Wani Haske Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Hameedah Category :  Complete Novels

Chapter   8 / 35

21K to 24K   out of 102.7K words

budewa ya hangota tsaye tana kallonsu kafin yayi yunkurin sakin ummu har ta juya cikin sauri ta fice daga falon, tana tafe tana hawaye tamkar wacce aka aikowa da mutuwa, zahiri yau ta yarda jabir bai sonta ko kadan domin tunda tazo gidansa bai taba nuna yasan da ita ba amma yanzu jibi irin soyayyar da yake nunawa matarsa wacce yake so, kukane ya kwace mata ba tareda ta shirya ba lallai wannan shi ake kira da SON MASO WANI.

A bangaren malam jabir kuwa tun da yaga fitarta sai baiji dadiba domin yasan kowacece dole sai taji bacin rai musamman ma ita da bai taba gwada mata so ba, sai da ya samu nutsuwa sannan ya fara tunaninta, yasan dan so tana sonshi to amma shi rashin musuluncin da bata yine kawai ya hanashi nuna mata so.

Kwana tayi tana kuka ga damuwa da tayi mata yawa dan kowanne lokaci idan ta rufe idanuwanta shi kawai take gani yana romancing din Ummu, kuka tayi mai isarta sannan ta iya hakura amma akoda yaushe bakinsa da take muradi take ganowa cikin na ummu, bacci barawo ne yayi nasarar saceta da misalin karfe 5 nasafe amma 9 tana yi ta farka a furgece, wanka ta shiga tayi ta fito duk ranta babu dadi, zuciyarta ta cika da kunci, tana daure da towel tana shafa mai taji knocking tashi tayi taje ta bude, ganinsa tayi tsaye yana rikeda hannun al'amin, bata iya cemusu komai ba ta juya zata wuce dakinta,

"Good morning anty" ta jiyo muryar al'amin, juyowa tayi ta kakaro murmushin dole tace,

"Morning my dear son"

Kallo mal jabir yabita dashi daga gani tana cikin damuwa amma yayi damarar share mata hawayenta a daren yau duk da ba wai yana sonta bane kuma yasan bazai iya sakin jiki ba domin kyankyami gareshi,

"Anty nima kinga za muje unguwa nida abbuna"

"Adawo lafiya my son" tafada ta shige cikin dakinta, kallon kofar dakin jabir yayi to wannan me kenan? Ko itama fushin take yi dashi?

"Goodness" ya kira sunanta a hankali,

Fitowa tayi batare data amsa ba,

"Babu abinda kike bukata?"

"Babu" tafada atakaice tareda juyawa ta koma cikin dakinta,

Hannun al'amin yaja suka fita daga cikin falon suka nufi inda mal idi driver ke jiransu.

Goodness dai wuni tayi cikin bacin rai abunku da wanda baya salla, tana ganin 3 tayi ta dauki bible dinta ta tafi church,koda taje church dinma tana tare da damuwa gashi yau ma ba tajeba morning service taje, zama tayi jugum tayi tagumi bata farga ba hawaye suka fara bin kumatunta,

"Hello goodness what's happening?" Ta jiyo muryar promise tsohon saurayinta, cikin sauri tafara goge hawayen dake fuskarta gudun kada yagani amma kuma ya rigada ya gani, tsugunnawa yayi agabanta yana kallonta,

"Goodness what's wrong with you?" Yafada yana kallon fuskarta,bible dinta ta dafe ta kalleshi amma ta kasa magana to ma me zata ce masa shin zata fada masa cewar mijin data aura baya kulawa da ita ko kuma za tace masa mijinta baya sonta? Ganin bata da amsar bashi yasata yin shiru domin shi idan yaji wannan maganar ma dariya zai yi mata tunda ta kishi a baya gashi yanzu kuma tun ba aje ko inaba tafara korafi, hannunta taji promise ya kama ba tayi kokarin hanashi ba domin tana cikin damuwa dayawa,

"Goodness i know kina cikin damuwa because i saw your face symbolised this, but you know am your true lover i can't hold my hands watching you feeling unhappy, so yanzu ki taso muje wurin birthday party din Moses kinga after idan aka tashi sai ki tafi gida by that time i know you can get some relief"

Kallonsa tayi ta mike suka tafi duk ranta a jagule, wani dan madaidaicin club sukaje inda ananne za a gudanar da party din,

Kujeru suka samu suka zazzauna suka fara kallon yanda bikin partyn zai gudana, nan kuwa aka fara gudanarwa ita dai goodness bin kowa take da kallo amma ta dan ji sauki acikin zuciyarta, suna nan zaune anata chasu har gari yayi duhu, tashi promise yayi yace

"I dey come goodness, make i go and bring us some cool minerals"

"Ok but don't be long pls kaga ina son nakoma gida in the right time"

"Don't worry dear yanzu zan dawo" yafada tareda juyawa yana murmushin mugunta domin shi kadai yasan muguntar da ya shiryawa goodness wadda ita bata san da ita ba, wurin da ake bayar da drinks yaje aka zuba masa juice mai sanyi acikin cups guda biyu, ahankali ya zaro wata yar karamar roba daga cikin aljihunsa ya bude ya zuba abinda ke ciki acikin daya daga cikin juice din ya mayar robar ya rufe ya sata cikin aljihunsa.

Goodness na zaune tana jiransa sai dan waige waige take, nan ta hangoshi ya taho yana zuwa ya mika mata wanda ya tsiyaya wannan abun aciki, hannu tasa ta karba ta dan fara kurba ahankali ji tayi lemon yayi mata dadi domin har wani tsami tsami yake yi kamar anhada da lemon tsami amma kuma ta kasa tantance yanayin taste dinshi,

"Promise what's kind of sweet juice is this?" Ta tambayeshi tana lumshe ido,

"Kedai ki sha sai akaro miki" ya fada yana murmushin mugunta, shanye juice din tayi take tafara jin hajijiya tana daukarta gashi ta fara ganin mutanen wurin bibbiyu bibbiyu,

"Hey promise make you carry me and bring me back to my house" tafada cikin maye,

"Now now kuwa" yafada yana dariya, hannunta ya rike ya jata zuwa waje, da motar Moses yayi amfani ya sakata aciki ya ja ya fita daga club din yayinda ita kuma goodness ke cikin yanayi na maye domin sai shirme take yi irin na wanda ya bugu.





_*Ummi Shatu*_πŸ‘ŒπŸ»
[10/28, 9:29 PM] β€ͺ+234 810 100 9022‬: [9/1, 11:02 PM] Ummi A'ishaπŸ‘ŒπŸ»:


*WANI HASKE*


_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_


_42-44_





~~~Gidanta ya nufa da ita domin bashida niyyar yin raping dinta domin a tunaninsa ba budurwa bace yanzu tunda tayi aure, a kofar gate din gidan ya sauketa ta debi takalmanta ta rike a hannu ta dauki bible dinta da jakarta, ga dan kwali shima ta rike a hannu tana layi,

"Hey promise thank you, till we meet tomorrow in the church"

Tafiya tafara yi tana layi tana harhada hanya,

Wani mugun bugu take yiwa gate din gidan kamar zata karyashi wanda har sai da mal jabir ya fito daga sashensa ya tsaya a compound din gidan dan ganin waye me yin wannan bugun kofar,

Dagudu mai gadi ya zo ya bude mata domin dama bayan gida ya dan zagaya, ganinta cikin maye ya sashi bata hanya,

"Don't worry dear, am not angry... Don't worry baba" ta fada cikin magana irinta bugaggu,

Takalminta da jakarta da Bible dinta da dan kwalinta a hannunta ta makale wasu a hammatarta tana tafe tana hada hanya,

Cikin razani mal jabir ya bita yasha gabanta kallo daya yayi mata ya gane acikin maye take "innalillahi wa inna ilaihir raji'un" shine kawai abinda ya iya furtawa tareda cakumar wuyan rigarta yana karewa jikinta kallo,

Sanye take cikin riga t shirt mai dogon hannu da skirt ta jeans blue,

"Have you drunk alcohol? Am asking you, tell me the truth" yafada yana jijjigata,

Wata dariya ta saka ta kalleshi ta kai hannunta kan fuskarshi tana shafawa, fusgarta yayi ya figeta yayi sashenta da ita shidai mai gadi yana tsaye yana kallonsu,

Kankameshi tayi ta gefensa tana dariya "am lucky, you are good looking, i love you soo much" haka taketa furtawa har ya shigar da ita falonta bayan ya bude kofar,

Tureta daga jikinsa ya shiga yi yana kallonta,

"Goodness me kika sha? Ki fada min abinda kika sha, alcohol kika sha?" Yafada da karfi wanda shi kansa bai san lokacin da ya koyi magana da karfi irin haka ba,

Gemunsa taja "i love you my dear, you are such a nice....!"

Tsawa ya daka mata "shut up your mouth, you better tell me what...!"

"Shhhhh" tafada tareda dora yatsanta akan bakinta "keep silent"

Hannu tasa ta shafo kumatunsa zuwa lips dinsa "i like you i swear, am in love"

"Goodness bakida hankaline ne? Ki fada min abinda kikaje kika sha" yafada cikin fada

"Alcohol nasha..!" Bata karasa rufe bakinta ba ya dauketa da mari tareda hankada ta kan kujera ya juya ya fice domin no need ya tsaya yaci gaba da westing din time dinshi a banza akan shirmenta.

Yanda ya fita ya barta haka ta zauna har wani bacci mai nauyi ya dauketa.

Yana zuwa dakinsa ya dafe kansa tareda zama a gefen gadonsa, wannan wacce irin rayuwa ce ya samu kansa aciki? To ko dama yarinyar nan bata gari bace? Ya tambayi kansa, tashi yayi ya fara zagaye dakin shi bai san da wacce kalma zai fassara wannan abun ba, yarinyar nan zuwanta cikin gidansa duk ta zubar masa da kimarsa wacce jama'ar gari ke kallonsa da ita,

Yanzu in banda kaddara taya za ace ansha giya agidansa? Bayan duk halaccin da yayi mata ya kyaleta take zuwa church daga gidansa hakan bai wadatar ba har sai ta hada da shan giya? Ya zama dole ya rabu da yarinyar nan tun kafin ta shigar dashi cikin wani hali,tabbas a gobe zai sallameta ta tafi gidansu tun kafin mummunar halayyarta ta shafi iyalan gidansa, _bathroom_ ya shiga yayi alwala ya fito yazo kan dadduma ya fara sallolin nafila kamar yadda ya saba gudanarwa ako wanne dare.


Tunda goodness ta kwanta bacci bata tashi ba sai da gari ya waye tamgararu rana ta fito, zaune ta tashi ta kalli jikinta take abubuwan da suka faru jiya suka fara dawowa cikin kwakwalwarta tun zuwansu club da promise har dawowarta gida hatta marin da jabir yayi mata duk sai da ta tuno,

"I can't pardone you promise, you kid me, you have cheating me, you deceive me promise, i can't forgave you" wasu zafafan hawaye ne suka shiga sintiri akan kumatunta, sai da tasha kukanta ta koshi sannan ta tashi ta shiga cikin dakinta, wanka tayi bayan ta fito ta shirya cikin doguwar riga pink colour mai gajeren hannu rigar roba ce dan haka ta kamata sosai, kitchen ta shiga ta dora ruwan zafi.


Shi kuwa mal jabir da bacin ran abinnan ya kwana dan haka koda gari ya waye bayan ya shirya yayi breakfast daukar al'amin yayi suka tafi gidan mahaifinsa wato takwaran al'amin din,

Lokacin da suka je yana zaure yana zaune yana lazimi, da gudu al'amin yaje ya dale shi yana dariya, jiyowa shima yayi yana dariyar yana cewa "ja'iri dama nasan babu wanda zaiyi min wannan aiki sai kai, yanzu kuke tafe?"

Karasowa jabir yayi ya zauna agaban mahaifin nasa tareda gaisheshi cikin girmamawa, bayan sun gaisa ne yake sanar dashi cewar zai sallami goodness ta tafi gida saboda ga irin abubuwan da take yi masa,

"Haba jabiru ina hakurin naka ya tafi? Ina tunaninka da basirarka suka tafi? Idan ka sallameta me akayi kenan? Bukatar tamu bata biya ba kenan tunda ka kasa zame mata *wani haske* acikin rayuwarta, kayi hakuri jabir ban aura maka wannan yarinya ba har sai da nayi bincike akanta, sannan duk wadannan abubuwan laifinka ne yasa suka faru,saboda ka kasa janta ajikinka, ka kasa sake mata fuska ka kasa bata damar da zata zauna dakai ta fuskanceka ka fuskanceta har ta fahimci menene musulunci har taji ya kwanta mata arai, duk ba kayi wannan ba, meyasa?"

"Malam insha Allahu zanyi kokarin kwatanta hakan"

"Kayi kokari ka kwatanta jabiru saboda ko dan lahirarka domin yarinyar nan tanada wani hakki na musamman a wuyanka muddin ka danne daya daga ciki saboda kaga ita bata salla to wallahi babu ruwan Allah dole ne ya tambayeka yanda ka gudanar da rayuwarka tareda iyalinka, muddin ka fifita daya akan daya saboda ita ba musulma bace to wallahi kasani ranar gobe kiyama zaka tashi gefen jikinka a shanye domin haka annabi yacewa sahabbai duk wanda suka ga rabin jikinsa ya shanye ranar alkiyama to karsu tambayi kowa shine Wanda baya adalci a tsakanin iyalansa, sannan ya kamata ka kyautatawa yarinyar nan domin annabi yace mafi alkairunku shine wanda yafi kyautatawa iyalansa amma ni nafiku alkairi saboda nafi kowa kyautatawa iyalai na,ka zauna da matarka da aminci taji dadin zama dakai ka sake mata fuska kayi wasa da ita kayi dariya da ita kayi mata duk wata hidama wacce zata ja ra'ayinta zuwa gareka"

Ajiyar zuciya jabir ya saki tabbas yasan duk wadannan abubuwan da Malam ya fada gaskiyane kuma tun farko hakan ya kamata ace yayi amma bai yi ba,

"Nagode Malam Allah ya saka da alkairi kuma in sha Allahu zanyi aiki da abinda ka fada min"

"Allah yayi maka albarka, agaida iyalin"

Tashi jabir yayi yana kallon al'amin "to za mu tafi ko anan zan barka wurin malam?"

"A'a daukeshi ku tafi dan ba zama zaiyi ba kana tafiya zai tada rikici yace shi abbunshi shi umminshi"

Mikewa al'amin yayi yana dariya "ni abbuna zanbi"

Sallama suka yiwa malam suka tafi, Gida suka koma suna shiga part din goodness yayiwa tsinke al'amin yana biye dashi, acikin dakinta ya iskota ta takure a karshen gado,

Har bakin gadonta yaje ya zauna abunda yayi mutukar bata mamaki,

"Goodness nazo ne domin muyi wata magana dake, abinda kikayi jiya banji dadinsa ba domin kin wulakantani kin wulakanta kanki a idon duniya, alcohol haramunne a musulunci duk da cewar nasan ke a addininku halal ce, tunda farko ban san kina shan alcohol ba da zan yi miki gargadi akanta domin ba ashanta agidana, sannan zancen zuwa church ni bazan hanaki zuwa ba but zaki rinka zuwane once in a week, amma daily service babu shi yanzu i have called up it at all,did you get me?"

"Yes sir but am so sorry, honest to God i have Neva take alcohol before, i swear jiyama deceiving dina suka yi suka bani but it will neva happen again" ta fada tana goge fuskarta,

"Don't worry i pardoned you,but you have to maintain it next time"

Tashi yayi ya juya ya fita yabar al'amin azaune awurinta, jin baya fushi da ita yasata sakin jikinta ta kamo hannun al'amin suka koma falo,

"Clever boy" tafada tana murza hannunsa,

"Anty farcenki yayi tsawo dayawa ki yanke ranar juma'a"

"Meyasa sai ranar friday? Yanzu ma sai in yanke my boy"

"A'a anty abbuna duk ranar juma'a yake yanke farcensa dana tambayeshi sai yace min yanke farce ranar juma'a tana daya daga cikin sunnonin ranar juma'a"

"Nagode my boy nima ranar juma'ar i will cut my pinger nails"

"Yawwa anty kinga nima zan samu lada saboda annabi yace duk wanda yayi nuni da aikin alkairi to zai samu kwatankwacin ladan wanda yayi aikin"

Baki ta rike tana kallonsa yanda yake magana kamar abbunshi har lumshe idanuwansa irin nasa ne,

"Al'amin waye annabi? Naji komai sai kace annabi yace kaza yace kaza"


"Anty annabi shine annabi Muhammad (s.a.w),dan Abdullah, yazo da addinin musulunci, Allah ya aikoshi ga dukkan mutane baki daya, kuma shine na karshen annabawa, shugaban manzanni, mutum bazai taba zama cikakken mumuni ba har sai ya soshi kuma ya yarda dashi"

"Okey i understand now, nagane al'amin thanks for the explanation, let me go and cook indomie for us"

Tashi tayi ta shiga kitchen kafin ta fito shi kam al'amin ya koma wurin ummunshi.


Indomie ta dora tana aikin tana rera wakarta "am waiting my love love, no body can love it the way i do, am waiting my love love"

Jiyo sautin wayarta da tayi a falo yana tashi yasata kwallawa al'amin kira,

"My son pls help me with my phone" tafada da karfi, daidai lokacin mal jabir ya shigo cikin falon, sake kwallawa tayi da karfi,

"Al'amin can't you hearing me? I said make you bring me my phone"

Daukar wayar yayi ya bita cikin kitchen din, daga inda take tsaye tana zuba indomie din acikin tukunya ta miko hannu dan ta karba duk a tunaninta al'amin ne amma kuma ta jiyo sanyayyen kamshinsa sai dai duk da haka bata kawo shi bane domin a iya saninta yanzu yana office babu abinda zai dawo yi agida, tsal ruwan indomie din ya fantsalo mata a fuska hakan ya sata saurin ja da baya da sauri tana fadin,

"Ohh God", jinta tayi ta fada jikin mutum ta baya nan ta sake tsorata ta jiyo da sauri take ta kara fadawa kirjinsa da sauri ya tareta,

"Oh sorry i didn't hear your step, banji lokacin da ka shigo ba"

"Oya take your phone, dazu nayi mantuwa acikin dakinki, bari na dauka" mika mata wayar yayi ya juya ya fita tana biye dashi har cikin dakinta,

A inda ya tsaya dazu anan ya fara dube dube,

"Sir me ka yar?" Ta tambayeshi tana kallonsa ta bayanshi kasancewar ya bata baya,

"Bari gashi ma nagani" nuno mata wani dan karamin key yayi wanda daga gani na safe dinsa ne wato drawer din office dinsa Wanda yake ajiye documents masu muhimmanci,

Bashi hanya tayi ya juya ya fita, "adawo lafiya" ta fada tana kallonshi,

"Allah yasa" ya fada ahankali tare da ficewa, komawa kitchen tayi taci gaba da hidimominta.

Karfe _5_ daidai ya taso daga office ya dawo gida, sashensa ya shiga anan ya iske ummu da al'amin suna zaune acikin babban falonsa,

Mikewa ummu tayi ta amshi jakar dake rike a hannunsa tana yi masa sannu da zuwa yayinda shi kuma al'amin ya tashi ya rungumeshi yana cewa,

"Sannu da zuwa abbuna, abbu na me ka kawo min?"

Kansa ya shafa, "al'amin ya kamata muje muyi aski nida kai anjima ko?"

Kansa ya daga "na'am abbu"

"Yawwa yarona, bari nayi wanka naci abinci sai muje"

Sakin hannun al'amin yayi ya shiga bedroom dinsa, a kofar daki suka yi clashe da ummu, hannunta ya riko "me kika tanadar min?"

"Komai my dear" tafada tana zare masa hular dake kanshi,

"To nagode bari nayi wanka"

Rakashi cikin dakin tayi sannan ta fito ta kyaleshi.

Karfe _6_ ya kama hannun al'amin suka fita domin zuwa aski, part din goodness yayi niyyar zuwa kafin su fita, adai dai kofar falonta yaji ana kiransa a waya hakan ya sashi tsayawa domin amsa wayar yayinda shi kuma al'amin ya wuce cikin falon,

Al'amin na shiga ya sameta kwance tana kallo, sadadawa yayi yaje ya rufe mata ido duk a zatonshi wai bata ganshi ba,

Murmushi tayi ta kyaleshi, tana ji ya dauki bakin dankwalinta dake ajiye agefe ya daure mata fuska,

"Al'amin if i catch you ko? Hmm i know you are the one ai, bari natashi"

Dagudu ya zura bayan labule yana cewa "anty don't interrupt the game

8 / 35