Author : Hameedah Category : Complete Novels
kankame juna suka yi suna dariya.
BAYAN SHEKARA 20
*
Wata mata na hango tana sanye da katon hijabi har kasa awani wawakeken fili wanda mata suka cikashi tana yi musu wa'azi, ta kwashe fiyeda awanni 3 tana yi musu wa'azin kafin ta kammala ta rufe da addu'a,
Wurin motarta ta nufa ta bude ta shiga tana murmushi akusa da wani saurayi ta zauna wanda kallo daya zaka yi masa ka gane jabir ne sak "dan autan abbu yau kai kadai ka taho"
Murmushi shima saurayin yayi "ammun yau ban samu yan rakiya ba duk sunki
rakoni sunce awurin abbu zasu zauna"
"Kace yau gidan namu acike yake da yan jikoki" tafada tana dariya,
"Ai kuwa dai ammun"
"Allah dai yayi muku albarka abdul halim" tace dashi tana murmushi, tafiya kadan ta sadasu da gidansu, nan suka shiga tun kafin tafito wasu kyawawan kananan yara kimanin su 10 suka taho suka rungumeta suna "jaddati oyoyo"
Rungumesu tayi suka shiga cikin falonta inda jabir ke zaune da wasu yaran yana koya musu alifun ba'un,
"Abbu yau haka gidan namu ya zama?"
Dagowa yayi ya kalleta "ga masu gyara gida nan sun zo yau"
Cikin dakinta ta wuce ta zauna tana hamdala acikin ranta domin hakika jabir ya zama *_WANI HASKE_* acikin rayuwarta domin ta sanadinshi duk danginta dake okene sunzo sun musulunta awurin jabir gashi yara 9 Allah ya azurtasu da samu ita dashi tun daga kan tasleem, abdullah, abdulrahman, abdulrahim, abdul hamid,abdul rashid, abdul gani, abdul malik sai dan autansu abdul halim,gashi yanzu harda jikoki suke dasu wurin su goma sha biyar,
Shigowar jabir ce ta katse mata tunanin da take yi,
"Yanmatan abbu ki shirya danki al'amin ya biya mana umarah"
Yafada yana zama akusa da ita,
"Allah saka masa da alkairi, shima Allah ya bashi masu yi masa" tafada idonta narai narai,
"Kar kiyi min kuka, nidai yanzu kulawa nake son kibani domin nakada wadancan jikokin naki zuwa gidan zoo suda uncle dinsu abdul halim"
Murmushi tayi ta kwantar da kanta ajikinshi "abbu baka gajiya dani, ban taba ganin sauyin fuska atattare dakai ba"
Hannunta ya kama ya rike cikin nasa,
"Binti duk auran da aka ginashi akarkashin koyarwar ma'aiki to haka yake kasancewa, shiyasa annabi yace maza su auri mace mai addini domin itace matar da kullum tana tsufa tana sake rike addininta, maimakon kaji tana fita daga ranka sai dai kaji tana sake shiga cikin ranka, sannan duk soyayyar da aka yita saboda Allah to tana dorewa"
Hannunshi ta matsa "nidai nayi sa'a, ina addu'a Allah yabarni dakai har lokacin da zan koma gareshi"
"Kizo muje mu kula da junanmu kidaina yi min maganar rabuwa"
Yace da ita gamida daukarta zuwa special room.
*ALHAMDULILLAH*
Anan nakawo karshen littafin wani haske ina addu'ar Allah yatara mu acikin ladan ya yafe mana kuskuren dake ciki, duk wacce ta karanta wani haske taji dadinshi to ta taimaka tayiwa ummi A'isha addu'a akan Allah ya biya mata bukatarta.
*SADAUKARWA*
Na sadaukar da wani haske gareki kawata *BAHIJJA BEBEELO* (marubuciyar D'a na kowane) dake da dukkan masoyan littafin wani haske, Allah ya raya miki yarinyarki iman, nagode kwarai da kaunarki agareni.
*TUKWICI NE*
agareki bestyna *PHERTYMAH XARAH* (marubuciyar littafin matar sadiq),Allah yakara dankon zumunci agaremu.
*DOMINKU NE*
Masoyana masu yi min fatan alkairi akoda yaushe.
*JINJINA GAREKI*
Uwar dakina *HAUWA M JABO* nagode da kulawarki.
*KINA RAINA*
Aminiyata mai share min kukana *CWT KAUSAR LUV*, hakika kinfi karfin kawa agareni, ke ta dabance awurina ina kaunarki kawata, Allah yabarmu tare,tabbas banda kamarki.
*FATAN ALKHAIRI*
Gareki tawan kawata *KHADIJA SIDI* nayaba miki sosai hakika ke ta musamman ce agareni.
Gaisuwa ta musamman gareku masoya yan uwana marubuta, ina addu'ar Allah ya kara muku basira da hazaka, yaci gaba da taimakonku acikin al'amuranku, ya kara muku baiwa mai amfani,ya baku lada aduk inda kuka yi daidai, ya yafe muku a inda kuka yi kuskure.
Gaisuwa mai dunbin yawa gareku masoya wadanda suke karanta rubutuna suna yimin fatan alkairi akoda yaushe, nagode muku sosai ina kaunarku mutuka kuma ina addu'ar Allah yabar zumuncin dake tsakaninmu, duk wanda yake kaunar ummi A'isha ko kuma yake kaunar rubutunta ko yaji tana burgeshi ko yaji yana sonta to UMMI A'ISHA loves you too, sai mun hadu acikin labari nagaba da yardar mai sama Rabbi Azimu.
DOCUMENT MADE BY SALMARH