Author : Hameedah Category : Complete Novels
wuyanta,
"Abbu nagode, kaima kayi kyau din ai"
Rike hannuwanshi tayi tana faman sunkuyar da kanta, "binti menene hakan? Me hakan yake nufi?"
Dagowa tayi ta kalleshi, "abbu muje kayi wanka"
Hannunshi tafara ja tana tafiya, binta yayi har cikin bedroom dinshi, hularshi ta cire ta nufi drewar domin adanawa, tana ajiyewa ta dawo inda yake tafara kokarin cire masa babbar rigar jikinshi, yana tsaye yana aikin kallonta duk wani motsinta akan idonshi ne har ta gama cire masa kayan ta barshi dagashi sai farar vest da gajeren wando blue,
"Bari nazuba maka ruwan wankan abbu"
Binta yayi har cikin toilet din tana hada masa ruwan yana ta bayanta atsaye sai da ta kammala cika wani katon baho da ruwa sannan ta jiyo gareshi,
"Abbu gashi" tana gama fada tafara kokarin fita, hannunta ya riko da tausassan hannunshi,
"Kar ki tafi binti, ki tsaya ki karasa ladanki"
Hannunta tafara kokarin zamewa daga nashi tana mammake kafadarta, cikin shagwaba tafara magana,
"Nidai abbu nayi wanka na dazu, dan Allah ka bar min kwalliyata kar ka bata min"
Janta yayi da karfi yayi mata masauki acikin kirjinshi "tsaya kiji bintina, kawo kunnenki nafada miki wani abu"
"Nidai a'a, abbu wlh kazama marar hakuri yanzu, gaskiya gobe kayi azumi"
"Babu azumin da zanyi, kuma ai kece kika sani nazama marar hakurin"
Daukarta yayi cak ya ajiyeta cikin bahon wankan.
Daukota yayi ya ajiyeta agefen gado yana yi mata dariya "binti da kikace bakya so, ashe dama gulma ce kinma fini so"
Fuskarta ta rufe da tafin hannunta,"abbu kabari ko inyi maka kuka"
Murmushi yayi yaje ya dauko lotion yazo inda take "yi hakuri kar kiyi pls"
Ajiyar zuciya ta saki daidai lokacin da yafara warware towel din jikinta domin shafa mata mai,
Agurguje ya shiryata shima ya shirya dama yanzu tanada kaya ajiyayyu acikin dakinsa kusan ma duk abubuwan da zata bukata ta ajiyesu adakin,
Hannunta yakama zuwa falo domin saura kadan lokacin sallar mangarib yayi, sai alokacin suka tuna da files din dake ajiye akofar falon
"Binti kina sani ina mantuwa fa" yafada yana jan hancinta,
Hannunshi ta rike "nidai kar ka dora min laifi abbu"
Tana manne ajikinsa sukaje suka dauko files din suka shigo dashi, zama tayi akan cinyarsa tareda kwantar da kanta ajikin kirjinsa,
"Zaki barni na iya yin aikin nan kuwa? Yace da ita yana shafar kanta,
"Zan barka mana abbu"
"To dagani naje masallaci nadawo" kiss tayi masa akan kumatunsa kafin ta dagashi tana kallonsa, masallaci ya fita ita kuma ta koma sashenta, sai da yayi har sallar isha sannan ya dawo gidan nan ya iske bahijja ta sake caba ado tasha kwalliya sosai cikin leshi yellow mai stones ajiki,
Zama tayi ajikinsa suka fara mikawa junansu sakonnin soyayya masu nauyin gaske, sun dade suna nunawa junansu soyayya kafin su hau dining table suka ciyar da junansu,
Falo suka dawo jabir yafara ayyukansa amma kuma duk hankalinsa yana kan bahijja motsi kadan sai ya kalleta dakyar ya samu ya duba files guda biyar daga nan ya rufe babin aikin ya bude babin soyayya shida bintinsa.
Misalin karfe 10 suna kwance adakinshi yana rike da hannunta yana da wasa dashi ya fara tambayarta akan littafin da yafara koyar da ita na akdari,
"Menene farkon abinda ke wajaba akan baligi?"
Juyi tayi akan kirjinshi kafin ta bashi amsa "farkon abinda yake wajaba akan baligi shine ya inganta imaninsa sannan yasan da wanne abune zai gyara farillan ainihinsa dashi"
Sake tambayarta yayi "kamar da wanne abune zai inganta farillan ainihinsa dashi?"
"Abbu kamar hukunce hukuncen sallah, dana tsarki, dana azumi"
Sake rungumeta yayi yana yimata sumba akan goshinta, "yarinya ashe kina gane karatun da nake dora miki, wannan hukunce hukunce ya wajaba akan dukkan baligi ya sansu kuma yayi aiki dasu domin kowacce ibada ana son mutum yasan hukunce hukuncen da suka shafeta kafin ya gabatar da ita, misali salla, ana son baligi yasan abubuwan da suke warwareta da wadanda suke gyarata kamar kabli da ba'adi, hakama tsarki, azumi shima yakamata baligi yasan abubuwan da suke batashi da kuma abunda mai azumi ya kamata ya nisanta domin akwai abubuwa da dama da suke warware azumi wadanda bamu daukesu a matsayin manyan laifuffuka ba kamar giba yi da wani, kazafi da karya"
"Abbu menene giba?" Ta tambayeshi tana dago kanta domin kallon fuskarsa,
"Binti baki san giba ba? Giba itace gulma, zancen wani, annamimanci, fadin abu marar kyau ga wani wanda baya nan amma annabi ya siffatanta giba da cin naman mutum domin wani lokaci suna zaune da sahabbai sai yace dasu _"shin dayanku yana iya cin naman dan uwansa? Sai sahabbai sukace tayaya dayanmu zai ci naman dan uwansa ya rasulillah? Sai annabi yace duk wanda yayi zancen dan uwansa baya nan yafadi mummunan abu akansa yaci mutuncinsa to kamar yana yankan naman jikinsa yana cine"_,kinga kuwa indai hakane ya zama dole mu rinka kame harshenmu domin shine yafi komai hatsari atattare damu shiyasa alokacin sahabbai akwai sahabin da yake zuba duwatsu acikin bakinsa saboda kar yafadi wata magana wacce ta kaucewa shari'a,shiyasa sai kiga sahabi yayi kwana uku baiyi magana ba yana ta juya maganar acikin zuciyarshi yana tunanin shin ya fadeta ko yayi shiru, akwai wania sahabi wanda ya nemida annabi yayi masa nasiha sai annabi ya zaro harshensa ya nuna masa yace kaji tsoron wannan domin yana halakarwa,amma mu ya muke ayanzu? Bamu dauki gulma da annamimanci amatsayin laifi ba gashi mun iya cin mutuncin junanmu bayan kuma acikin wani hadisi annabi yace _"'duk wanda yaci mutuncin dan uwansa to Allah zaici mutuncin fuskarsa da wuta aranar alqiyama"'_ bafa wai dan uwa najini ba a'a dan uwa musulmi domin musulmi dan uwan musulmi ne haka annabi yafada, shiyasa yana da kyau mutane su rinka sauraron malamai saboda su gane illar gulma da annamimanci da k'azafi domin dukkaninsu laifuka ne masu nauyin gaske shi kansa mai yin annamimancin ma annabi cewa yayi _"'La yadkulil jannatu nammamun, wato annamimi bazai shiga aljannaba"'_ wannan hadisin daga wurin huzaifa dan yamani aka karbo shi,bukhari da muslim kuma suka rawaitoshi"
"Abbu Allah ya rabamu da sharrin harshe"
"Amin binti, kina jin bacci ko wata hirar za muyi?"
Idanuwanta ta rufe da tafin hanunta "abbu sai kanata sani ina jin kunya"
Murmushi yayi ya zare hannun nata daga fuskarta, "hakanma da lada binti domin kunya wani yanki ne daga cikin yanki na imani"
"To nidai bacci zanyi kayi min addu'a"
"To shikenan Allah ya kaimu gobe da asuba sai kiyi biyan bashi"
Shiru tayi tai lakwas ajikinsa yafara karanto mata addu'o'in kwanciya bacci yana tofa mata ajikinta.
Washe gari da safe bayan ya shirya domin zuwa office ya riko hannun bahijja wacce tasha gayu cikin farar atamfarta mai zanen hannu ajiki,
"Binti ki hada min kayana anjima zanyi tafiya, zanje Kaduna wani conference"
Yatsunshi ta riko ta makalkaleshi,
"Abbu tare zamu tafi ko?"
Kai ya girgiza mata "a'a batare zamuje ba, ai kinga hotel ne bazan iya zuwa dake hotel ba, kiyi hakuri kinji kwana 3 kawai zanyi"
Daru tasa masa tafara doddoka kafafunta akasa tana kuka kamar wata yar karamar yarinya,
"Nidai abbu sai nabika, kuma shikenan ni kadai zaka bari, nidai bazan yarda ba, tare zamu tafi" tana fada tana kuka, kallo kawai yake binta dashi dama haka ya guda shiyasa yaki sanar mata da maganar tafiyar tun jiya saboda yasan zaisha rikici da shagwaba iri iri,
Binta yayi inda take tsaye ta juya masa baya tana kuka, ahankali ya rungumeta ta baya yafara kissing din wuyanta, juyo da ita yayi ya zubawa fuskarta ido, kuka take yi sosai kamar wacce aka yiwa mutuwa,
"Kiyi shiru binti, kwana ukune fa"
Idonta ta runtse wasu sabbin hawayen suka sake iyo ambaliya akan Kumatunta,
"Dan Allah abbu kar ka tafi ka barni"
Rungumeta ya sakeyi ajikinsa "to binti, shikenan amma dai ki hada min kayan bari naje office nadawo, ba lallai ne ma nayi tafiyar ba amma dai kihada min kayan kinji"
Kai ta daga masa tafara share hawayen kan fuskarta, dakyar ya iya rarrashinta ta tsaida kukan sannan ta rakashi tsakar gida tadawo tafara hada mishi kayan nan dinma tanayi tana hawaye har ta kammala.
Karfe 3 nayamma ya dawo gidan lokacin tana sashenta tana gyara style din dayan bedroom dinta tana canja salon jeren cikin dakin domin abune mai kyau uwar gida ta rinka sauyawa dakinta fasalin jerensa daga lokaci zuwa lokaci,
Ahankali ya sadada yaje inda take tsaye da pillow ahannunta tana gyarashi acikin rigarsa, ta bayanta ya tsaya yakai hannu ya toshe mata baki,
Mutsu mutsu ta fara yi tana ihun da ba a ji, kokawa take yi iya karfinta tana kokarin kwatar jikinta sai kuma tafara jin kamshin turarensa ahankali yana ziyartar hancinta,
Sakinta yayi yana yi mata dariya,
"Ke matsoraciya ce binti"
Kallonsa tayi sai kawai ta dauki pillow tafara kai masa duka
"Abbu kayi mugun bani tsoro wlh, nazata gardine ya shigo min gidan"
"Yi hakuri bintina, babu wanda ya shigo miki, nine nan"
Dukan ya shiga karewa da hannunsa har yayi nasarar kwace pillow din yajata ya hadata da jikinsa ya rungume,
"Abbu zakayi tafiyar ko ka fasa?"
"Binti kibari kibani abinci naci mana tukunna"
Hannunshi takama suka tasamma part dinshi inda ta shirya masa abinci mai rai da motsi, white rice with stew sai hadin salad,
Suna ci tana yi masa hira har suka kammala, zancen tafiyarshi ya fara yi mata anan tasake tayar masa da wani darun, kuka ta saka masa,
Janta yayi jikinsa yafara lashe fuskarta yana shanye hawayen da take yi, wata irin zazzafar soyayya yashiga nuna mata dolenta tayi shiru ta daina kukan,
Daukarta yayi yakaita cikin dakinshi ya ajiyeta akan tangamemen gadonshi yashiga nuna mata so.
Ajikinshi ya kwantar da ita yafara yi mata tausa adukkan bangarorin jikinta,iska yafara hura mata acikin kunnenta yana yimata kalamai masu dadi dan haka lokaci kankani bacci yayi awon gaba da ita.
Kwantar da ita yayi yatashi ahankali ya nufi toilet yayi wanka ya fito, cikin sauri sauri yayi shirinsa yasaka kayanshi ya debi dukkan muhimman abubuwanshi ya karasa Inda take kwance rungume da pillow ita ala dole shi ta rungume, sunkuyawa yayi ya kai bakinshi kan nata yayi mata kiss, yasake yi mata wani agoshinta sannan kumatunta sai nakarshe a tsakiyar kirjinta,
Jakarshi ya dauka yafita domin ya kusa makara saboda jirgin 4:30 zaibi zuwa Kaduna yanzu kuma gashi 4 harda yan mintuna ga baiyi salla ba.
Yana tafe yana waiwayenta har yafice daga cikin dakin, sai da ya tsaya a masallaci yayi salla sannan driver ya tafi kaishi airport, gaba daya jinsa yake yi babu dadi saboda zai tafi yabar bintinshi wacce yanzu yana jinta acikin ransa fiyeda yanda yake jin kanshi,kamar ya kirata awaya sai kuma ya rabuda ita yaga gwanda ya barta har sai ya sauka agarin Kaduna tukunna.
Bahijja kuwa tunda jabir yatafi yabarta take ta bacci kamar wacce jabir ya durawa maganin bacci, ba ita ta iya tashi ba sai wurin karfe 5:30, ahankali tafara bude idonta, ganinta tayi rungume da pillow amadadin jabir, ahankali ta tashi zaune sai kuma ta shagwabe fuska tafara kuka tana kiran
"Abbu...!" Ta kira sunanshi cikin shagwaba da kuka,
"Abbu...!" Jin shiru bai amsaba yasata tashi ta jawo towel dinshi ta daura ta leka cikin bathroom amma wayam baya ciki,
Fitowa tayi tana tafiya tana kuka tana kiransa, falo ta duba nanma baya nan, dakinshi ta sake dawowa ganin babu jakar data hada masa kayan tafiyarshi ya tabbatar mata da wayo yayi mata yai tafiyarsa,
Da kukanta ta shiga toilet tayi wanka tafito gashi ko salla bata yiba gashi jabir yau ya tara mata gajiya ba kadanba gashi baya nan, daurewa tayi ta daina kukan ta shirya tayi salla ta zauna tafara tasbihi har 6 tayi, alokacin taji kiran jabir awayarta,
Daukar wayar tayi bayan tafara kuka "abbu...!"
Jin muryarta ya tabbatar wa da jabir kuka take yi,
"Binti kukanne har yanzu baki daina ba?"
"Abbu shine ka tafi ka barni, kayi min wayo kasani bacci kafin natashi ka gudu"
Dan sansanyan murmushi jabir yayi yana mai tuno kyakkyawar fuskarta da dukkan kyakkyawar surarta wacce take tsumashi acikin kowanne irin yanayi,
"Ba gudu nayi na barki ba binti na, kiyi hakuri kinji, ba dadewa fa zanyi ba"
"Nidai bazan hakura ba sai dai idan ba zaka sake tafiya ka barni ba"
Kiss yayi mata ta cikin wayar "bazan sake ba binti wannan ma dan babu yanda zanyi ne amma bazan sakeba,i promised you my binti, ga sako nan naturo miki"
Murmushin itama tayi ta fara mayar masa da martanin kiss din da yayi mata,
"Binti kiyi hakuri ki bari haka kar kisa nakasa bacci"
Fuskarta tasoma gogewa sannan ahankali ta furta "abbu dan Allah kar ka kalli yanmata"
Dariya tasashi yi batare da ya shirya ba "binti ni ina ma zanga yanmata? Ina daki babu inda zanje daga daki sai ko dakin taron da zamu gudanar da conference din, ki kwantar da hankalinki kinji, daga ke babu kari kece yar auta awurina"
Tamkar yayi mata bishara da gidan aljanna haka taji, "abbu to yaushe zaka dawo?"
"Haba binti anyita nanata magana dayane? 3 days zanyi babu yawa"
Rufe idonta tayi tana tunanin yau ko a ina zata kwana,
"To abbu Allah ya kaimu"
"Amin binti, anjima zan kiraki kinji"
Kashe wayar tayi tana tunaninshi acikin zuciyarta.
Daren ranar bata iya bacci ba dakinta taje ta kwanta amma tunanin abbunta ya dameta, zaune ta tashi ta zubawa kan gadon ido tana nazari,
tattarawa tayi takoma dakin jabir ta kwanta amma kuma sam ta kasa baccin da zarar ta rufe idonta babu abinda take gani sai yanayin da suke kasancewa tare ako wanne lokacin bacci,idan kuma ta bude idonta sai ta rinka ganin kamar zata ganshi ne,
Daukar wayarta tayi tasoma laluben wayar jabir amma fuskarta sharkaf take da hawaye ohh bahijja irin wannan kuka haka sai kace pherty,
Jabir na daukar wayar yaji shasshekar kukanta "abbu nakasa bacci"
"Yi hakuri binti, kiyi alwala kiyi sallar nafila kinji, ko kin fara hutu?"
"Kai abbu yaushe nafara hutun naga dazuma kafin katafi kasan ina salla"
Murmushi yayi "ai tambayace binti, nasani ko nadace kwallona ya shiga raga"
"Kai abbu" tafada cikeda kunya,
"Ke binti" ya kwaikwayi maganarta, hakan da yayi ne yabata dariya,
Dariya take yi tana kyakyatawa kamar ba itace take kuka yanzu ba,
"Abbu ai al'amin ya ishemu"
"A'a binti al'amin dan ummu ne kema ki daure ki dage ki samu ki haifi naki,ko bakya son ki haifi mai kama da ni? Nafi son kema ki haihu ki zama mama"
Hannunta tasa ta toshe bakinta tana murmushi, cikin dabara ya samu ya rabata da damuwar da ta shiga, sun dade suna hira har tafara gyangyadi, addu'ar bacci yayi mata ta shafa ta kwanta taci gaba dayin wayar dashi yana bata labari mai dadi, shirun da yajine ya tabbatar masa da cewar tayi bacci, wayar ya kashe yana murmushi.
Kullum suna makale awaya dashi har yayi kwana ukun, aranar da zai dawo taje gidan kitso aka yarfo mata kananan kitso masu kyau harda wanda aka zubo mata shi gaban goshinta aka tufke mata shi,
Rasa inda zata saka kanta tayi dan tsananin murna, alla alla takeyi kawai ya dawo ta ganshi saboda tayi missing dinshi ba kadan ba.
Karfe 2:30 ya sauka amma baije gida ba office yawuce tunda ya sanar da ita saukarsa taji kamar tayi tsuntsuwa taje ta daukoshi, jin yatafi office yasata kasa hakuri har saida ta aika masa da lafiyayyen girkin da tayi masa. Sai da yasha aiki a office har 5 tayi sannan ya tashi ya nufi gida,
Yana zuwa gidan sashen bahijja yafara shiga amma ko ina ya duba bata nan dan haka ya fita ya nufi nasa sashen, tunda ya shiga falon yake shakar kamshi mai dadi yana tashi afalon,
Jakarshi ya ajiye ya tasamma cikin bedroom dinshi, abin mamaki nanma bata ciki juyawa yayi zai fita amma aranshi yana tunanin to ina bahijja ta tafi, jinta yayi dalaf ta daleshi tana murna,
"Oyoyo abbuna"
Makaleta yayi ya nufi gaban mirror ya tsaya yana hangota ta cikin mudubin, wata kwalliya tasha tayi kyau sosai tayi kwalliya sosai cikin yar bingilar pink din rigarta da bakin wando matsattse,
Birkitota yayi yafara kallon kitson kanta yana shafashi,
"Waye yayi miki wannan kitson? Yayi kyau"
"Nagode abbu, agidan kitsone can baya"
"To zan bada tukwici yanzun nan"
Bata ankaraba taji yayi sama da ita bai direta ako inaba sai akan makeken gadonshi.
Basu iya barin junansu ba sai daf da sallar magrib, daukarta yayi zuwa bathroom yayi mata wanka yayi mata alwala ya dawo da ita cikin dakin, ita dai duk kunya ta gama rufeta,
"Daga dawowa ko gaisawa ba muyi ba kika rikitani da soyayyarki" yafada cikin tsokana yana kokarin daura mata towel,
"Ayya abbu ai laifinka ne ba nawa ba" rufe fuskarta tayi bayan tagama maganar,
"Nagode miki sosai kuma naji dadi Allah ya yi miki albarka binti"
"Amin abbu, nagode"
Shiryawa yayi agurguje ya saka jallabiya kalar ruwan toka ya tafi masallaci bayan ya shiryata itama.
Haka rayuwa taci gaba da kasance musu cikin farin ciki da annashuwa gashi kullum cikin kyautatawa junansu suke, ita dai bahijja bata da damuwar komai sai ta mahaifiyarta domin kullum abin sake tabarbarewa yake babu sauki saima gaba da yakeyi, duk lokacin da taje gidan bata samun sakin fuska awurin ma sai ko wurin mahaifinta.
Cikin wannan yanayine jabir yayi musu shirin zuwa madina domin suyi umarah sannan su ziyarci su ummu al'amin saboda rabonsa dasu yanzu ankusa shekara saura yan watanni,
Lokacin da bahijja taji wannan albishir din ba karamin murna tayi ba anan suka shiga yin shirin tafiya bayan duk abinda zasu bukata natafiya ya kammalu, sai da suka je suka yiwa dukkan wand yacancanta sallama sannan suka daga kowannensu zuciyarsa dauke da murna musamman ma bahijja.
Acikin jirgi ajikin jabir ta lafe ta makaleshi gam tana muzurai sai aikin hararar wata mata take yi wacce ke gefen jabir azaune tana satar kallonshi,
"Abbu jiyo da fuskarka nan" tafada gamida saka hannunta ta jiyo da fuskarshi zuwa kusa da tata,
"Menene binti?" Ya tambayeta yana dora idanuwansa kan nata,
"Gani nayine sai kallonka ake tayi kai kadai sai kace babu wani namiji anan sai kai daya" tafadi hakan cikeda kishi,
"Binti dadina dake kishi, kinada kishi sosai tun kafin kisan abinda ake yiwa kishin,bare yanzu da kika sani"
Idonta ta sauke ta kwantar da kanta akan kafadarshi tana murmushi, hirarsu suka ci gaba dayi har Allah ya saukesu acikin madina,
Lokacin da suka fito suka hango al'amin da ummunshi tsaye suna jiran isowarsu, kallon kallo aka fara yi tun daga nesa tsakanin ummu da bahijja,
Hannunta rike cikin na jabir tasha bakar doguwar Arabian gown sannan ta yane kanta da bakin mayafin rigar, ba karamin kyau ta sake yi ba,
Ita dinma bahijjan shigar da ummun tayi take