A Duniyata Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Huguma Category :  Complete Novels

Chapter   89 / 119

264K to 267K   out of 356.9K words

don mutum ba" Ya qarasa fada yana jifan fu'ad da harara wanda yayi relax abinsa jikin kujera kaman badashi yake ba.

Miqewa tayi da zummar basu guri.

"Kin gama ne?" Ya fada muryarsa can qasan maqoshi. Kai ta girgiza tana satar kallon farouq tana masa alama dashi. Ya fahimci me take nufi amma ya basar,don haka ta buda baki.

"Zanyi waya dasu huda kafin ku kammala". Agogo ya kalla da narkakkun idanunsa.

" Minti goma ki dawo ki qarasamin"

"Okay sir" Ta fada a girmame ta qarasa tana daukan wayarta ta fice.

Farouq bai jira ta kammala fita din bama ya soma fesar da abinda ke ransa.

"Zuwa nayi na maka sallama". Dariya ya taso ma fu'ad amma ya danneta,sai ya miqe sosai ya zauna yana ware idanunsa akan farouq

"Ina zaka kuma?"

"Gida zanje ayimin aure.....bazan zauna na mutu na tashi a gafiyar lahira ba". Wannan karon dariya ta gasken gaske ya bawa fu'ad,har wanda ke parlor din zai iya jin sautinta,kalan dariyar daya jima rabonshi da irinta.

"Bafa inda zakaje dude.....ko zaka hadiyi zuciya saika gama jinyata ka cikasa ladanka".

"Lada irin naka ne banaso......ina samun ladanka kaima kana samun naka ladan ko?....bazan iya ba....ni yanzu wallahi kafi qarfina" Kai ya jinjina yana shafa sumarsa. Da gaske yasan farouq aure yakeso.....kuma koda shine yake a matsayin farouq din yana sanya auren mace kaman sabreen bayajin zai iya haqurin da yayi ma.......baiga abinda zaiwa farouq ba sama daya tabbatar da aurensu a daidai date din da aka saka.....baya jin zai yarda ya zama silar daga bikin farouq koda na kwana daya ne.

"Ka yiwa pilot nassar magana......ayi booking barinmu taiwan zuwa Nigeria.......inaso larabar nan mu koma gida". Waiwayowa farouq yayi yana kallonsa da mamaki.

"Ina zakaje kana jinya?,ina zakaje bincike kuma bai kammalu ba?". Murmushi ya saki me taushi yana duban farouq din,duba irin na 'yan uwantaka ta jini me cike da dumbin qauna.

"Bincike ya gama kammala farouq......fareeda keda alhakin komai......ta samu nasarar aiwatar da komai dinne ta silar maamah data bata full details din......abu daya da ban sani ba shine.....bata da masaniyar abinda fareeda zatayi dashi?,ko tana da masaniya?,tayi hakanne dukka cikin tsare tsarenta data dauki shekara da shekaru tana gudanarwa?" Ya qarasa maganar duk wata walwala da yake ciki tana sulalewa daga jikinsa. Ba farouq kadai ba,hatta sabreen data dawo da niyyar daukan slipper dinta ta zagaya koda veranda din dakunan saita tsaya tana komawa da baya. Wani irin tausayinsa yana sasuqar zuciyarta. Yadda walwala tayi qaura daga fuskarsa karo daya ya tabbatar mata a yanzu a rayuwarsa bashi da sauran wani ciwo daya wuce MAHAIFIYARSA. A jikinta ta dinga jin cewa......She has to put in effort to help him overcome his past,ya kamata ta sake matsawa sosai cikin rayuwarsa.....yana buqatarta fiye da yadda take hasashen zai kasance.

"No dude.....no.....kada kayi wannan tunanin.....ko yaya ne.....ko yaya kuke da maamah uwa ce.....bana tunanin kowanne kalan hali ne da ita zata iya bada qofa ko daman rabaka da rayuwarka". Idanunsa da suka sauya kala ya maida kan farouq yana dubansa.

"Farouq.....duk yadda zan gaya maka abinda ke nan gurin..." Yayi nuni da qirjinsa da yatsansa.

".....ba zaka fahimta ba.......mun rasa MAHAIFIYA.....MUN RASATA RASHI NA HAR ABADA......saidai na yadda nayi kuma imani,yana cikin rashin cikar kamalar ni'imar mutum cikin DUNIYARSA......cikakkiyar ni'ima tana lahira".

"Duk da haka dude please......ka ajiye wannan a side"

"Na ajiye farouq......fareeda zata girbi duk abinda ta jima tana shukawa.....she must pay.....bawai iya kaina kawai ba". Kai farouq ya jinjina,wani aikine daya shirya gudanarwa da kansa,sai gashi fu'ad din ya rigashi.

"But dude.....inaga kaman ka qarasa warkewa....."

"Noooooo......dole farouq dina ya shiga qwaryar manya as soon as possible.....ta iya yiwuwa ya rage zargina.....ta iya yuwuwa kuma ya daina katsemin muhimman lokuta na da DUNIYATA". fuskewa farouq din yayi yana sosa kanshi

"Eh to.....kaman tafiyanma zaifi mana Alkhairi gaba daya.....don bana tunanin idan ka zauna a nan dinma warkewar arziqi zakayi,gadon ya muku kadan gwara a koma gadon gida". Toshe bakinta sabreen tayi,salin alin ta debi kayan kunyarta taja jikinta tana barin gurin tun wani a cikinsu bai ganta ba.

β˜…Salati drivern ya saki,hannuwansa bisa saman kansa yana sake sakin salatin gami da cewa.

"Ku kawo dauki bayin Allah......hajiya ta zube". Dukka hankalin ma'aikatan gidan ya tattaru a kanta,saidai har matan ciki tsoro da shayin dagata suke,basusan haqiqanin abinda zai biyo baya ba idan suka dagata bayan ta farka.

"Dole haka za'a ceci ranta,kome zai biyo baya ai ba za'a barta ta mutu ba ko?". Malam sa'adu me gadi ya fada.

"Matso ke raliya ki kama musu ita" Ya fadi yana matsawa baya.

"Gashi ba kowa gidan Alhaji hamza ballantana muji ina ake kaita" Malam sa'ad ya fada yana duban driver din.

"Kowanne asibiti ma kaita za'a yi tunda abune na gaggawa.....ki shigo mu tafi" Yace da raliya yana shigewa cikin motar.

Tuqi yake a gaggauce yana tsoron kada ta mace a hannunsa,babar babban mutum irin me jadda ta mutu a hannunsa tabbas ba qaramin tashin hankali bane.

Tafiyar minti shabiyar suka samu wani private suka tsaya a nan,aka dauko wheelchair aka dauketa akai,har a sannan bata dawo daidai ba.

Sai da suka kashe minti kusan sha biyar a kanta sannna ta farfado,suka cire mata oxygen suka daura mata ruwa da suke saka ran minti talatin ya qare sannan likitan yace zaije ya dawo kafin ruwan ya qare.

Kanta kawai take mirginawa tana jin qirjinta yana mata wani ciwo,duk inda ta juya fuskar raliya data drivernta kadai take gani,har bacci ya saceta.

Still data farka din ba wasu sabbin fuskokin saisu din dai. Wani abu ya tsaye mata a wuya,wasa wasa tana shirin kamanceceniya da tsintacciyar magen da bata da wani gata. A hankali ta sauke dubanta kan wata mata dake kusa da gadonta,wanda su biyu ne kacal dama a dakin. Yara hudu ne tsaye a kanta,tana zaune saman gadon,daya a hannun damanta.....daya a hagunta,dayan yana tsaye saman kanta yana bare mata ayaba yana bata tana ci,dayar tana saman kujera gaban gadon nata riqe da robar yoghurt tana jira ya gama bata ta miqa mata.

Hira suke a tsakaninsu,kowanne fuskarsa dauke da walwala duk da cewa jinyar mahaifiyarsu sukeyi. Tana gama ci ya karbi bawon ya jefa a Dutsbin,zai karba yogurt din daga hannun ta zaunen ta hanashi.

"Saika kwashe ladan duk kai kadai,nima inaso" Ta fada tana kai roban bakin mahaifiyartasu.

Idanu maamah ta dauke tana runtse idonta,wani irin bacin rai yana ratsata. Tasan koda kwatar kwatar kwatar kudin fu'ad duka yaran matar basu kai ba.....amma yadda suke tattalinta da nuna mata qauna da kulawa kadai abun kallo ne.....ita gata ta qare da zama 'yar kallo,cikin rayuwar kadaici da rashin wani sashe da zai tallafeka.

"Allah ya isa ameenatu.....Allah ya isa" Ta fada a sarari tana ji har zuciyarta anni ta mata cutar da bazata taba iya wankuwa daga ranta ba.....hakanan kowacce kalar fansa data shirya dauka ba zata iya ramawa daidai da abinda tayi mata ba.

Daga raliya har driver din da kallo suka bita,saidai babu bakin magana,daidai nan likitan ya shigo.

"Ta farka ko?" Ya fada cikin kulawa yana dauko file din gami da sake duba abinda ya rubuta,ya qara wasu rubuce rubucen sannan ya ajiyeshi yana dubanta.

"Hajiya ki rage saka bacin rai a zuciyarki.....ki rage saka damuwa a ranki,kina da hawan jini bai kamata ki dinga zama cikin damuwa ba.......irin wannan gaskiya yana iya haifar da matsala kala kala,ba'ason abinda zai dinga sanyawa jinin yana hawa haka ta farat daya....kuyi qoqarin ganin ta kiyaye" Ya qarasa maganar yana dubansu raliya ganin maamah din taja idanunta abinta ta kulle.

"Tom.....in sha Allah" Raliya ta fada a sanyaye a ranta tana cewa mu asuwa?,indai taji da kunnenta ai shikenan mun kubuta.

"Kuna iya tafiya gida.....amma da zarar taji wani abu daban ayi hanzarin dawowa,saboda yanzun takai matakin da dole a dinga yawa checking up nata".

"Mun gode likita" Driver ya fada bayan ya karbi takardar magungunan daya rubuta mata.

Yana shirin tada motar ya dan waiwayo

"Ya za'a yi da magungunan nan hajjaju?,zamu siya ne a hanya ko za'a kawo?".

"Kai sagiru" Maamah dake a qufule da yadda suke jaddada mata cutar hawan jini ta kira sunansa.

"Naam hajiya".

"Ka fita daga ido na......hawan jinin banza hawan jinin wofi?,maqaryatan banza wanda mutum baya ciwon Allah da annabi?,shekarata nawa a duniya hawan jinin bai sameni ba sai yanxu ina fafutukar cika burikana?,Allah ya tsinewa wanda ya fasa cewa ina da hawan jini.......hawan ruwa ne dani.....bani takardar nan nan" Ta fada cikin fada tana miqa masa hannunta.

"Hajiya......ki tsaya ki duba maganarnan,don bakiga yadda kike bane dazu.....bai kamata ki wasa da magani ba....." Kai ta jijjiga.

"Lallai sagiru wuyanka ya isa yanka.....ashe kana dab da rasa aikinka" Ta fada cikin mamakin tsaiwa.musu da yayi da ita.

"Ka bata mana sagiru" Raliya tayi saurin tunasar dashi,salin alin ya miqa mata yana cewa.

"Tuba nake,Allah ya baki haquri".

" Idanma hada baki kukayi dasu saboda ku manna min ciwo ku kasheni to ta Allah ba taku ba.......rayuwa a duniya yanzu na farata,maqi gani ya kauda idonsa" Ta fadi tana yayyaga takardar ta watsar ta window tana cewa

"Muje gida" Tana jin lallai tana buqatar tayi magana da fu'ad da gaske.

Ya gama shirin kwanciya tsaf sanye da pyjamas masu taushi farare qal,yana zaune saman yalwatacciyar sofa yana binta da kallo sanda take qoqarin gyara masa gadon don yaji dadin kwanciya.


"Sabrrrr" Ya kirata da sautin da ya sanya taji tsigar jikinta ta zuba. A nutse ta waiwayo tana kallon lumsassun idanunsa.

"Yau bazan kwanta kan gadon nan ba". Da dan mamaki take kallonsa,kafin takai ga tambayarsa dalili sai musaddiq yayi knocking. Sabreen ta sauka a nutse tana nufan qofan da dan mamaki,don yanzun sukayi sallama dasu zasu wuce gida. Kanshi yadan rusunar yanajin nauyinta da tsoron kada hamman ya fatattakoshi.

"Maamah keson magana da hamma" Ya fada yana miqa mata wayarsa. Bin wayar tayi da kallo kafin ta matsa tana baiwa musaddiq hanya. Dubanta yayi saita daga masa kai alamun ya shige,a sanyaye yake takawa ciki itama tabi bayansa da nufin gama gyara gadon ta fita ta bashi waje don ya samu amsa wayar sosai.

Wani yawu musaddiq ya hadiye yana duban hamman nasa daya tsareshi da ido.

"Maamah ce tace lallai na kawo......" Hannu ya daga masa yana amsar wayar,sai ya miqa masa yana fita daga dakin a gaggauce yana jin bazai iya jiran ma ya gama amsa wayar ba ya karba sa hadu gobe,don haka kai tsaye ya wuce inda cab ke jiransa.

Handsfree ya sanya wayar,ya kuma ajiyeta a gabansa kawai yana zuba mata idanu,irin yadda yakeyi idan ranshi yana bace kuma baya da buqatar amsa wani kiran amma tilas ta sakashi amsawa.

"Ina kyautata zaton kana jina?,ko yanzun ma 'yar mulkin taka ce ta daga kiran?" Tayi maganar da wata irin hasala da fusata.

"Muhammad fu'ad jadda ne" Ya amsa mata da wani irin nutsuwa yana zubawa sabreen ido wadda ka ta ke duqe tana gyara bedsheet din gadon da pillow case din.

"Naji dadin jin hakan......umarni ne daga uwa zuwa shashan danta wanda baisan inda yake masa ciwo ba.........ka kama dukiyar mahaifin yarinyar dake mutuwar sonka ka garqame.....ka masa sanadin aikinsa duka saboda kana hannuwan mutanen da suke riqe da ragamar rayuwarka......sai abinda suka ce.....ni mariya dana dauki cikinka daga gudan jini har zuwa tsoka.....harka zama mutum.....saboda lalurar rayuwa ta nesantani daku shikenan yanzun nice wulaqantatta a wajenka......to indai nice mahaifiyarka ina baka umarni cikin qasa da awa daya komai na ambassador khaled ya koma kan aiki daidai".

"Tom" Kawai yace da ita yana sanya dukkanin wani qarfi na qwanjinsa dana ruhinsa yana danne zuciyarsa. Wasu irin abubuwa ke taso masa......yana rantsuwa da ubangijin ka'aba......banda da gaske ya ratsa jikin maamah ya bullo zuwa cikin duniyar da yake rayuwa a yanzu a cikinta......babu wani halitta kaf duniya daya isa yayi masa quarter quarter abinda tayi masa a yanzun. Hannunsa yake mutstsukawa yatsunsa suna wani irin qara,yana jin wadannan mutanen guda biyu sun fara kai masa ko ina a rayuwarsa.

Kunnuwanta ne taji ba zasu iya dauke maganan maamah din ba,saita saki gyaran gadon ta soma nufar qofa tana takawa a gaggauce.

"Sabreen.....dawo" Ya fadi kansa tsaye ba tare daya damu maamah zata iya ji ba.

"Ina magana da kai kana kiramin sunan wannan yarinyar?,annamimiyar karu....." Ya riga ya shanshano abinda take da muradin fada,sai kawai ya sanya hannunsa da wani irin zafi ya datse kiran yana kashe wayar gaba daya.

Da gaske wani irin abu sabreen keji,wani yanayi taji yana tsarga mata,ba zata iya zama ba da gaske,ba zata iya jura ba.....don haka ta sake takawa zata fita,sai kawai ya sanya hannunsa me ciwon dake nade ya fusgota sai gata ta fado zuwa jikinsa yasa hannuwansa duka biyun ya lullubeta cikin qirjinsa kaman ya manta ko baisan ciwon dake hannunsa ba ko kuma wani sassauqan rauni ne da bashi da radadi ko zafi ko kadan.

A zafafe yake kiran wata number,tsoronsa a karon farko ya kamata ganin yadda numfashinsa yake fita da sauri,zuciyarsa na wani irin bugawa.

"Haka fushinsa yake?" Ta tambayi kanta da kanta,daidai sanda kiran ya shiga aka daga. Ko muryar dake wancan bangaren bata jiba ya soma sauke musu umarni.

"Inaso a daren yau basai gobe ba.....fareeda khaleed mustapha ta kwana a a cell......ba ita kadai ba,da duk wanda ya kawo wargi ko yunqurin hana fita da ita" Abinda yace kawai kenan yayi wurgi da wayar.

Matseta yayi so sai a jikinsa,yana daga idanunsa da suka kada suka sauya launi yana zubesu cikin nata......


_tofa.....ran 'yan maza ya baci.....an manta da ciwon da ake jinya......ko sabreen zatayi aikinta?🫣,zamu gani_



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862



𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 133


*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*


*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*


*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*

*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*

*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*

*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*

*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*

*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*

*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*

*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*

*_HAIHUWA KIKAYI?_*

*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*

*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*

_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_

08104553105
08127084190

*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*


*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*



133


Sasai taji wani abu yana ratsa jinin jikinta game dashi......wani narkakken tausayinsa yana taso mata yana kuma mamaye ilahirin jikinta. Ta yarda dari har bisa dari cewa......da uwa irin maamah gwara ka rayu cikin maraici......da uwa irin maamah gwara ka zamana cikin layin yaran nan da ko dumin iyayensu basuji ba ubangiji ya karbi rayukansu......ta sake yarda da cewa.....komai ubangiji ya tsarawa bawa tabbas akwai manufa da alkhairi a ciki.

"Ya zakayi haka?" Ta fada tana sake saka idonta cikin nasa sosai tana kuma riqe da fuskarsa cikin tafukan hannayenta. Kaman wanda yasha wani abu ya maku yake magana

"Ya bazanyi haka ba.....ta yaya zanyi wasa da duniyata?.....ta yaya zan bari a taba duniyata?" Numfashi taja me zurfi wanda ya shige jikinta da wani irin mahaukacin sonsa da kowacce safiya yake qaruwa cikin ruhinta,ta sake bude idonta a kansa tana kallonsa.

Taga abubuwa da yawa cikin idanunsa......giyar soyayya da qauna.....da kuma wani irin fushi. Ji tayi kaman bata da wani sauran aiki daya rage mata a duniya a yanzun banda ta kwaranyar da wannan fushin da kuma damuwar daga wannan ruhin daya gama macewa a soyayyarta. Ba zato ba kuma tsammani yaji ta hade bakunansu guri guda.

Wani irin zazzafan kiss ta soma ajiye masa kafin ta tura harshensa cikin bakinsa ta soma sarrafashi kaman yadda yake mata. Cikin qasa da second biyu kowacce wuta dake jikinsa ta dauke,ya soma kokawar qwato numfashinsa,wanda bata daga masa qafa ba ta fara aike masa da qarin wasu saqonnin da suka birkitashi......suka sakashi ya soma mance wayeshi?,a wacce DUNIYAR yake?,meye matsalarsa a rayuwama gaba daya?.

Tayi masa ba zata ta qarshen qarshe......ta kuma tashi kansa da wasu irin zafafan salon da suka saka har ya manta meye ma yakeyi?. Wani irin saqo take aike masa me cike da jan rai......sai taji ya gaza jurewa ya juyeta ya maidata qasa.

Nutsuwarta taso maidawa jikinta,ta dafe qirjinsa a sanda yayi mata rumfa tana kallon narkakun idanunsa da suka sauya launi. Dubanta yayi shima yana neman qarin bayani,saita masa nuni da hannusa me ciwo da ya dafesu ya aza masa nauyi kaman ya manta yana da rauni.

"Kina tsoron jini ne?" Ya tambayeta ha tare daya kalli inda take nuna masa din ba. Fuska tadan bata daban,ta sani ba'a fiya son yayi wani aiki sosai da hannun ba,saboda a samu ya warke da wuri.....kuma wannan fitinar da yakeso yayin tabbas zata iya maida ciwon danye.

"Alright" Ya fadi da hanzari cikin qasa da second

89 / 119