Author : Huguma Category : Complete Novels
sanyata a idanunsa ba,suna dakin annin ita da amna. Bazaice ga abinda sukeyi ba,amma lokaci lokaci yana jin muryar amnan da motsinsu,ita kanta amnan bata sake fitowa ba. Ita da amna suna seat din kusa da juna,kaman magana suke qasa qasa,baka iya ji saboda musaddiq da saddiq da suka cika gurin da musunsu da bai gane ma akan meye suke musun ba.
Kaman wadda aka umarta,nata fararen idanun da a kwanakin yaga kaman sun qara girma ta daga ta watsa masa cikin rashin sanin shi dinne ya is wajen. Qwayoyin idanunsu suka gauraye da wani irin mabanbantan feeling. Da sauri ta janye qwayar idonta yayin da nata kallon a gareshi ya zame masa kamar wani irin dafi daya sabbabba mutuwar dukkan wasu gabbai a jikinsa. Tsigar jikinsa ta zuba sanda ta soma motsa wadannan siraran lips din nata tana tauna Chip's din dake gabanta. Bazai taba manta abinda yaji daga kowanne sashe na jikinsa ba a ranar farko daya soma tsotsar tausasan lips dinta ba......wani mahaukacin saqo da suka aike masa da baisan inda zai iya adana yawansu a kwanyarsa ba. Yanzun da take juyasu tana tauna sai ya zamana tamkar tsokanarsa takeyi haka yakeji tana aika saqo kowanne sassa na jikinsa.
Fitowarsa ya sassauta tashin muryar saddiq da musaddiq din,kowa ya maida hankalinsa jikinsa,kasancewar sunsanshi mutum ne da baison ire iren musunnan nasa. Yakance
"Shashanci ne wannan,kuna da abubuwan yi da yawa a gabanku cikin rayuwarku,shi ya kamata ku fuskata" Sau tari musaddiq yakanyi dariya idan bai wajen
"Shifa hamma ya dauka kowa irinsa ne.....ba baki nayi mana ba,amma ba zamu iya achieving abinda yayi achieving ba.....we are doing the best,amma ba zamuyi kaman nasa ba". Kujerar dake opposite dintata ya zauna,sam table din baida fadi sosai,wannan yana iya sawa idan ka zura jiki da yawa gwiwarka ta iya taba ta abokin zamanka.
Zamansa a wajen sai taji kaman gaba daya ya cika wajen.....kwarjininsa da qamshin sassanyan turarensa gaba daya ya gauraye wajen. Nauyin idanuwansa takeji har tsakiyar kanta,abinda bata taba ji ba a kansa tsahon tarayyarsu.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 84
_Allah S W T yana cewa "lallai sallah tana hana alfasha da munkari_
_Duk wanda salla bata hanashi qarya ba,zina sabawa iyaye,zuwan gidan boka shirka kenan,cutar da maqota da sauransu,to tabbas ya tuntubi sahihancin sallarsa_
84
"Barka da fitowa hamma" Amna ta fada wadda sun hadu yau kusan sau uku sun riga da sun gaisa already.
"Lovey dovey.....barka da dare" Ya fada cikin wani irin aji kaman me qididdige adadin kalamansa na ranar. Murmurshi amna ta saki qasa qasa.
"Hamma.....kada ka saka adda sabreen taji kishi fa.....sunan nan for now ya kamata ace nata ne". Daga shi har ita nauyi maganan ya musu musamman da anni ke a wajen,wadda tayi burus kaman bataji ba tana qarasa shan black tea dinta. Amnan ya kalla sannan a dabarance ya saci kallon sabreen din. Bayajin akwai wani suna daya cancanci ya kirata dashi......har yanzun duk sunan daya bata sai yaji tafi gaban wannan sunan. Daidai lokacin tana jefawa amna harara da fararen qwayar idanunta ne,wani irin kyau yaga ta sakeyi masa,tsigar jikinsa yaji ta zuba sosai har sai daya lumshe idonsa.
"Ka maida hankalinka fa.....aiki zaka fita kayi" Wani sashe na zuciyarsa ya gaya masa ganin tana neman dagula dukkanin lissafinsa.
"Yi serving hammanku takwarata" Anni data kammala shan tea din ta yiwa sabreen magana. Hakan ya masifar yi masa dadi,sai ya ajiye mug din daya dauko da farko yayi relaxing bayansa jikin kujera yana jin jikinsa yana sake mutuwa gaba daya....wani irin feeling yana taso masa yana sake kashe masa duk wani kuzari nasa.
Sai data ji gabanta ya fadi da anni ta fadi haka,amma dole ta ajiye fork din hannunta ta miqe,fork din yabi da kallo,gaba daya ya gama karantarta,bata qaunar abinci ko kusa ko alama....bayajin zai iya bari taci gaba da hakan,dole ta dinga cin abinci me inganci tana qoshi,bayajin indai zata dinga zama ba abincin kirki zata iya dauke lalurarsa yadda yakeso. Shi kansa wani lokaci yana tsoron kansa,tun a lokacin da yake shi kadai ma.....shi da kansa yasan yana da buqatar mace me juriya kafin ya samu abinda yakeso. Faruwar abunnan kuma ya tabbatar masa sa zarginsa,bai taba kawowa ma zata iya dauke buqatarsa.....duk da abinda ya farun yasan akwai aikin gaggawa da kuma rashin sabo a tattare da ita,amma yasan cewa lallai akwai aiki a gabansa,dole sai ya horar da ita yadda zata dace da muradi da tsarinsa.
Kwata kwata ya mance ya samu farouq a wajen,ya shagala wajen qare mata kallo ta qasan idanunsa. Zaka dauka sam ba ita yake kallo ba,amma kowanne motsi da zatayi idanunshi suna kanta sanda take zuba masa abincin. A cikin qaramin hijab take,amma shi ba hijab yake gani ba,wannan kyakkyawar surar tata yake gani,kyakkyawar surar da yakejin koda zata shekara a yana ganinta zallarta bazai gaji ba......kyakkyawar surar data kusa qwace kowanne tunani tasa,ta kusa sanyashi manta waye muhammad jadda gaba daya. Wani sashe na zuciyarsa dake danqare da mahaukacin kishinta ya soma masa zafi,gani yakeyi musaddiq saddiq da farouq dake zaune a wajen suma suna iya ganin abinda yake gani.....yana jin kamar duka suma qare mata kallo sukeyi.
"Gyara kintsi yallabai.....anni fa na wajen nan kada a tafka abun kunya" Cikin kunnuwansa ya tsinci muryar farouq yana fada. Cikin dakiya ya gyara zamansa yana basarwa,abinda ya kusan sawa farouq ya fashe da dariya.
"Shi yasa ake cewa bawa yaji tsoron Allahnsa koda yaushe" Farouq ya kuma fada sama sama. Tunu fuad ya gama karantar abinda yake fada,so amma yanzun baida energy din kulashi. Hannu yasa don karbar mug din da take miqo masa,cikin dabara ya hade da zara zara yatunta da suka ja hankalinsa sosai,ya kuma motsa hannun nasa yana lullube bayan hannunta da tafin hannunsa.
"Thank you" Ya fada da wani irin sauti can qasan maqoshinsa yana karbar mug din.
Kaman an yarfa mata ruwan sanyi haka taji sanda dumin tafin hannunsa yake ratsa kowacce jijiya ta jikinta,ta koma ta zauna tana jin cikin ta duka ya gama cushewa ta qoshi da chips din,sai ta koma juya cokalin kawai.
Tana jin hirarrakinsu amma ita din ta gaza cewa komai,kaman yadda shima ta fahimci jifa jifa yake cewa wani abu. Kanta da idanunta cikin plate din,ta gagara daga idanunta saboda yadda takejin kowanne motsi nata ita yake kallo,ranta ya dinga baci kadan kadan,wannan wanne irin kallon wuce qa'ida ne?. Ta aje kallo a muhallin mazan bariki,wanda yawancinsu suna amfani da wannan hanyar idan sunso dilmiyar dake su afakaki komarsu.....wannan dalilin ya sanya da wurwuri take qarawa namijin da ya fiya kallon wuta. Amma wannan karon nasa kallon sai taji ya banbanta da nasu,don nashi kashe mata jiki yakeyi,ya kuma aza mata wani kwarjininsa sosai da har yake hanata sakewa.
Tsoro sosai taji sanda taji ana lalubar tafin hannunta ta qasan kujerar. Ta fidda idanu waje tanason fahimtar waye,saidai ya bata haske ta hanyar cewa.
"Miqo min tissue paper dincan please" Da wani narkakkiyar murya. Kallonsa tayi ya kashe mata ido daya,ta janye dubanta da sauri tana tura masa tissue din,ya dauka ya aje gefe yana ci gaba da cin abincinsa tabbacin ba amfani zaiyi da ita ba kenan.
Tana ji tana kuma gani yaci gaba da murxa tafin hannun nata ta qasan table din,lallausan tafin hannunsa yana saukar mata da wata irin kasala da kuma tsoro,bai bata dama ba ballantana ta miqe ta nesanta kanta dashi,ba kuma zata iya nunawa kowa abinda yake faruwa ba.
"Amman adda.....you look familiar,tun randa kuka iso Maldives naji kaman na taba ganin face dinki......kin taba zuwa asibitin SAMHG?" Musaddiq ya shigo da maganar cikin hirarsu. Duban musaddiq tayi tana qoqarin daidaita yanayinta kada wani ya fahimci akwai abinda ke faruwa under the table.
"Eh......kaman sau daya ba......na taba kai wata....." Zancanta kuma sai ya katse,ta maida dubanta kan fuskar anni. Duk tsahon watannin da kwanakin sai yanzu fuskar ta dawo mata fes cikin kanta. Matar nan data fadi wajen sallah asma dinta taso tashi.
"Exactly anni itace..." Ya fada yana sakin murmushi sosai gami da ture abincin gabansa.
"Anni ya akayi kika samota?.....wannan data dinga mana masifa saboda mun barki ba kowa a wajenki.....wannan dinnan dataqi bayyana kanta bare ki gode mata,bayan ta dawo miki da jakanki ba'a dauki komai a ciki ba". Maganganun musaddiq suma sanyashi daga kai daga abincin da yakeci yana maidawa kan fuskarta gami da matse yatsunta softly cikin nasa,yanason yaji qarin bayani,yanason samun tabbacin da gaske ita ta taba cetar anninsu?. Anni da mamakin duniya ya isheta ta ware hannunta tana sakin qaramar dariyar farinciki
"Ban sani ba musaddiq......hammanku zaka tambaya.....duk da shima nasan bai sani ba,tunda bai santa ba" Ta qarashe maganar tana kamo hannun sabreen ta riqe cikin nata
"Yau kuwa zan miki godiyar da nayita so nayi miki ban samu dama ba.......sai gashi cikin hikimar ubangiji wadda ta ceci raina ta zama mata ga yaro na......dame zan saka miki sabreen?". Numfashi taja sosai kaman numfashinta zai qwace mata saboda yadda ta qasan table din fuad din ke mata wani irin salo tsakiyar tafukan hannayenta. Ta kasa fadin komai,sai muryar anni data sake ratsowa.
"Komai zan miki ban saka miki ba takwara.....lallai kinyimin abinda bazan iya saka miki dashi ba.....wallet dina babu ko sisi da aka taba a ciki,kaman yadda wayata ta dawo lafiya lau.....ubangiji ya jiqan magabatanki ya kyautata makwancinsu.....na gode na gode sosai". Murmushin jin nauyin annin ta saki tana yin qasa da kanta.
"Ba komai anni......idan har kana da hali dole ka taimaki wanda yake buqatar taimakon nan,da jikinka koda kudinka". Kai take jinjinawa tare da sake qaunar sabreen din,qasan ranta kuma tana tsara wanne abu zata mallakawa sabreen madadin kirkinta gareta?. Hirar yadda abun ya faru a ranar aka fara maidawa,kadan kadan yana kallon fuskarta yana cin abincin,kallon dake qara bashi qwarin gwiwar cin abincin. Duk wani hirar abun da sukeyi sai yakejin kamar suna qara mata gurbi ne da muhalli cikin rayuwarsa.
"Ashe ta mallaki wannan dabi'ar me kyau?" Ya tambayi kansa yana tuna kiran wayar anni daya dinga yi a wancan lokacin.
"Dama can me tsiwa ce.....dama can bata da tsoro" Ya fada qasan ransa yana tuna yadda ta daga wayanshi har sukaso yin fada.
Tana kallonsa ya gama laqai laqai dinsa,abincin da zaici cikin minti ashirin sai daya jashi talatin da biyar,kafin ya gama duk ta jiqe da gumi,tayi saurin miqewa tana cewa
"Bari nayi fitsari" Sanda ta samu ya cire hannunsa a nata.
"Karki yadda da tsarin yin nesa dani......bazan lamunta ba" Ya fada mata qasa qasa sanda take giftashi. Numfashi kawai ta dinga saukarwa cikin bandakin tana jin bacin ransa,haka kurum zai fara zame mata takura ya hanata sakewa?.
Wucewarta yasa yaji cin abincinsa ya qare,ya dan ture plate din yana miqewa.
"Anni zanje Vaadhoo......but bazan jima ba". Maganansa ya daki kunnenta sanda ta murda qofar dakin anni zata shige. Bata fasa shiga din ba,duk da tayi kaman ta tsaya ta kuma waiwaya ta kalleshi.
" Vadhoo kuma?,wajen wa?" Ta tambayi kanta tana zama gefan gadonsu zuciyarta na tuna mata abinda ya faru na qarshe a wajen a waccan ranar.......ranar data bashi dama ya bude wata qofa da ba tashi ba....qofar da bata tanadawa kowa ita ba. Kusan minti uku tayi zaune a wajen,bata shiga bandakin ba bata kuma san me take tunawa ba. Wani mugun tsaki taja,hankalinta yana dawowa jikinta
"Ko ina ma zaije menene naki a ciki?" Ta tambayi kanta da kanta sannna ta miqe da confidence tana shiga bandakin don rage fitsarin da taji mararta ta tara.
Sanda Jordan ke bude masa murfin motar yaji amna na kiransa. Sai daya shiga ya zauna yabar qafafunsa a waje sannan ya jira isowarta.
"Ga card dinka hamma" Ta fada tana miqa masa black card din. Hannu yasa ya karba yana juyawa. Yana jira yaga nawa aka cira?,amma har yau baiga an dauki ko sisi ba.
"Amneee.....kun gama amfani dashi ne?". Kai ta mirgina tana dubansa a shagwabe kaman yadda ta saba musu.
"Hamma.....adda na kam daban take,taqi karba ma bare ta cire komai,duk inda akaje ko za'a siya abu sai tace bata buqatan komai.....haka adda take wai?,bata da buri sam sam?". Idanusa yadan lumshe yana kuma budesu lokaci guda,wani abu yana saukar masa a zuciyarsa. Yasha aje abubuwa masu daraja da amfani a dakinsa amma koda ta gyara masa inda ya aje komai haka yake zuwa ya sameshi. Baisan adadin dollars da pounds din da yake ajiyewa ba amma ko qwaya daya bai taba dubawa yaga ta zara ba. Kai yake jinjinawa,yanason karantar wacece ita?,yanason ya santa sani na zahiri.....a dazun yaji anni na yiwa iyayenta addu'a marainiya ce da gaske?.
Wani guri ya danna ya zira card din,yana jin a jikinsa bazai iya tafiya bai ganta kusa dashi ba,bazai iya tafiya baiji dumin jikinta ba,qilan idan ya tafi a haka bazai iya aikata komai ba,don haka yace
"Jeki ki kiramin ita......but kiyi sauri ana jirana"
"To" Amna ta fada tana juyawa ciki.
Tana fitowa daga toilet din amna na shigowa.
"Matar hamma hamma yana kiranki.....yace kiyi sauri zai fita ne" Ta fada da dan dariya alamun tsokana kenan a muryarta. Ta bude bakinta da zummar aika masa ba zata samu daman zuwa ba saita hangi anni na shigowa daga baya,wannan ya sanya taja bakinta ta rufe.
Batasan me zata cewa amna ba,zataje ko bazata je ba......amma yadda anni tayi magana ya tabbatar mata annin tayi supporting taje din.
"Idan kin dawo takwara ga ragowan magungunanki nan" Ta aje wata 'yar jaka a hannunta ta juya tana bar musu dakin. Sai dataga fitar anni ta gasawa amna harara.
"Tsakaninki da Allah shi ya aikoki?,banason wasa amna?" Ido ta zaro waje tana duban sabreen gami da son boye dariyarta.
"Am serious Allah adda......ba ruwana shikeson ganin matarsa" Ta fadi tana watsa hannaye. Harararta ta sakeyi ta taka tana neman hijabinta daidai nan anni ta sake shigowa.
"Kuyi da jiki kuzo inason ganinku" Maganan ya gaya mata da ita anni take,sai kawai ta zunduma hijabinta tayi gaba tana qunquni cikin zuciyarta. Itakam ta shirya barinsa cikin kwanaki kadan,....don meye zaita kusanta kanshi da ita?,waima ba zaluntarta da cutarta yakeso yayi ba?,kuma duka yayi?,meye sauran abinda yake nema kuma?.
A hankali ta dinga takawa har ta isa dab da bakin qofar motar inda yake zaune. Tunda ta fara takowar idanunshi yana zube a kanta ta side mirror. Ya lumshe idanu ya bude yafi sau goma,yana jin tana tayar masa da makamansa,wani irin taku gareta da bai taba lura dashi ba sai yanzu......takun qasaita takeyi kamar na bijimin dawisu.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 85
85
"Fatabarakallahu ahsanul khaliqeen" Ya motsa labbansa yana fada yana kallon yadda sassan jikinta ke juya kansu sanda take takawar. Da hannunsa ya dafe kansa yana jin kishi yana cin zuciyarsa,ta fita da abaya me madauri......ta fita da Chantilly......ta fita da qaramin mayafi duka dai kenan kowa ya taba ganin jikinta?.
"Dole na killace kayana" Ya fadawa kansa da kansa cikin qwarin gwiwa.
Kaman bashi yake neman susucewa ba sanda take takowar ba ta cikin madubi,data iso gabansa sai ya zubawa fuskar nan tasa wannan izzar tasa data sanshi da ita. Ya dubeta a kaikaice.
"Haka ake zuwa kiran miji,ka yima mutum tsaye aka?" Ya fada a dake girarsa a tsuke. Duba daya ta masa ya mata kwarjini ta dauke kai,ta soma mita qasan ranta saidai batasan labbanta suna motsawa ba
"Waye yace ka kirani ina zamana?,sai kayi rayuwarka nayi tawa ai,kada wanda ya damu wani"
"Shigo ki gayamin abinda kike cewa" Yayi maganar duka da jawota cikin motar lokaci guda,sai gata kwance a qirjinsa ya dafeta sosai cikin jikinsa,yasa daya hannun nasa yana rufe murfin motar,sannan ya taba wani abu take glass din motar duka suka zama tentac fitilun motar suka koma blue me haske da fari. Sun samu cikakken tsaro da hijabi ta yadda bame iya ganinsu.
Qoqarin tashi takeyi a jikinsa amma ya hana mata wannan damar,ya mata wata kyakkyawar runguma data sanya numfashinsa ya soma sauya.
Maimakon ya barta ta tashinma sai ya kamo fuskarta ya riqeta dab da tashi yana kallon qwayar idanunta,hannunsa daya sauka a qirjinta zuwa wuyanta yana jin yadda zuciyarta ke bugu tak tak tak.
"Ms kike fada dazun?,speak louder" Yayi maganar hucin numfashinsa daya gauraya da qamshin mint na bakinsa tare da sassanyan turarensa suna neman lahantata da tsoronsa da kuma wani kwarjini. Mutsu mutsu ta fara yi cikin tsoron sauyawar da taga launin idanunsa sun fara yi tace
"Nifa bance komai ba" Shuru ya mata bai amsa mata,sai qarewa kyakkyawar fuskarta kallo da yakeyi,kwantacciyar gashin gira dana ido,pink lips dinta da suka dan dago saboda yadda ya riqe fuskarta. Ajiyar zuciya ta kubce masa,ya fahimci kaman akwai tsorosa a lamarinta abinda bai fara ganinsa ba sai bayan faruwar abun,duk da Dr fadwa ta gaya masa zai iya experiencing hakan a na