Author : Hameedah Category : Complete Novels
take ji haka kawai,
Rankwafawa yayi saitin fuskarta wanda har tana iya jiyo fitar numfashinsa wanda yake sauka akan kumatunta,
"Yau bakya jin tsorone da zaki kwana ke daya?"
"Yeah" tafada atakaice gamida kokarin juya masa baya, batayi zatoba taji ya dauketa cancak yana kokarin sauka da ita daga kan gadon, zillewa ta fara yi tana tutturo baki,
"Nidai ka ajiyeni natafi da kafata"
Direta yayi yaja hannunta suka fita, shine ya tsaya ya rufe mata part din nata sannan suka wuce,
Tana gaba tana doddoka kafa shikuma yana baya biye da ita har suka shiga cikin bedroom dinshi,
Can karshen gadon taje ta kwanta ta juya kanta ta kalli bango, murmushi yayi ya matsa kusa da ita,aranshi yana tunanin hali irin na mata kwata kwata ba a iya musu domin ita kanta ummu al'amin complain take yi masa wai ya rage bata kulawa ba kamar da ba saboda ya sake aure alhalin itace bata sani ba shi har yanzu ma babu abinda ya hadashi da amaryar, wannan dalilinne ya sashi fara kwantar mata da hankali yana bata hakuri har goodness ta shigo ta sameshi to ashe itanma nata borin yana gaba,
Yan yatsun kafarta ya kama yafara jansu daya bayan daya ahankali,
"Binti fushi kike yi dani ko? Ki fada min abinda nayi miki sai in baki hakuri"
Idanuwanta ta rufe kamar meyin bacci, tashi yayi yana kallonta,
"Kici gaba da yimin shiru idan ina yi miki magana, shekaran jiyama ai hakkina ne yasa wannan kwaron ya cijeki, yauma idan da rabon zai cijeki shikenan"
Fitila yaje ya kashe, ai goodness najin haka tayi maza ta matsa kusa da barin da yake kwanciya, yana zuwa yajita kwance awurin, murmushi yayi ya kwanta agefenta ya lalubo hannuwanta ya hada ya rike cikin nashi,
"Abbu kayi hakuri bazan sakeba"
"Na hakura binti, karma ki sake bani hakuri akan wannan maganar"
Kanta yafara shafawa yana sinsinar daddadan kamshin turaren da jikinta ke futarwa so yake ya gane kowanne irin turare ne amma ya kasa, haka yaci gaba da sinsinarta har bacci ya daukesu bayan yayi musu addu'o'in neman tsari.
***
Washe gari da safe misalin karfe 10 tana falonshi zaune kusa dashi taji yana waya kan akawo masa kayan abinci wadanda zai rabawa makotansu sadaka, girgiza kai tayi agaskiya jabir dan aljanna ne domin yana kare hakkin duk wanda yake tare dashi ta raya hakan acikin zuciyarta,
Hannunta taji yana matsawa ashe har ya kammala wayar batare da tasani ba saboda ta tafi duniyar tunani,
"Binti tunanin me kikeyi ne?"
"Abbu babu komai kawai dai ina tunanin irin yadda kake kyautatawa kowane duk wanda zama ya hadaka dashi ciki kuwa harda makotanka"
Murmushi yayi mai yalwa "binti kenan ai makoci yanada babban hakki akan makocinsa domin annabi ya kasance yana yiwa sahabbai nasiha akan girman makoci, bai gushe ba har saida sahabbai suka tsammaci annabi zaice makoci zai iya gadon makocinsa, shi makoci ai abin tambayane ranar gobe alqiyama shiyasa ake son ka kyautata musu akoda yaushe domin acikin alqur'ani mai girma akwai inda Allah ya ambaci cewar abawa makoci hakkinsa, haka kuma annabi yace : _imanin dayanku bazai cikaba har sai yasowa makocinsa abinda yake sowa kansa, awani hadisin kuma yace duk wanda yayi imani da Allah da ranar karshe to kada ya cutar da makocinsa,cikin wani hadisin kuma yace Duk wanda makocinsa bai amince da amanarsa ba to bazai shiga aljannah ba_,amma mutane basa bawa makota hakkinsu, yanzu mutane sun kasance masu son kawunansu masu cutar da makotansu, alhalin da akwai matar da tashiga wuta bayan tana kwana tana salla kuma tana wuni da azumi abakinta amma lokacin data rasu sai annabi yace tana gidan wuta saboda tana cutar da makotanta"
Zaro ido goodness tayi ita dai idan jabir yana bata ire iren wadannan labaran har bata son ya daina domin dadi suke yi mata,
"Abbu ka sake koya min yadda ake yin wankan nan, anjima zanje inyi"
"To muslima" yafada da niyyar tsokanarta, batace komai ba illa dan murmushi da tayi,
"Farko dai ana so ka tanadi ruwanka mai tsarki wanda bai canja kala ba sannan kuma bai canja dandano ba, sai ki tsiyayi ruwan ki wanke hannuwanki sau uku sannan sai kiyi tsarki ki tabbatar kin wanke ko ina inda kike tunanin jinin ya taba, daga nan sai kiyi alwala amma sau daya daya ba sau ukuba sai dai ba zaki wanke kafafunki ba a iya shafar kunnuwa zaki tsaya, daga nan sai ki wanke gashin kanki sau uku amma ga ita mace anfi son ruwan ya ratsa har can karkashin gashinta, ana son ko ina ya samu, sai ki wanke fuskarki zuwa wuyanki shima sau uku daga nan sai ki wanke barinki nadama wasu malaman sunce daga kafada zuwa saman mazaunai za a wanke na barin dama sannan akoma barin hagu ayi haka sai asake dawowa barin dama awanke daga kan mazaunai zuwa agara sannan akoma bangaren hagu nanma awanke duk sau uku uku sai a game dukkan jiki da ruwa awanke kafafuwa wato karashen alwalar da aka faro daga farko, amma wasu malaman kuma sunce idan anzo wanke barin dama to daga kafada zuwa agara ne za awanke sau uku sannan sai akoma barin hagu shima ayi masa haka sai kuma agame dukkan jiki da ruwa sai awanke kafafuwa amma yana dakyau arinka tsettsefe yan yatsu domin ruwa bai cika shiga wurinba sosai, wannan shine siffar wankan,sannan basai lallai an tsefe gashin kai ba malamai sunce ko gashin kan mace akitse yake to zata iya yin wankan ahaka kawai dai abin bukata shine ta tabbatar ta kwarara ruwa agashin kanta yanda ruwan zai tabo har can karkashin gashin, amma ga macen data gama al'ada to yana dakyau tayi amfani da turaren almiski da ganyen magarya domin tsaftace jikinta hakan sunnace domin Nana A'isha ta kasance tana aikata hakan duk lokacin data kammala jinin al'ada haka kuma idan kinyi wankan ne kafin faduwar rana to sallar azahar da la'asar suna kanki idan kuma sai bayan faduwar rana kikayi to wajibine ki sallaci sallar mangariba da isha'i"
"Nagode abbu bari natashi naje nagani amma indai banga jininba ai shikenan ko?"
Kai ya girgiza mata yana jan dan yatsanta guda daya,
"Har wannan mai kalar ruwan kasa kasan ko kuma yelo dinnan shima indai kin ganshi to zaki bashi hukuncin jinin al'ada ne domin jinin ne yake saba kala akarshen al'adar, domin fadin Nana A'isha uwar mumunai Allah ya kara mata yarda tace sun kasance suna daukar wannan ruwan mai fatsi fatsi a matsayin jinin al'alda mutukar suka ganshi alokacin al'adarsu haka kuma basa yin wanka har sai sunga farin ruwa mai kamar farar kasa ya bayyana"
Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi domin jabir tako ina yayi kuma yasan abubuwa da dama wadanda suka shafi mata kai kace su ya karanta ma gaba daya,
"To bari naje nadawo" tafada tareda tashi ta tafi part dinta, binta yayi da murmushi yana mai jin wani yanayi agame da ita.
Kullum suna tare yana koya mata karatun alqur'ani ko kuma yana bata kissar annabi Muhammad (S.A.W) domin littafin sira ya samo mata yake koyar da ita akowanne dare, amma har yanzu bashida niyyar kulata irin kulawar da miji yake yiwa matarsa domin so yake yaga ta fahinci addini sosai sannan ta sake sakewa dashi gudun kar yaje ko har yanzu tana tsoronshi yasan hakan zai iya haifar mata da illa.
Yau ta kama ranar Monday dan haka da azuminsa ya tashi, ita goodness bata saniba dan haka taje ta shiryo masa breakfast mai lafiya,
Acikin bedroom dinshi ta tarar dashi yana kwance gashi kuma yau zai koma office, daga shi sai dogon wandon bacci ko riga babu ajikinsa,
Gaban gadon taje tayi kneel down agabanshi ta saitinshi ta soma mika masa littafin larabcin dake hanunta,
"Abbu tuna min sunan wadannan abubuwan namanta"
Karbar littafin yayi,
"Yadun hannu, rajlun kafa, uzunun kunne, ainun ido, anfun hanci, fammun baki"
Littafin ya mika mata yana gyara kwanciyarsa,
"Yawwa abbu nagane, yadun hannu ko?" Sai takamo hannunsa takama sannan tasaki,
"Um rajlun kuma kafa ko?" Kafarsa takoma takama ta shafi tafin kafarsa,
"Sai uznun kunne, abbu wannan?" Kunnensa ta kamo tana tambayarsa, kai ya daga mata yana kallonta gaba daya wani iri yake ji,
"Abbu ainun kuma ido ko?" Ji yayi tana shafar idonshi daya, kafin ya farga har ta cafko hancinsa,
"Anfun kuma hanci, yehhh gashi abbu dama Kanada dogon hanci"
Hannunta ya rike, "binti ki bari mana, azumifa nake yi"
Dariya tayi "Allah abbu yau bazan bariba tunda Kaine kace min duk karatun duniya in andorawa mutum to da practical yafi tafiya"
Kafin ya lalubo amsar da zai bata ta haye jikinsa tana cewa "fammun baki" caraf ta cafki bakinsa cikin nata, hmmm su malam jabir koya lafiyar wannan azumi? Umm pherty Xarah ko kinada amsa ne kibani?
_Gaisuwa babba gareku masoya masu karanta wannan littafin na wani haske._
_*Ummi Shatu*_ππ»
[10/19, 5:48 PM] βͺ+234 903 993 4050β¬: [10/9, 8:01 AM] Ummi A'ishaππ»: *WANI HASKE*
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_101-105_
_Assalamu alaikum masoya masu karanta littafin wani haske kuyi hakuri da rashin ganin posting akan lokaci wannan ya farune ta sanadiyyar wasu hidimomi da suka hau kaina sannan kuma kun san wannan littafin abubuwan da suke cikinsa sun shafi bincike da nazari shiyasa zakuga wani lokacin nadade banyi posting ba, yanzunma korafe korafenku naji shiyasa kawai na rubuto muku abinda ya sawwaka amma da a manufata zan kawo muku matsaloline wadanda mata suke fuskanta musamman ma ta fuskar auratayya tsakanininsu da mazajensu da kuma hanyoyin warwaresu to amma jin korafin naku yayi yawa yasa na ajiye wannan batun agefe saboda naji wasu na cewa ummi ta fiya jan rai akan wannan book din, to kuyi hakuri wlh ba jan rai bane yanayin rubutun ne haka, sannan kuma wata baiwar Allah tace ya kamata yanzu adaina kiran tauraruwar littafin da goodness tunda ta musulunta ana kiranta da bahijjanta, dan haka yanzu bahijja zakuji ina ambata, wannan Shafin nabayar dashi kyauta ga duk wata masoyiyar wani haske._
~~~Duk iya kokarinshi na ganin ya hanata aikata abinda tayi niyya kasawa yayi dolenshi haka ya rabuda ita taci gaba da yin yanda take so da bakinsa, rungumeshi tayi tana murmushi,
"Abbu yau bazakaje office ba ko?" Ta tambayeshi tana shafar sajensa, bude idonshi yayi yana kallonta kafin ya bata amsa wayarsa dake ajiye akan bedside drewar tafara vibration, hannu ya mika ya dauko ya duba mai kiran nasa,secretary dinsa ne na office dinsa dan haka yayi saurin dagawa domin yasan tunda ya kirashi to muhimmin abu zai sanar dashi,
Asanyayenshi ya daga wayar bayan sun gaisa yake sanar dashi bakin da zasu zo wurinshi anjima domin tattaunawa akan wata kwangila da zasu samu, wayar ya kashe yana tunanin dole yayi saurin fita zuwa office before bakin nasa su zo,
"Dagani naje nayi wanka" yace da ita yana kallon yar kyakkyawar jar rigar dake jikinta mai yalo yalo marar nauyi,
"Abbu kana yin azumin ko? Bayan kuma na yi maka breakfast, ni wlh bazan yarda ba" tafada cikeda shagwaba,
"Binti ai nafasa yin azumin tunda kin rigada kin bata min shi, idan nayi wanka yanzu zanci duk abinda kika girka min"
Wani tsalle ta daka ajikinsa tana murna, "yawwa abbu ko kaifa"
Murmushi yayi ya tashi zaune har lokacin tana kan cinyarsa azaune, kallo yabita dashi acikin zuciyarsa yana cewa "ai kuwa zaki sani tunda kika karya min azumina"
Hannunshi ta kama tana kallon fuskarshi "abbu inje in hada maka ruwan wankan"
"Uhm" yafada ahankali, wani tsalle ta dira ta sauka ta nufi toilet din yayinda shikuma yabita da kallo har yanzu akwai kuruciya da yarinta a tattare da ita,
Tana ciki tana sirka masa ruwan zafin data tara acikin wani babban baho ya turo kofa ya shigo cikin bathroom din, juyawa tayi ta kalleshi sai ta ganshi da dan gajeren wando, da saurinta ta juya wadda har tana kokarin fadawa cikin bahon ruwan zafin bata sani ba,
Da saurinshi ya rikota ta fada jikinshi ya riketa,
"Binti wannan gangancin fa? Saura kadan ki fada cikin ruwan zafi" yafada ahankali yana rikeda ita,
"Abbu gashinan kayi wankan, bari naje na gyara maka dakinka kafin ka fito" tafada tana mai sake rufe idanuwanta,
"Kitsaya binti, ai tare zamu yi wankan yau, ko bakya son ki samu lada?" Bude idonta tafara yi cikin sauri tareda yunkurin raba jikinta da nasa,
"Abbu kayi hakuri dan Allah, nidai wlh bazan iyaba kunyarka nakeji"
Dan murmushi yayi mai kayatarwa gamida dafa bangon bathroom din da hannuwanshi yayi mata runfa tana jingine ajikin bango tana neman hanyar guduwa,
"Ai kema wasa kike yi yarinya, ki karya min azumin nawa sannan kuma kice ba za muyi wanka tare ba, binti ladafa zaki samu domin babu abinda yafi kyautatawa miji saurin samun lada, duk umarnin da na baki muddin kika bishi to lada zaki samu, idan kika yimin wani abu wanda ya sani farin ciki shima lada zaki samu..!"
"Abbu wlh zaka makara a office gashi ana can anata jiranka"
Kallonta yayi yana sake bude manyan idanuwansa yana kallonta, fuskarta ya zubawa ido yana kallonta amma ita takasa kallonshi idonta yana kasa,
"Binti kinga, dago idonki ki kalleni"
Kasa dagowa tayi har lokacin kasa take kallo, hancinta ya lakuce "wannan yarinyar kin fiya wayo da yawa"
Ruwan da yake zuba acikin bahonne yafara zuba akasa domin bahon tuni ya dade da cika,
"Tunda kin ki yin abinda nasaki shikenan bari nayi ni daya kafin amaryata tazo munayi tare"
Juyawa yayi yaje gaban fanfon yafara kashe ruwan da yake zuba,
Ahankali bahijja ta bude kofar bathroom din tafita, agaban mirror ta tsaya tana tunani aranta, tunanin maganar da jabir ya fada mata yanzu take yi indai kuwa hakane amma da tasan sunanta gawa domin ayanda take jin zuciyarta gani take yi indai ya kara aure yanzu to babu makawa mutuwa zata yi, lallai Ummu al'amin tayi kokari gamida juriya data iya barinta ta zama kishiyarta,
Bata taba sanin kishi yanada daci ba sai yanzu da take auren jabir, kasa gyara dakin tayi tana tsaye har lokacin tana juya maganar da jabir yafada mata acikin kwanyarta, har jabir yayi wankan ya fito ya sameta tsaye agaban mirror wadda ita bata ma san yafito daga wankan ba,
Kafadunta ya dafa da duka hannuwanshi guda biyu sai alokacin ta dawo hayyacinta a sanadiyyar sanyin ruwan da taji ajikinta,
"Me kike tunani ne binti?"
Fuskarta ta shagwabe ta turo baki tana son yin kwalla,
"Abbu ba kaine ba kace...!"
Sai kuma tayi shiru,
"Nace me? Fadi inji, me nace?" Ya tambayeta yana kokarin juyo da ita,
"Kaine kace wai, wai, wai...!"
Hawayen idonta ne suka silalo kan kuncinta, hakan yasashi bude baki yana kallonta cikeda mamaki domin bai san abinda yafaru ba,
"Binti me nace? Yi shiru ki fada min kinji"
Kamar ya zugata sai tafashe da kuka tareda fadawa kirjinsa, rungumeta yayi ya fara shafa gashin kanta,
"Binti idan baki fada min ba wa zaki fadawa wanda yafini? Ni yafi cancanta da ki sanarwa da dukkan damuwarki"
"Abbu kaine kace wai idan amaryarka tazo, wai, wai, wai tare zaku nayin wanka" tana gama fadin haka ta boye fuskarta acikin kirjinsa, dariya sosai maganarta ta bawa jabir domin shi yayi tsammanin wani abune muhimmi tunda yaga harda kuka tayi,
"Yanzu binti wannan maganar kike yiwa kuka? Ohhh, nifa nayi zaton wani abune babba yasaki kuka, kishiyar kike yiwa kuka? So kike ta rainaki tun kafin tazo kenan"
"Abbu dagaske kake?"
Kanta ya shafa yana murmushi wanda har hakoransa sai da suka fito, kanta ya dago yana kallonta,
"Wasa ne binti, bada gaske nake yi ba dawasa ne amma indai bakya bani kyakkyawar kulawa to zan yimiki abinda bakya so, indai bazaki rinka bani farin cikiba to zanyi miki kishiya"
"Abbu dan Allah kayi hakuri Allah bazan sakeba" tafada idonta narai narai tana kokarin sake yin wani hawayen,
"Shikenan nahakura, karki sake yin kuka kinji, maza kije ki kawo min breakfast din kafin na shirya"
Sakinta yayi yana yi mata lallausan murmushi, fita tayi tabarshi yafara shiryawa ita kuma ta nufi sashenta, kwanuka masu tsafta ta dauko ta zubo masa doya da kwan data soya masa ga dan farfesun kayan ciki agefe sannan ga custard powder data dama sai tea wanda yasha kayan kamshi aciki,
Kinkimar kayan tayi ta kai masa falonshi ta ajiye sannan tabishi cikin dakin, lokacin data shiga har ya gama shiryawa cikin wani bakin danyen boyel mai kyau dakin gaba daya ya gauraye da kamshin turarensa mai dadi na special oud.
Acan wurin da ya kebe domin gudanar da ibadarsa ta hangoshi yana sallar walaha, tsayawa tayi ta zuba masa ido tana kallon shi hakika yayi mata kyau domin gayunshi ya burgeta mutuka, tun daga hular kansa har agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa duk kalar kayansa ne, tana nan tsaye tasaka zaren gabar rigarta abakinta tana wasa dashi har ya idar yayi addu'a yatashi ya nufo inda take tsaye tana jiransa, gabanta ya karaso ya tsaya, hannunsa yasa yana kokarin zare zaren dake bakinta tana wasa dashi da hakorinta,
"Binti abin riga kike ci? Kalleki kamar wata baby"
Kallonsa tayi tana murmushi "abbu kayi kyau sosai"
"Nagode binti, yau yarintar ce ta motsa?" Yafada yana lakuce hancinta,
Murmushi tayi taja hannunsa tana kallonsa, "abbu muje kayi breakfast, bana son ka makara azuwa office"
Bin bayanta yayi har suka isa wurin da takalmansa ke jere reras, wani bakin takalmi ta dauko masa na fata half cover mai kyau, ajiye mishi tayi agabansa,
Falo suka nufa bayan yasaka takalmin, akan kujera ya zauna ta jawo masa dan karamin stool ta ajiye masa abincin akai tana kallonsa,
"Binti wannan girkin naki ai sai yasa kunnena ya cire" yafada daidai lokacin da yafara cin doyar data soya masa,
"Abbu banda tsokana fa" tafada tana murmushi,
"Babu wani tsokana binti, abincin yayi dadi gashi naga harda wani koko koko, kunu kunu kika hada min"
Murmushi tayi tana tafa hannunta "lah jama'a kunji abbu bai san custard powder ba, amma abbu idan akaji dariya za ayi maka"
"To ai gashinan kin fara yimin dariyar"
Hannunsa ta riko na hagu, "abbu bari na gyara maka agogonka"
Agogon ta kunce ta sake daura masa tana murmushi koda ta gama daura masa bata saki hannun nasa ba yan yatsunta tafara ja tana lankwasa masa su suna kara kas kas,
"Binti kema kin iya mugunta ko?"
"Abbu me nayi maka? Daga gyara?"
Mikewa yayi yana murmushi aranshi yana burin wani lokaci da yake hasashen zuwansa a daren yau,
"Bari naje binti"
"Abbu, Allah ya kiyaye hanya, Allah ya bada sa'a" tafada tana kallonsa
"Amin binti" yafada tareda jan hancinta saboda ganin idonta ya fara kokarin kawo kwalla,
"Meyasa bakya gajiya da kuka ne? Ki rage saurin