Author : Hameedah Category : Complete Novels
da miya, na'a na'a ta dafawa jabir ta kai masa sannan ta koma sashenta tayi wanka ta saka kayan bacci lokacin karfe _8_ na dare, zama tayi ta fara kallon wani Nigerian film mai suna _the night of spirit_ film din ya tara abubuwan tsoro daban daban amma haka ta tsaida idonta take kallo, tana zaune part one ya kare aka saka part two shima ya kare aka saka part three duk tana zaune tana kallo, ba agama film dinba sai karge 1:30 nadare, tana gama kallon ta karkashe komai taje ta kwanta anan kuma tsoro yace salamu alaikum domin abubuwan da ta gaggani a film dinne suka fara dawowa kwakwalwarta gashi wani irin kukan aljanun take ji acikin kunnuwanta, tsorone ya kamata sosai acikin duhun daren take ganin halittun data gani dazu,
Kun san goodness da tsoro ai aguje ta tashi ta bude kofa ta nufi sashen jabir da gudu kanta babu dan kwali kafarta babu koda takalmi.
*_Ummi A'isha_*ππ»
[10/11, 2:52 PM] βͺ+234 701 117 6189β¬: [9/19, 9:16 PM] Ummi A'ishaππ»: *WANI HASKE....!*
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_67-70_
~~~ A firgice ta kama kofar falon jabir ta bude ta shiga jikinta yana karkarwa, acikin falonshi ta hangoshi yana tsaye akan darduma yana salla, yana sanye da kayan bacci light blue masu santsi riga da wando,
Lungun kujera taje ta takure tana jiranshi ya gama, amma da yake doguwar sura yake karantawa sai da ta shafe wurin mintuna 20 kafin yayi sallama ya juyo yana kallonta, duk kitson attach din kanta ya gama yamutsewa sannan kallo daya zaka yi mata ka fahimci cewar a tsorace take ainun,
"Goodness meya faru?" Ya tambayeta yana mai kallonta,bakinta yana rawa tace,
"Sir i can't sleep inside my room"
"Why?" Ya sake tambayarta,
"Sir i can't, am afraid" ta sake bashi amsa,
"What do you want now?" Ya tambayeta,
"Sir i want to sleep inside your room pls"
"Ok shiga ki kwanta" yace da ita,
"No Sir ka gama sai mu shiga tare" ta fada tana tattara gashin kanta,
Bai sake magana ba ya tashi ya gabatar da shafa'i da wutri, duk tana zaune agefe tana kallonshi, hannuwanshi ya daga sama ya fara addu'o'i bayan yayi sallama, mintuna kadan ya shafa ya tashi ya juyo ya dan kalleta,
"Shigo" ya fada a takaice, tashi tayi sim sim sim ta bishi tana mai cigaba da karkarwa, wannan shine karo na farko da ta fara shiga bedroom dinshi, wani sanyin kamshi ne mai dadi ya bugi hancinta lokacin da ta saka kai domin shiga, katon gado kirar royal bed ta gani coffee colour wanda akalla mutane sama da guda biyar zasu iya kwana akai, gefe mirror ne cike da turarurraka kala kala, daga bari daya kuma dan karamin library ne cikeda littattafan addini iri iri sannan ga wani kebantaccen wuri nan wanda da alama wurin salla ne,
"Kije ki kwanta" ya fada yana nuna mata gadon,
Ahankali ta hau kan gadon taje jikin bango ta takure tana mai runtse idonta,
Zama yayi agefen gadon yana kokarin bude laptop dinshi nan ya fara daddannata wanda bata san iya adadin lokacin da ya dauka ahaka ba bacci yayi gaba da ita.
Ya dade azaune yana amsawa mutane fatawarsu wato tambayoyin addini ta kafar sada zumunta na facebook kafin ya kashe laptop dinshi ya juya ya kalli goodness tana kwance rub da ciki tana makalkale da pillow tana ta sharar baccinta,
Light din dakin ya kashe ya kwanta agefen gadon ya fara addu'a,mintuna kadan da fara baccinshi yaji goodness tana k'ara tana tuje tuje, mafarki take yi wai aljanun da ta gani a film din dazu sune suka biyota bakinsu duk jini suna son shan jininta,
Wata k'ara ta sake saki cikin razani ta farka tana zare idanuwa, kusa da jabir ta matsa ta kwanta agefenshi ta kankameshi,
"Goodness wai meke damunki ne?"
"Sir wani film na kalla dazu shine nake tsorata" ta bashi amsa cikin razani,
"Shiyasa na hanaki kallon dare amma kullum bakida aiki sai in dare yayi ki zauna kallo wani time dinma har 3 kike kaiwa kina kallo"
"Sir ai nadaina, daga yau bazan sake ba"
"Shaidan ne kawai yake razanaki domin kyakkyawan mafarki daga Allah ne, mummunan mafarki kuma daga shaidan haka annabi Muhammad sallallahu alaihi wasallam ya fada, tsaya nayi miki addu'a" addu'ar da akeyi idan anyi mummunan mafarki ya fara karanta mata a tsakiyar kanta wato _Allahumma inni a'uzibika min sharri fi manami an yadurruni fi dini wa duniyaya_,yana gamawa ya karanto ayatul kursiyyu da amanar rasulu sai falaqi da nasi ya shafa mata a fuskarta, wani sanyi taji yana shigarta, lafewa tayi luf acikin jikinsa tana shakar daddadan kamshin da yake fita daga jikinsa na turaren madinatul akram, lokaci k'ank'ani bacci ya sake dauketa, yana jinta tana fitar da numfashi ahankali wanda yake sauka akan kirjinsa, gaba daya jikinsa yarrrrrr! Yake jinsa amma ya daure ya kyaleta ajikinsa yau kadai domin itama taji irin dumin da mata ke samu ajikin mazajensu, bedside lamp ya kunna ya kalli agogo _2:50_ na dare, fitilar ya kashe ya mayar da idanuwansa ya lumshe har shima baccin yayi nasarar saceshi.
Sai misalin karfe _6:15_ jabir ya iya farkawa, lokacin gari har ya soma haske, idanuwansa ya bude ya saukesu akan goodness wacce ke mak'ale dashi tana bacci gaba daya ta kanannade ajikinshi ta cusa fuskarta cikin kirjinshi asalima bakinta akan kirjinshi yake, shi kuma ya zagaye hannuwanshi ya rungumeta wanda bai san lokacin da yayi hakan ba amma yasan acikin baccine,
Ahankali ya zame jikinsa ya tashi ya shiga toilet ya dauro alwala ya fito yazo yayi salla yana idarwa ya fara kallon gadon inda goodness ke kwance shidai rabon da ya rasa sallar asuba har ya manta saboda kullum cikin jam'i yake yin sallarsa, jijjiga kai yayi acikin zuciyarshi yana cewa "kenan kwanciyar da yarinyar nan tayi ajikina ne yasa na makara"
Alqur'ani mai girma ya bude ya fara karantawa har rana ta fito sannan ya rufe ya tashi yana kallon goodness, idonta ta bude ta kalleshi,amma ta kasa tashi, yana nan tsaye yana uzurinsa har ya gama ya shiga toilet domin yin wanka tana ganin haka tayi maza ta tashi tana duba wurin da take kwance duk gurin ya baci da jinin period din da yazo mata bata sani ba cikin dare, pillow ta dora awurin ta tashi ta fita ta koma sashenta domin shiryawa.
Bai jima ba ya fito daga wankan anan yaga bata dakin, zobenshi daya yaga ya fice daga dan yatsanshi hakan ya sashi matsawa gaban gadon ya fara dubawa, pillow din data dora akan wurin da ya baci ya janye nan yaga wurin ya gama baci da jini,
"Oh shiyasa dazu taki tashi? To ai dole nasan zata dawo tunda ban bata always din da na siyo mata ba" ya fada aranshi, pillow din ya mayar ya saka kamar yadda ta ajiye, a kasa gefen gadon ya hangi zoben nashi ya dauka.
Shiryawa yayi cikin farin boyel ya gyara sajensa da dan madaidaicin gemunsa,
Ita kuwa goodness tana zuwa dakinta wanka ta shiga amma koda ta fito sai ta tuna da bata da always ko daya, babban towel ta daura ta dauki wani dan madaidaici ta yafa ta rufa akanta tabi ta kofar baya ta shiga sashen jabir,
Yana tsaka da fesa turare ta shigo,
"Um, uhm good morning sir" ta fada kanta a sunkuye,
"Morning" ya fada atakaice,
"Sir wannan month din baka kawo min...!" Shiru tayi ta kasa karasawa,
"What?" Ya tambayeta yana kallon fuskarta,
"Sir.....!" Ta sake yin shiru,
"Go and carry it inside that drewar" ya nuna mata bedside drewar dinshi, wuceshi tayi taje ta dauko guda biyu tazo zata fita,
"Kar kiyi breakfast dani ina azumi" ya fada cikin muryarshi mai dandano,
"Ok sir, but sir pls don't lock your room,i want to clean it before you come back"
"Ok" ya fada ahankali, mitsitsin bakinshi ta kalla ta fice tana mai tunanin hali irin nashi, yanada kyawawan halaye wadanda kusan ma ita sune suka jata har ta fada cikin kaunarshi,
"He's a nice person" ta fada lokacin da take shiryawa, lokacin da ta gama kintsawa ta fito kitchen ta shiga ta hada tea tana tsaye tana sha ya shigo yayi mata sallama ya fita, agurguje ta shanye tea din ta tafi sashen jabir, gaba daya zanin gadon nashi ta yaye da pillow case din takai cikin toilet, acikin toilet din taga kananan kayanshi da kayan baccinshi acikin laundry basket, hadasu tayi duka ta wanke taje ta shanya ta koma ta wanke cikin toilet din sannan ta gyara dakin ta fesa room freshener,
Sashenta ta koma ta dora girki tunda shi jabir yana azumi kayan shan ruwansa daban zata yi masa dama ta saba ko lokacin da tana gida tana yiwa mahaifinta girkin shan ruwa,
Dankali da kwai ta soya masa ta dama kunu sannan ta dafa masa cous cous da miya, fruit ta gyara masa tayi musu design mai kyau, ita kuma ta hadawa kanta lemon kankana da kwakwa wanda ya zame mata jiki saboda kusan kullum sai ta shashi.
Bayan ta kammala komai ne taje sashen jabir ta shiryasu akan dining ta kwashi kayan da ta wanke ta zauna a falonshi ta fara goge su. Sai _6_ daidai ya samu damar shigowa gidan domin yau meeting yayi da directors dinshi a office sai 5:30 suka fito,
Yana shiga falonshi ya sameta tana goge kananan kayanshi da kayan baccinshi, tana yi tana rera yar wakarta,
"Welcome sir" tace dashi lokacin da ta dago ta ganshi,
"Thank you" ya fada ya wuce cikin dakinshi, dakin ba karamin kyau yayi ba gashi sai kamshine ke tashi, koda ya shiga cikin toilet dinma abin haka yake komai fes fes tsaf tsaf, cikin nishadi yayi wankanshi ya fito ya shirya ya fita lokacin an kira sallar magrib, hannunsa rikeda dabino yana ci ya sameta a falon har lokacin gugar take yi,
"Sir sannu" ta fada ahankali,
"Yawwa" shima ya fada ahankali tare da fita, bai dade da fita masallaci ba ta gama gugar kayan ta koma sashenta.
Sallar magrib kawai yayi ya dawo gida yasha ruwa, lokacin isha nayi ya koma masallaci, bashi ya dawo gidan ba sai wurin karfe 9,
Sashensa ya shiga ya yi wanka bayan ya dawo daga mosque, kayan bacci yasa maroon colour masu taushi, kamar kullum laptop dinshi ya bud'e ya shiga net ya fara amsa tambayoyin jama'a, yana nan zaune agefen gadonshi laptop din na ajiye akan cinyarshi goodness ta bude kofar dakin ta shigo, daga kai yayi ya kalleta tana sanye da kayan bacci doguwar riga mai rubi biyu iya gwiwarta light purple kanta sanye da hular roba baka, tana rike da karamin tea flask wanda ta zubo masa dafaffen shayin na'a na'a aciki,
"Weldon sir" tace dashi tareda karasawa gaban gadon ta ajiye masa tea flask din akan dan karamin stool dake ajiye agaban gadon,
Da mamakinsa sai yaga ta haye kan gadon tana cewa "sir aikin office ne kake yi har agida"
"Ba aikin office bane" ya bata amsa a takaice, pillow taja ta kwanta ta dora kanta akai tana mai fuskantar jabir wanda ya tsaida idonsa akan laptop din dake gabanshi lokaci lokaci kuma yana dan kurbar shayin dake ajiye agefenshi,
Fuskar nan tashi mai kyau ta zubawa ido tana kallo ko kiftawa bata yi, kamarsu daya sak da al'amin danshi sai dai shi al'amin din yafi shi hasken fata domin ummunshi ya dauko a haske amma baya ga haka komai na al'amin irin nashine,
"Oh my al'amin am missing you" tafada ahankali,
"Abbu bani aron wayarka" ta fada tana daga kwance, ahankali ya jiyo ya kalleta tareda maimaita sunan aranshi "abbu" yafada acikin zuciyarshi,
"Me zaki yi da wayata?" Ya tambayeta, "pls abbu i want to hear the voice of my lovely son al'amin" ta fada cikin shagwaba, daga kai yayi ya kalli agogo karfe _10_ saura yan mintuna,
"Yanzu al'amin yayi bacci amma gashi ki kira kiji" mika mata wayar yayi ta mika hannunta ta karba ta fara neman layin ummu al'amin din amma wayar akashe, ta dade tana kiran wayar amma bata samu ba dole ta hakura ta mika mishi,
Kallonsa tayi tace "abbu kayi min addu'a ina son zanyi bacci"
Dago kanshi yayi ya kalleta,
"Wacce irin addu'a?" Ya tambayeta tare da mayar da hankalinsa kan laptop dinshi,
"Irin wacce kayi min jiya, ban taba yin bacci cikin nutsuwa kamar wanda nayi jiya ba"
"Kawo hannuwanki inyi miki" ya fada ahankali, zaune ta tashi ta matsa kusa dashi ta hada hannuwanta wuri daya ta mika masa tafin hannuwan nata, addu'o'in kwanciya bacci ya karanto yana tofa mata acikin tafin hannunta har ya kammala ya dubeta,
"Ki shafe jikinki"
"Thank you abu al'amin" ta fada tana shafe jikinta kamar yadda yace, hakan data fada sai ta tuno masa da matarshi Salma wato ummu al'amin.
Kwanciya ta koma tayi tana kallon kyakkyawar fuskarshi har bacci ya dauketa, sai da ya kammala abinda yake yi sannan ya tashi yaje toilet ya dauro alwala yakoma inda ya keb'e domin gudanar da ibadarsa ya fara sallar nafila.
Can tsakar dare goodness ta farka daga bacci tafara dube dube domin taga gadon wayam babu jabir, acan gefe ta hangoshi yana salla, jijjiga kai tayi ta koma ta kwanta tana mai jinjina rikon addinin da jabir yake dashi, sai wurin _3_ ya hawo gadon ya kwanta har lokacin goodness idonta biyu tana kallonshi, addu'o'in kwanciya bacci yayi kafin ya kashe wutar dakin,
Minti 10 atsakani taja jikinta taje ta shiga jikin jabir kamar yadda tayi jiya, cikin barci ya rungumeta tareda k'ankameta ba tare da ya sani ba, tamkar zasu mayar da junansu cikin cikinsu haka suka yi.
K'arfe _5:30_ ya samu ya farka bakinsa dauke da salati,mamaki ne ya kamashi jin yadda shi da goodness suka makalkale junansu kamar wasu tif da taya, hannuwanshi yasa masu mutukar taushi ya janyeta daga jikinsa ya tashi ya shiga toilet, bin bayansa da kallo goodness tayi aranta tana mai burin inama zasu dawwama ahaka ita da jabir.
Tun kafin ya dawo daga masallaci ta koma sashenta tayi wanka ta shirya ta shiga kitchen ta hada abin karyawa ta dauka ta kaiwa jabir nashi sashensa sannan ta dawo dakinta tafara gyara kayan sawarta tana shisshiryasu cikin sif,
Stool din madubi ta dauko ta taka tahau dan ta dora wani akwatin kayanta asama, cikin tsautsaye ta goce ta fad'o, gefen kunkuminta sai da ya bugu da gadonta, tashi tayi kokarin yi amma ta kasa dan haka ta ci gaba da zama awurin har jabir yashigo yace mata ya tafi office.
Tunda ta buge agefen kunkumimta ta baya take tafiya dakyar tana dingishi, da haka ta samu tayi duk wasu ayyukanta har yamma tayi jabir ya dawo, ganinta tana yin dingishi ya sashi tambayarta abinda ya sameta, bata boye ba ta sanar dashi,
"Ok dauko Robb acikin dakina sai ki shafa awurin bayan kin gasa gun da ruwan zafi" ya fada yana kallonta,
"No abbu" ta fada tana mak'e kafadarta,
Bai sake cewa komai ba ya tashi yafita ya tafi salla sai da ya dawo yana zaune akan gado hannunsa kuma rikeda littafin _sahihul bukhari_ ta shigo tasha kayan baccinta doguwar riga fara sai faman kamshi take zubawa,
Kan gadon ta hau ta kwanta tana gyara hular kanta, mikewa jabir yayi ya ajiye littafin hannunsa akan drewar din gadon ya shiga toilet, ruwan zafi tafasasshe ya taro acikin karamin baho ya dauko towel karami wanda yake goge jikinshi dashi idan yayi wanka,
Tana kwance ta yi rub da ciki tana fuskantar bango yazo inda take,
"Oya tashi" yafada ahankali,
Tashi tayi babu musu ta juyo tana kallonsa ganinshi da kayan gashi ya sanyata mikewa da sauri domin guduwa, robar ruwan zafin ya ajiye ya yi sauron rikota babu zato ta fado jikinsa ta baya nan ya rungumeta baiyi wata wata ba ya dage rigar dake jikinta nan take farin pant din dake jikinta ya bayyana, da saninsa ya sake dage rigar domin yana son ganin kalar bra din da ta saka, itama fara ce sol,
"Hmmmm to match akayi kenan, komai white, that's good" ya fada acikin zuciyarshi, jin tana kokarin kwacewa daga rikon da yayi mata ne ya sanyashi dawowa daga duniyar tunanin da ya lula, towel din ya tsoma cikin ruwan zafi ya dauko shi yana tiriri gashi harda ruwan ajiki ya manna mata akan kunkuminta,
"Abbu, pls da zafi ka bari" ta fada arude, bai kulata ba ya sake tsoma towel din ya ciroshi ya dora mata akan wurin gashi idan ya dora baya daukewa har sai ya huce, haka yayi ta mata har sai da ya tabbatar gurin ya gasu sannan ya kyaleta,tashi tayi tana goge gumin da ya feso mata agoshinta dan azaba idonta kuma yayi rau rau tana son yin kwalla,
"Ungo Robb shafa awurin, ko ba zaki iya ba na shafa miki?" Ya fada yana bin lukuta lukutan cinyoyinta da kallo,
"No abbu zan iya" tafada cikin sauri tareda amsar Robb din, toilet ta shiga ta shafe wurin da Robb amma ba karamin dadi taji ba saboda har taji saukin ciwon da wurin yake yi mata,bude kofar toilet din tayi ta fita aranta tana jin dadin yadda jabir wani lokacin yake sakin jiki da ita har yayi mata wasu abubuwan masu kama da na masoya gashi yanzu ya sake shiga ranta sosai dalilin kwana da ta fara yi dashi a gado daya,
Yana zaune yana jona laptop dinshi a charge ta fito tana kawar da fuskarta, ta gefen ido ya dan kalleta yayi murmushi wanda shi kadai yasan yayishi, ya gane nufinta na shiga toilet wato dan kar yaga jikinta ne ya sanyata yin haka, bakinshi ya tabe aranshi yana cewa,
"Na nawa kuma? Jiki kam ai nagama gani yarinya sai dai ki kiyayi gaba kuma" idonshi ya lumshe ya tuno manyan cinyoyinta da ya gani dazu, juyawa yayi ya kalleta lokacin da take kokarin hawa kan gadon,
Gyara zamanshi yayi ya dauki laptop dinshi ya kunna ya dorata akan gadon ya fara lallatsawa,
"Abbu addu'a" ya jiyo muryar goodness tana fada masa cikin wani salo na daban,
Kamar yadda yayi mata jiya yau ma haka yayi mata ta shafa ta kwanta, amma kuma bacci yaki daukarta son jabir ne kawai ke azalzalar ruhinta, tana son amon muryarshi domin idan yana yin magana har ji take kamar dodon kunnenta zai suma da dadin muryarshi.
Fiyeda minti talatin ta shafe tana kallonshi yanata rubuce rubucenshi acikin laptop gashi ita kuma baccin yaki zuwar mata, tashi tayi zaune ta saisaita muryarta tace,
"Abbu kayi min labari, bacci yaki daukata yau" ta