ji sun zubo mata kawai.

"Alhamdulillah." Abba yace daga zaune,

"Allah ya ga niyyata ta son karfafa zumuncin mu Yaya duk da sanin waye Adam da irin halin sa, amma na dauka cewa Adam da Umar duk nawa ne, kuma hannun ka baya rubewa ka yanke shi ka yar, ki gafarce ni idan nayi miki ba daidai ba, itama Asma'u tana da hakki akaina a matsayin ta na yata, na bi mata hakkin ta kar Allah ya kamani da hakkin ta ranar gobe kiyama. "

Wani abu ne ya daki Maman, ta kasa motsa ko da yan yatsun ta ne daga wajen, tana ji tana gani suka tashi dukkan su, sukayi wa tsohon sallama suka fice. Da k'yar ta mike ta fito sai ta tarar babu motar da suka zo, Adam tafiya yayi ya bar ta kenan, Nadeeya ta kira a waya bata daga ba tana wanka, sai ta shiga takawa a hankali zuwa titi, ta tsaida napep ta hau zuwa gida!

_ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!! ZAFAFA BIYAR!!_

_ASSALAMU ALAIKUN MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

_BARKAN MU DA SALLAH, ALLAH YA MAIMAITA MANA, AAMIN_

_KU MATSO KUSA, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE ZABUROWA DA ZAFIN SU KAMAR YADDA KUKE KAUNAR SU._

_WANNAN KARON MA SUNZO DA WANI SALO MAI NUTSUWA HADI DA ZAFAFAN DARUSSA NA RAYUWA KANA DA FADAKARWA AKAN RAYUWAR YAU.. BANGAREN KOGIN KAUNA KUWA BAA MAGANA. DOMIN WANNAN KARON SUN SAKE TAHOWA DA ZAFAFAN KAUNANNAKI MASU NARKE ZUCIYOYI._ WANDA ZASU ZO MUKU  IN SHA ALLAH

_KADA KU MANTA ZAFAFAN NAKU DE SUNE KAMAR HAKA_

_SAFIYYAH HUGUMA: TAZO DA NATA SALON MAI SUNA: *KUFAR WUTA*_🥰

_BILLYN ABDULL TA ZABURO DA WANI TAKEN MAI SUNA: *BAQAR INUWA.*_😍

_MAMUH GEE ITAMA WANNAN KARON TA SAKE TAHOWA DA: *NOORUL-ALB*_🥰

_HAFSAT RANO WANNAN KARON TAZO DA NATA RUBUTUN MAI SUNA: *RAYUWAR MACE*_❣️

_NANA HAFSATU (MSS XOXO) WANNAN SALON MA TAZO DA : *MASARAUTA*_😍

***_DUKA LITTAFAI BIYAR ZASU ZO MUKU NE AKAN FARASHIN YADDA SUKE KAMAR KODA YAUSHE_*

_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_

_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE  MU TA: _

*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya👇🏼

*_09032345899_*

*KATIN MTN*👇👇

09166221261

______________________

ZAFAFA BIYAR

VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)

VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.

TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.

*_TEAM ZAFAFABIYAR_*


*RM*

     16

***Suna isa gida suka tarar da Ya Hadiza tazo, yanayin da ta gansu ya sakata rage damuwar da ta tawo da ita, falon Abba suka wuce gaba daya, Asma'un ta kwanta su kuma duk suka zauna. Ajiyar zuciya Abba ya sauke bayan ya nutsu yace

"Toh dai kunga yadda Allah yake al'amarin sa, tun farko ba wai na aurawa Asma'u Adam bane dan bana son ta, babu iyayen da basa son yayansu kuma ba zan taba cutar da Asma'u ba, ina so ki saki jikinki, ki cire komai a ranki ki dauka hakan shine kaddarar ki, in sha Allah Allah zai kawo miki miji na gari ko dan hakurin da kikayi."

"Haka ne." Ya Hadiza tace tana kallon umma da taki saka baki

"Wai har yanzu fishin ne hajjaju?"

Abban yace wa umma yana son tabo ta

"Toh ga yayanki nan dai suna kallon ki, ku tayani bawa gimbiya hakuri Umar."

Dariya suka saka dukkan su har Asma'u, suka mike daya bayan daya suka fice Ya Hadiza ta tallafa mata zuwa dakin ta, tsohon dakin ta da ta tafi ta barshi ba tare da ta shirya ba.

  Suna fita umman ta mike itama tabi bayan su, Abba yayi murmushi kawai dan yasan halin kayarsa, fushi take dashi sosai amma yasan zata sakko ne. Fita suka sakeyi da Umar suka biya aka siyo wa Asma'un nama me yawan gaske, Abban yace ayi mata farfesu ta ci sosai sannan a sarrafa mata wani, Ya Hadiza ce tayi aikin kafin ta gama ma sai gasu Hidaya da Rauda kusan a tare, dukkan su da tsohon cikin su, tare suka zauna da ita har dare sannan suka tafi, suna tafiya bacci ya dauke ta dan dama ta gaji sosai ga ciwon kan da yaki barin ta.

***Sau biyu me napep na nanatawa Hajiya Mama an zo, kafin taji dan tayi nisa a kogin tunani, sauka tayi ta bashi kudin sa ta wuce zuwa cikin gidan, ta ja kafarta zuwa cikin falon da tunanin ganin Adam din a falon, baya nan babu kuma alamar ma ya shigo gidan, fasa zama tayi ta juya zuwa gidan nasa, ta kwankwasa kofar megadin sa ya bud'e, ya matsa da sauri ganin ta, ta wuce ciki ba tare da ta iya amsa gaisuwar sa ba. A kwance a falon ta tarar dashi yana waya sama-sama, cikin bacin rai yake maganar ta riski karshen in da yake cewa

"To hell with her."

Yaja tsaki ya kashe wayar, sai a sannan yaga Maman, ya kawar da kansa gefe a dole yayi fushi, bata zauna ba, daga tsayen ta kira sunan sa sai dai yadda sautin muryar ta, ya fita ya saka shi tashi dan ya ji fushi sosai a muryar tata

"Adam!"

Da ido ya amsa mata, ta nuna shi da da dan yatsa tace

"Ni ka watsawa k'asa a ido, a bainar jama'a? "

" Mah wallahi ba zan iya cigaba da zama a wajen nan ba, dan rainin hankali kina ganin yadda tsohon nan yake min wasu banzayen tambayoyi kamar dan jarida, Asma'un gwal ce? Da za'a dinga raina min hankali haka. "
Sakar baki tayi tana jin sa, ya cigaba

" Idan ma banda dai kaddara ni me zan da ita, taimaka mata fa nayi, kwantai tayi a gida na taimaka mata, shikenan sai ace za'a daga min hankali akai, babu dole ai dan ni dama ba wai ina son ta bane. "

" Adam! "

" Yanzu Adam ni kake kallo kake faffadawa wadannan maganganun? Duk abinda nayi maka a rayuwa? Yanzu har ni zaka iya wulakantawa a gaban mutane kayi saki irin sakin da yake mafi muni sannan ka taho ka barni. "

" Raina ne ya baci, su je su jika yar tasu su sha, idan ta rube musu a gida su suka jiyo, mtsw! "

Dauke shi tayi da mari, mari me karfin gaske, rik'e wajen yayi cikn tsananin mamaki, Mama ce yau ta mare shi, abinda bai taba faruwa ba a kaf rayuwar sa, akan wata banza, akan wadda be taba dauka a cikin jerin mutanen da suke da muhimmanci ba.

"Bansan baka da mutunci ba wallahi sai yau, nayi dana sanin barin ka da nayi haka sakaka, dama duk abinda ka fada min akan Asma'u karya kayi mata, ka saka na musgunawa yar mutane saboda farin cikin ka, karshe ka dake ta, dukan da yayi sanadiyyar zubewar gudan jininka, amma ko gezau baka ji ba!? Baka ji komai ba?"

"Ni tun chan dama bana bukatar haihuwa, it's too early ni ban shirya hayaniya ba, yara stress ne kawai, da damuwa su ishi mutum. "

Saura kiris ta fadi daga tsaiwar da tayi, ta rik'e gefen kujerar da take kusa da ita, bakin ta ya kasa sake furta komai saboda kaduwa, haka tayi sakaci? Haka tayi sakaci da rayuwar Adam har ta lalace haka? Ashe shima namiji kamar mace kana bukatar jajircewa wajen tarbiyyar sa, kamar yadda zaka kula da mace a tsare mata mutuncin ta haka da namiji ma ya kamata kayi masa? A tunanin ta babu wani abu da yake tsakanin iyaye da yaran su maza, musamman iyaye mata basa iya tsawatarwa yayan su maza da zarar sun kai wani lokaci, sai a sake su da tunanin duk abinda namiji yayi ado ne, hakan shine silar gurbacewar al'umar mu, domin namijin shi ne zai dawo ya fara bata rayuwar yara matan da aka tsare aka kare!
   
   Zagaye kujerar da take kai yayi ya fice daga gidan yana kunkuni, zuciyar ta, ta dinga bugawa da sauri, jinin ta nan da nan ya hau saboda bacin rai, ji tayi ba zata iya tashi ba, sai kawai ta zauna a wajen tana kokarin ganin ta samu daidaituwar zuciyar ta.
  

Wayar ta dake cikin jakar hannun ta, da ta dire a falon ta wuto gidan Adam din Nadeeya ta kira, sai taji ringing din a falo, ta taso tazo ta duba sai taga jakar, a tunanin ta Maman na daki ko ta shiga toilet, amma kuma shiru har lokacin yaja sosai bata fito ba, zuwa tayi ta kwankwasa jin shiru shiru ya sakata turawa ta gani,babu kowa a ciki, nan da nan sai hankalin ta, ya tashi ta shiga duba Maman lungu da sako a cikin gidan, ganin dai da gaske maman bata nan, duk kuma masu aikin babu wanda yaga shigowarta, kiran Adam ta yi, har ta karaci ringing dinta be daga ba, tana kokarin kiran Asma'u taji ko har lokacin basu gama bane, sai ga Maman ta shigo a cikin yanayin da ya tsorata su, duk sun yi cirko cirko tazo ta wuce ciki Nadeeya tabi bayan ta da sauri tana tambayar abinda ya faru.

"Nadeeya na cuci kaina, na cuci Karami na kuma cuci Asma'u da zumunci, ashe Adam shine bashi da gaskiya, kinga dukan da yayi wa yarinyar nan, ya kuma zubar da cikin da yake jikinta, cikin da na kwallafa rai nake dakon zuwan sa, ashe wai har yana da bakin magana, hmm."

"Subhallahi, gaskiya boy be kyauta ba, be yi adalci ba sam, daman ni nayi tunanin haka, saboda kusan abinda ya faru kenan lokacin da tayi rashin lafiyar nan, ban sanar dake bane amma Adam sai da ya kusan yi mata illa, dan kusan fyade yayi mata."

"Na shiga uku na, amma shine baki fad'a min ba? "

"Toh gani nayi ba wai abun fad'a bane, da kunya kuma tunda hakan sirrin su ne, babu ma kyau fadar, amma nayi masa fad'a sosai wallahi, yayi min alkawarin ya daina kuskure ne ma, shi yasa na kyale maganar ma."

Dafe kanta tayi da hannu bibiyu,

" Adam yayi asarar mace, yayi asarar mace daya tamkar da dubu, ya cuci kansa kuma sai yayi dana sani."

" Ya rabu da ita ne? "

" Saki uku yayi mata, sakin wulakanci,. "

" Ya Salam, ya Salam! "

***Wuni Maman tayi a daki, dan sai da Nadeeya ta dubata tayi mata bp dan jinin ta ya hau sosai, shi kuwa gogan ko sake waiwayo gidan be ba, a dole fushi yake da Maman akan ta mare shi, gidan Fido yayi tafiyar sa ya kwanta yayi bacci, yana farkawa ya ganta a zaune a gefen sa cikin yanayin damuwa.

" Lafiya?"

Yace dan har ga Allah ya bashi tsoro da farko. Takardar hannun ta, ta mika masa tana tabe bakin ta,

"Duba ka gani."

Karba yayi ya hau dubawa, be gane komai ba , ya mika mata cikin son jin ta mecece yace

"Ban gane komai ba, takardar menene?"

"Takardar ciki ce, I'm pregnant with your baby."

Wani yimm yaji akansa, ya daga ido yana kallon ta, kallon karki rainawa kanki hankali mana, itama kallon nasa take a dake, dan ta riga ta shirya komai ba zata taba jin tsoron hargagin sa ba.

"Ciki kuma, kamar ya?"

"Ciki dai ciki dai."

Mikewa yayi ya zabure

"You must be kidding, ciki ana zaune kalau, ta yaya kika samu ciki?"

"Ka fini sani ai."

"Kin ga... Bana son wasa please"

"Allah ba wasa bane, ciki ne dani kuma cikin ka!"

Chakumar wuyan rigarta yayi

"Ni zaki raina wa hankali? Wallahi karya kike kije tun wuri ki nemo ubansa, tun dare be miki ba. "

"Akwai ubansa da ya wuce kai ne, saki ne malam! 

Tayi masa nuni da hannu, kin sakin ta yayi, ta fincike tana mikewa

"Ko kaki ko kaso wallahi kaine uban cikin nan, idan ma baka yarda ba toh, kanka, zan je in da za'a saka ka karba ta karfin gaske."

Kiranta ya dinga yi amma tayi masa banza tayi ficewar ta ta bar gidan ma, tsaki yaja ya mike shima ya fito, sai ya koya mata hankali sannan zata gane shi ba sa'anta bane, kuma ciki ba zai karba ba, dan be shirya daukar dawainiyar kowanne yaro ba bare ya takura masa ya hanashi more rayuwar sa, da zarar ka haihu shikenan sai duk tsufa ya kamaka, ina ba zai iya ba, idan ma tun wuri zata nemi uban yaronta ta nema ba sai dare yayi mata ba.
Mota ya shiga a fusace ya tada kura, ko gefen sa baya dubawa gudu kawai yake yi a cikin layin, duk wajen da yazo sai an kalle shi an kara kalla, masu Allah wadai nayi masu matsawa da sauri nayi dan har wani tsoho ya kusan zubarwa akan keken sa, kwana yazo zai sha wanda yayi daidai da fitowar su, suma zasu sha kwanar, yadda ya shigo da mugun guda babu horn ba komai ya sakasu kusan hadewa Allah ya takaita amma dai sai da suka taba juna.
Fitowa yayi a fusace, a dole an masa laifi yayi wajen motar yana zage zage, a dole an masa laifi, babu wanda ya motsa a cikin su, suna zaune daga motar suna kallon sa har ya karaso ya daki glass din gefen driver din, tint ne a motar shiyasa be iya ganin na ciki ba, hakan ya taimaka wajen sake kular dashi sosai, zuge glass din akayi, yayi masa kallon raini yace


"Malam haka ake tuki a garinku?"

"Ban sani ba." Adam yace a fusace

"Idan ka iya koyawa ai sai kazo ka koya min yadda ake yi din."

"MD let him be please, kasan bana son hayaniya, menene damage din da akayi masa, ya fad'a sai a biya shi."


A dage Adam ya kalli na gefen da yayi magana, ya watsa masa banzan kallo

"Kai waye da har zaka iya biyana,ko an gaya maka ni matsiyaci ne."

Wanda aka kira da MD ne yace


"Kai fa na lura kamar baka da aikin yi, mu bamu da lokacin batawa, idan zaka fadi abinda za'a baka ka fada, idan baka fad'a mu wuce."

"MD... " Ya kira shi yana saka masa ido

" Abuya, please ka bari mu kyale guy din nan, kasan sauri muke, yaci kansa kawai."

Daga haka ya daga glass din sama, ya take motar suka bar Adam a wajen tsaye yana zage zage, da kyar ya tattara ya koma wajen motar sa cike da haushin na gefen dan shi yafi bata masa rai dan yadda yake magana kawai ya lura dashi, hakan ya sake kular dashi, ya rike number din motar watarana zasu gauraya ko ba yau ba,sai ya nuna musu shi din gogaggen dan duniya ne na ajin farko!


Gida ya wuce kai tsaye, tun be karasa kofar gidan ba, ya hangi motar Fido a fake a kofar gidan su, wani irin wrong parking yayi ya fito da sauri, ya fad'a cikin gidan nasu jikin sa har rawa yake yi!



*RM*

        *17*

***A durkushe ya samu Fido din a tsakiyar falon su tana kuka wiwi, daga gani bayani ta gama yi, wajen da Hajiya take zaune ya kalla sai yaga tana hawaye. Kan Fido din yayi gadangadan, ta mike da sauri tayi tsalle zuwa bakin Nadeeya da take tsaye cike da mamakin Adam din.


"Karka kuskura ka taba ta."

"Me tazo tace muku, wacce karyar tazo ta sanar daku?"

"Ka santa kenan ashe." Hajiya Maman cike da takaici, sai a sannan ya tuna tabargazar da yayi, da ya sani ya nuna be gane ta ba, a kada a raya yace shi sam be gane ta ba.

" Kina ina fiddausi."

" Gani Mama." Tace kamar ta kirki

" Kiyi hakuri dan Allah dan darajar annabi ki bar maganar nan, idan ta fito ba Adam ba, ni kaina na shiga

11 / 30