Author : Boss Bature Category : Complete Novels
tace me kike yi ma dariya Aneeleh tace”Ai dole inyi dariya, ke yanzu baki gane muryata ba ne? Aneelerh fa ce matar abokin mijin ki Shu’aibu”
Da buɗar bakin budurwar sai cewa tayi”ƙarya kike yi aini mijina basu nan shi shu’aib ba, TAJ ne sunan shi, Kina son ki yi mini wayau ne”
Jin ta ambaci sunan Taj Yasa Aneelerh Tsayawa cak ta dakata da yin tafiya, yayin da bugun zuciyarta ya ƙaru, Muryarta na ɗan rawa ta furta”ƙarya kike yi, ba sunan mijin ki tajuddeen ba, so kike in yadda don kada ki faɗa min ainihin sunanshi, ai ni nasani Shu’aibu ne sunan shi”
Matashiyar budurwar tace”To kada Allah yasa ki yadda ma, kuma wlh ma ƙarya kike yi mini cewa wai ke matar abokinsa ne baki da gaskiya,” da alama ranta ya 6aci ta fara harzuƙa.
Sassauta murya Aneelerh tayi”Ki yi haƙuri, ba yadda ki ke tsammani bane, Dan Allah ki faɗamin ina mijin naki yake inason yin magana dashi”
Dogon tsoki matashiyar Taja, kafin ta furta”ba kin ce ke matar abokinsa bane? To ki ce ma shu’aibun Ya kawo ki gidan mu,” kafin Aneelerh ta furta wani abu, Matashiyar ta katse kiran!”
Hankalin ta Yaƙi kwanciya, Jiri ta soma gani acikin idanuwanta, a daddafe ta nufi gado, Ta haye ta kwanta, Yayin da idanuwanta ke fuskantar ceilling, zuciyarta ta shiga ruɗani, tun da Matashiyar ta ambaci sunan tajuddeen, natsuwarta tabar jikinta, taso ace tayi waya da shi don ta tabbatar da abun da take hasashe.
Har ƙara jaraba kiran layin tayi amma matar taƙi ɗagawa.
Dubara ce ta faɗo mata aranta, da sauri ta rubuta mashi saƙo cikin harshen turanci.
_Idan ka karanta saƙona, dan Allah ka kira ni, Inason Yin magana da kai, saƙo daga Aneelerh muhammad falgore_
Ajiyar zuciya ta sauke Bayan ta kammala rubuta mashi sakon, Ta ɗaura wayar saman side drawer, A gogon ɗakin ta kalla ƙarfe Uku na rana, kwanciya tayi saman gadon tana jiran tsammanin Kiran me wayar.
❤ZEENATU❤
A 6angaren zeenatu kuwa tun da ta fito da gudu daga ɗakin Dr. Shureim ta koma ɗakinta, ta fada saman gado taci gaba dayin kuka tamkar ranta zai fita, cikin muryar kuka take fadin”yaya shureim ba sona yake yi ba, wata yake so daban, dama nasani babu namijin da zai yarda yaso ni saboda rashin natsuwata,”
Idanuwanta sun kaɗa jawur, miƙewa tayi zaune ta soma cire lace jikinta a saman floor, ta watsar da kayan hada ribbon din da aka daure mata gashin kanta, iya undy ta bari a jikinta, ta jashi saman ƙirjinta, tana huci yayin hawaye ke cigaba da wanke mata fuskarta, saukowa tayi daga saman gadon ta nufi gaban dressing mirror dinta, cikin 6acin rai ta sanya hannu ta watsar da jerin turarurrukanta komai sai da ta wurgo shi ƙasa, bayan ta gama ta koma gaban wardrobe dinta, ɗaya bayan ɗaya sai da ta wurga da suturar saman floor, hankalinta bai kwanta ba har saida ta maida ɗakin kamar na mahaukata, tukunna ta koma saman gadon ta haye tare da jan bargo ta lullu6e zuciyarta na ta farfasa.
Bayan Dr. Shureim ya fito daga wankan, kimtsa kanshi yai ciki shiga ta larabawa Ya feshe jikinsa da turare,
Ya ruƙo wayar shi a hannun shi, tare da car key dinsa, walking quickly ya fito daga bedroom dinsa, Ya nufi ɗakin zeenatu, duk inda Ya gifta a paloun masu aiki ne suke Yin aikace aikacen su cikin girmamawa suke gaishe da shi.
“Yalla6ai barka da fitowa” muryar Tani ce ta katse mashi hanzarinsa, dakatawa yai da yin tafiyar ya juya ya dubeta
“Yawwa barkanki, Ya aiki” fuskarta da fara’a ta amsa mashi”Lafiyalou Alhamdulillah,”
Har zai wuce ta Ya kuma tsayawa ya kalle ta”Ɗakin zeenatu nake nema” Da rawar Jiki ta ce”Yana a second floor, muje in nuna maka ɗakin” ta faɗa tare da yin gaba Yabi bayanta, Yayi matuƙar ƙagara da son ganinta, duk don Ya lallasheta akan laifin da yayi mata.
Bayan sun hau elevator ta sauke su a second floor, Tani ta nuna mashi ƙofar ɗakinta.
“ki shiga ki faɗa mata inason magana da ita”
Tani ta amsa da toh, tana zura ƙafarta ɗakin zeenatu, gabanta Ya faɗi ganin irin 6arnar da tayi, hankalin ta ba ƙaramin tashi yai ba, jiki na rawa ta nufi gefen gadonta.
“Zeenatu! Lafiya meke damunki ne? Meyasa kika hargitsa suturar ki”?
Shiru zeenatu bata tanka mata ba, saima ƙara ƙudundune kanta da take yi cikin bargo.
“Dan Allah zeenatu kiyi mini magana, nasan 6ata maki rai akayi ki fada mini wanene”
Jin tayi shiru ba ta yi mata magana ba yasa tace”ba zan takura maki ba, Yanzu ki tashi Yayan ki shureim Yana a ƙofar ɗakin ki, shine yace in yi maki magana yana son ganinki”
Kamar jira ta ke yi Tani ta ambaci sunan shureim, Cikin shessheƙar kuka tace”Tani, I don’t want to see him. Please tell him I won’t come. Yaya Shureim doesn’t love me wata yake so daban, tun jiya yayi min alƙawarin zamu fita yawo atare, yau kuma da kanshi yace min inje in shirya kafin in dawo zai yi wanka ya shirya, Tani da naje ɗakin shi babu abunda yayi, yana akwance saman gado yana kallon hoton girl friend dinsa a laptop....” daƙyar ta ƙare maganar.
Jikin Tani yai sanyi, duk sai taji ba daɗi, sai yanzu ta gane dalilin dayasa ta shiga halin da take aciki.
“Kiyi haƙuri zeenatu, ki tashi ki gyara jikinki, Yace yana son magana dake nasan yazo ne don ya baki haƙuri, kuma naga ya shirya hada key din mota a hannunshi....” Katse ta Zeenatu tayi”Na fasa zuwa ki faɗa mishi bazan je ba, tun da bayaso na”
Cikin muryar raɗa Tani tace”yana fa jin ki, bai kamata kina ɗaga murya ba, sannan ke in banda abunki waya fada maki budurwashi ce yake kallo awayar?
“Ai naga hoton da yake kallo, Yana a kwance saman gado ya rungumeta a kirjinsa” ta fada tana jan numfashi taƙi fitowa daga bargon.
“Zeenatu, kiyi mashi kyakkyawan zato, yaya shureim yana sonki fiye da yadda kike son shi, Ni shawarar da zan baki shine kada ki bari ya gane kina son shi, idan kika kwantar da hankalin ki da kan shi zai furta maki kalmar so”
Sassauta muryarta tayi”Tani, zan iya jure wannan amma bazan Iya jure kallon hoton budurwarshi da Yake Yi ba,”
Dafe kai Tani tayi da hannu ɗaya”zeenatu baki da tabbacin budurwashi ce, pls kibi komai a sannu zamu gano ainihin wacece Yake kallo awayarshi, Yanzu Ki tashi muje Yana awaje yana jiranki’
“Tani ki daina wahalar da kanki, Nifa ba inda zanje, Ki fada mashi bana Jin daɗi bacci Nike Yi”
Duk yadda Tani taso ta lallashe ta akan ta tashi ta je gare shi taƙiya, a dole ta ƙyaleta ta juya ta fuce daga ɗakin.
A tsaye ta same shi Ya jingina bayanshi jikin bango.
Harya fara Gajiya da tsayuwa
“Ka yi haƙuri, Zeenatu tayi fushi bansan meya haɗa ta dakai ba, nayi ƙoƙarin In lallasheta amma taƙi amincewa ta amsa kiran ka, ban ji daɗi ba shureim, duk da bansan meya haɗa ka da ita ba, amma bai kamata tun yanzu afara samun rashin jituwa a tsakaninka da ƙanwarka, zeenatu tana da haƙuri sai dai tana da zuciya idan aka 6ata mata rai’
Tun da ta fara magana Ya natsu yana sauraronta, sai da ta kai karshen maganar tukunna yace”Inaso zan shiga ciki”
bai jira amsar da Tani zata bashi ba yai saurin haura ƙafarshi cikin ɗakin zeenatu.
Dafe kai tayi da hannu ɗaya tunawa da 6arnar da zeenatu tayi a ɗakin, gashi kuma Ya shiga hake zai je ya same shi kamar bola, can kuma ta ayyana aranta cewa ɗan uwanta ne, daga haka ta ƙara gaba.
A tsanake Yake bin ko’ina na ɗakin da kallo, yayi mamakin ganin yadda ta hargitse komai, ta rikita mashi tunanin shi, Ya rasa gane fushin menene take yi da shi? Don shi a tunanin duk akan fitar da yace za su yi ne.
Sam bai lura da lace din data cire ta jefar saman floor, idanuwanshi na akan gadonta, bargon da ta lullu6e dashi sai kerma yake kamar wadda sanyi ya kama.
daddaɗan ƙamshin turarensa ne Ya daki hancinta, Nan take ta fahimci Ya shigo ɗakin nata.
Gefen gadonta ya zauna Yana dubanta, calmly ya furta”Zeenat ina son yin magana dake
Shiru tayi bata tanka mashi ba, tayi tunanin Tani ta fada mashi cewa bacci take yi kamar yadda tace ta gaya mashi.
“Nasan Kina Jina zeenatu, Ki amsa mini, nazo ne don in baki haƙuri, nasan ban kyauta maki ba, Yanzu haka da nike yi maki magana na kammala shiryawa ke nake jira mu tafi”
Cikin disasshiyar murya tace”yaya shureim bana jin daɗin jikina, bazan iya fita ba, sai dai zuwa gobe”
“am sorry zeenatu, fushi kike yi da yayan naki? Ba za ki yi mini uziri ba?
“Yaya shureim ni ba fushi nike yi dakai ba, fitarce na fasa, Bana jin daɗi”
Ya rasa ya zai yi ya shawo kanta don ta amince su fita.
Yanke shawarar Yaye Bargon Jikinta yai don ya samu damar lallashinta dakyau.
Tsautsayine Yakai hannun shi saman bargonta, Ya ruƙo shi tare da jan shi, Ras yaji gabanshi ya faɗi da sauri Ya maida mata bargon a jikinta, Yana faman jan numfashi da ƙarfi da ƙarfi, miƙewa yai da wani irin Yanayi ya nufi ƙofar fita daga ɗakin Yayin da la66ansa ke ambaton sunan Allah, Har ya kusa kaiwa ƙofar ɗakin Muryar zeenatu ta katse mashi hanzarin shi.
“Yaya shureim kai da kanka ka faɗa mini cewa baka ta6a yin soyayya ba, amma meyasa kake kallon hoton wata awayarka”
Ta gaza haƙura har saida ta amayar masa da abunda ke cikinta, shi kuwa Man din duk ya rasa natsuwarshi, tunda Yaja bargonta Yayi arba da undy din jikinta shara shara Hakan ba ƙaramin tada mashi hankalin shi yai ba, ga dukkan alamu ita batasan ma ya buɗe bargon ba saboda ta ƙudundune kanta, idanuwanta suna arufe.
“Zeenatu, abun da na faɗa maki da gaske ne, banyi maki ƙarya ba, Ni ban ta6a yin soyayya ba” A hankali Ya ɗan Juyo yana dubanta, a lokacin ta fiddo da kanta daga Cikin bargon, Yalwatacciyar sumar kanta, ta rufe mata gefen fuskarta, Jan bakin data shafa ya dame fuskar saboda kukan da tasha, har saman kumatunta jan bakin ne, duk da kwalliyar fuskarta ta 6aci ba ƙaramin kyau tayi mashi ba.
Muryarta da shagwa6a tace”ka faɗamin wacece ka ke kallo awayarka? Idan ba budurwar ka bace.
Ƙayataccen murmushine Ya bayyana akan fuskarshi, sai yanzu ya gane dalilin dayasa take haukan nan, wato kishin shi take Yi saboda yana kallon hoton wata wayarshi, aranshi ya ayyana da ace tasan hoton wacece yake kallo da batayi haukan nan ba.
“Zeenatu, dama saboda hoton wayata kike kuka”? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh.
“Okey, Ki kwantar da hankalin ki, ba budurwata ba ce,” maƙe mashi kafaɗa tayi”ni ban yadda ba yaya shureim, idan har dagaske kake yi min ba budurwan ka bace to ka nuna min hoton in gani”
Lumshe idonshi ya ɗanyi tare da waresu kan fuskarka, duk da tazarar dake a tsakanin su, ba ƙaramin Kyau take yi mashi ba musamman yanzu daya fahimci irin zazzafan son da take yi mashi.
Ganin ya tsareta da ido, ba tare daya furta komai ba yasa tace”Yaya shureim magana fa nake yi maka, kayi shiru baka ce komai ba, Ni dama nasani baza ka nuna min hoton in gani ba”
Yadda take yin maganar tana jujjuya eyes balls dinta ne suka ƙara rikitar da shi.
Gyaran murya ya ɗanyi kafin yace”Idan har Ki ka amince zaki shirya mu fita, Ni kuma zan nuna maki wacece nake kallo awayata,” zum6ura mashi baki tayi”toh, amma ka fara yi min alƙawari,”
“Nayi maki alƙawari”
“Yanzu zan shirya yaya shureim,” ganin tana ƙoƙarin miƙewa tsaye yai saurin fuce wa daga ɗakin gudun kada Ya ƙara ganin abunda zai hana shi Runtsawa.
Fitowa ya yi daga cikin gidan Ya nufi harabar ajiye motocin su, Wasu danƙara danƙaran motoci ne na Alhaji musa a killace a ƙalla sun haura goma shabiyar, kuma dukansu babu motar ƙasa da miliyan talatin, Manya manyan motocine tsadaddun gaske masu numfashi.
Motarshi Ya buɗe Ya shige Ciki Ya zauna a driver seat haɗi da ɗaura kanshi jikin headrest, bakomai Yake tunawa ba face maganar da Alhaji musa ya faɗa mashi akan Aiki da kuma aure, A yanzu ya fara tunanin ta yadda zai 6ullo mashi da zancen auran zeenatu, yafi buƙatar auren akan komai, saboda yanason ya samu natsuwar cigaba da gudanar da rayuwarshi, zeenatu ta kwanta mashi aranshi ɗari bisa ɗari, kuma yana da tabbacin zeenatu zata maye mashi gurbin abunda ya rasa.
Almost 15 mins, ƙamshin turarenta Ya doki hancinsa, Nan take ya fahimci ƙarasowarta, buɗe motar Tayi tare da samun wuri ta zauna gefenshi” ɗaura idonshi yayi akan face dinta, babu make up, zallar kyan da Allah yayi matane, ta canza kayan jikinta zuwa turkish gown launin black gray, Ta yafa mayafi akanta, Idanuwanta sun kumbura saboda kukan da tasha.
Kallon Juna suka somayi kamar zasu haɗiye kawu nan su, Ko ƙyaftawa basa yi, kunyar shi ce ta kama ta, da sauri ta daura kanta saman laps dinta.
“Zamu Iya tafiya” da shagwa6a tace”a’a yaya shureim, nafi so ka fara nuna mini hoton in gani”
Zaro wayarshi yai daga cikin aljahu Ya daddanata, Kafin Ya miƙe mata wayar”kar6i ki ganta, Kyakkyawa ce tafi ki kyau, ita nike da burin aure”
Gabanta na faɗuwa ta ɗago, tare da sanya yatsun hannunta dake kerma ta kar6i wayar da ya miƙo mata, idanuwanta rufe tabarsu, Gudun kada taga abun da zai hanata kwanciyar hankali.
Dr. Shureim dake kallonta, murmushine ɗauke akan fuskarshi
“Meyasa ki ka rufe idonki”? Muryarta na rawa ta furta”bana son inga abunda zai hanani bacci”
“In sha Allah ba zai hanaki yin bacci ba, sai daima ya sanyaki yin bacci cikin kwanciyar hankali, now Open your eyes slowly and look at the picture,”
She took a deep breath and tried to slowly open her eyes kamar yadda ya bata umarnin ta bude su a hankali.....”
(Kaɗan daga cikin na sati mai zuwa idan Allah yakaimu da rai da lafiya🤣 sai dai Allah yakaimu zamu gani, Very soon In sha Allah Zamu shiga Takun ƙarshe na labarin kurkukun ƙaddara)
*Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya, Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_
~Middle step~
سجن القدر❤🤍❤
_THE PRISONERS E24🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
Confusion of the heart💫
lokacin da ta ware idanuwanta akan screen din wayar wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta ganin fuskarta, hotonta ne tun tana ƴar shekara goma sha ɗaya a duniya, tsabar farin ciki Ya hanata rufe baki, hada hawayenta saboda farin cikin ganin hotonta ne yaya shureim yake kallo, bata kawo komai aranta ba saboda ta yarda da shi.
Ɗagowa tayi idonta acikin nashi ta furta”yaya shureim dama hotona kake kallo”? Ɗaga mata gira yai alamar eh, ta kuma cewa”yaya shureim wannan ai tsohon hotona ne a ina ka same shi”
Fuskarshi ɗauke da murmushi yace”nima tsohuwar ajiyace a cikin memory dina, saboda inason hoton bana so na rasa shi, bama shi kaɗai ba akwai sauran hotunanki a gallery ɗin wayar zaki Iya dubawa ki gani”
Yatsun hannunta na kerma ta bubbuɗe sauran hotunan tana kallonsu hada wanda tun tana jaririya akayi mata shi, abunda ya ɗaure mata kai gaba daya gallery na wayarsa hoton mutun biyune acikinsa daga hotonta saina ƙanwarshi benazir.
“Yaya shureim tun yaushe kake kallon hotuna na”? ta faɗa da mamaki akan fuskarta.
Muryarshi ƙasa ƙasa tamkar tame yin raɗa ya furta mata”tun lokacin dana fahimci kece ƙaddarata” wurga mashi blue eye balls dinta tayi akan face dinsa.
“Ƙaddararka? Kamar yaya kenan”? Cikin rashin fahimtar kalaman shi ta ambaci hakan.
“Lokaci zai ƙure mana zeenatu, ki bari idan muka dawo gida zan fahimtar dake abunda nake nufi” amsa mashi tayi da toh, haɗi da miƙa mashi wayarshi Ya sanya hannu ya kar6a, ya turata a aljhu, har cikin ranshi ba ƙaramin daɗi yaji ba, ganin bata kawo komai aranta ba, Duk da ya 6oye mata ainihin hoton da yake kallo.
“Allah sarki aunty benazir, nayi missing dinta Yaya shureim, tsawon lokaci babu ita, Allah dai yasa aganta da ranta da lafiyarta” cikin sanyin murya zeenatu ta yi maganar, ya amsa mata da ameen.
Yana ƙoƙarin tada motar, ba zato ba tsammani yaji zeenatu ta kwantar da kanta saman kafaɗarshi, wata irin kasalace ta soma baibaye shi sakamakon ƙamshin turarenta dake kashe mashi jiki.
A hankali motarsu ta miƙi Hanyar babban gate din gidan, Gate security officers ɗin dake tsaron gidan suna ganin motarshi gaba ɗaya suka yunƙuro suka nufo motarsu, hannunsu ruƙe da jibga jibgan bindigu, ba arziƙi dr. shureim Yaci burki, Jin ya dakata da yin driving din yasa zeenatu ɗago da kanta daga saman kafadarshi ta dube shi.
“Yaya shureim meyasa ka dakata da yin driving din”
“Masu tsaron gidan nan ne suke tunkaro mota ta,” ya bata amsa a takaice.
Dafe kai tayi da hannu ɗaya”Namanta