Author : Huguma Category : Complete Novels
d'ai cikin wani yanayi da zai tabbatar maka da cikar kamala da nutsuwa gami da kammaluwar hankali da nutsuwarta waje guda.
Sanye take cikin wata Turkish gown ta wani lafiyayyen material,rigar ta bude sosai daga qasa,armless ce butter color me adon gray color da wasu manyan flowers masu ban sha'awa,wadda aka yiwa top gray color me dogon hannu da kuma sarqarta a jikin rigar ta yadda basai ta buqaci wata spare sarqa ba.
Tayi rolling kanta da gray color din wani exclusive veil,qafarta na sanye da wani high hill daya kasance mahadin qaramar handbag din hannunta da batafi taci qananun abubuwa ba sai tsananin tsada da jakar ke dashi.
Rungume take da wata baby girl wadda ke sanye da gown armless fara qal data kasance mahadin takalmin qafarta da kuma dan crown din dake saman kan yarinyar wanda ya hana sassalkan dogon gashinta bazuwa zuwa sassan fuskarta.
Wani irin kamanni ne tsakanin ta da yarinyar na sak da sak.......abinda kawai ya banbanta su shine kasancewar yarinyar 'yar kululluba da ita.
Ameenatu muhammad jadda kenan IFFA......shalelen family din jadda....diya mace qwaya daya da suke da ita cikin villa din tasu. Chubby din abbee......chubby din anni......kuma chubby din triplet da twins na jadda villa.
Cikin kyakkyawar nutsuwar nan tata Madame kuma duniyar muhammad jadda wato ameenatu ahmad ke sauka da takalmin ta me tsini wanda zakayi tsammanin ba zata ita tafiya dashi ba,saidai caf caf take takawa da abinta cikin sani kan ado da gayu daya ratsa jini da jikinta gaba daya.
Wani fitinannen qamshi take fiddawa wanda ya huda jikinta,irin qamshin da sai kazo kusa da ita kake iya jinsa a duk wani motsi da zatayi.
Dawowarta kenan daga qasar saudi Arabia,bisa gayyatarta da sukayi don su karramata da lambar yabo da kuma girmamawa ta musamman kasancewar gidan marayunta gida na farko da kaf nahiyar africa dama wasu qasashen qetaren babu koda kwatankwacinsa.
Gida ne daya fara bawa yara feature me kyau......ya fara inganta musu rayuwa da inganta mafarkansu bisa jagorancin me gayya me aiki muhammad fu'ad jadda mamallakin kamfani guda daya da baida kishiya dake sarrafa gold da Diamond a qasash kusan arba'in cikin qasashen da muke dasu a duniya sama da guda dari biyu.
"Karbeta najma.....tayi bacci" Sabreen ta fadi a nutse tana miqawa nanny dinta ita gami da gyara rolling dinta daya dan cukuikuye.
"Sarkin rigima" Nanny din nata ta fada tana rungumeta a kafadarta
"Kunfi kusa,fadanki dana iffa ko waye ya shiga ma kunya zaiji" Sabreen ta fada tana murmushi.
Murmushin daya samu isa ga idanuwan Muhammad fu'ad dake zaune cikin mota,ya kuma kori Jordan ya saita madubinsa yana qarewa duniyarsa kallo abinsa.
Sam bata ganshi ba,bata kuma san yana mata kallon qurillar nan tashi ba,duk da cikin jikinta tana jin kamar wani kusanci yana wanzuwa tsakanin zukatan guda biyu.
"Welcome maa" Shine abinda dukka ma'aikatan da suka rako boss jadda suke fada cikin rusunawa da girmamawa,yayin da ita kuma take amsawa cikin nuna kulawa da tambayarsu aikinsu.
Abun yana bawa fu'ad mamaki sosai.....gaba daya ta zama tamkar wata uwa tsakanin kowanne ruhi dake rayuwa cikin jadda's villa. Ba iya yaran gidan su huda amna dasu saddiq ba......tsakanin kowa da kowa ma,muddin kana kwana kana tashi a jadda's villa.
"Wannan tsadajjen murmushin rabonshi da akeyi ya isa haka please" Ta tsinci lallausan sautin nan nasa cikin kunnuwanta a sanda ya fito daga motar yana bude mata murfin motar yana kuma gyara babbar rigarsa da daya hannun.
"Wow" Ta fada da wani boyayyen sautin da labbanta ne kawai zasu gaya maka abinda ta fada,tana fidda idanunta waje dukka a kansa.
"Muffin......ka koma exactly ranar da ka zama angon ameenatu sabreen.......sak irin shigar".
" Har yau har gobe har kullum ma cikin taya kaina murna nakeyi da mallakar mace irinki......ki taimakeni ki sakayamin kanki cikin motar nan kafin mazan dake airport dinnan kaf su qarasa kallemin ke" Kai ta girgiza tana dariya sanda ta fara takowa cikin jan aji.
"Hammana yaushe xai canza ne?baya kallon madubi yaga yadda ya fara zama babban mutum?,babban mutum din daya ajiye yaran da sati me zuwa zasu kammala secondary school dinsu?"
"Fu'ad bazai taba canzawa ba.....kishinsa da soyayyarsa game da Sabreen suna nan kaman yau aka ginasu" Ya amsa mata yana rufe motar,ya zagaya ya shiga nasa side din.
_wacce addua kuka yimin littafinnan yaqi kammaluwa a yau?_π₯Ήπ₯Ήπ₯Ήπ₯Ή
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
*_NACE BA......._*π§π½π§π½
*_Hajjaju a ina kike siyan turare?....._*
*_NACE A INA KIKE SIYAN TURARE?_*
*_Ga wani fa........TASTED AND TRUSTED ne.......mun gwada munga ingancinsa_*
*_Da yardar Allah saikin godemin_*
*_KUNSAN DUK INDA QAMSHI YAKE ZAKA SAMENI A GURIN,MAGANAR GASKIYA KENAN AHTO_*ππ
Golden oud
Hawi
Sandal balls
Sandal flakes
Cotton bakhoor
Kabbasine mix
Khumra(alba,alsuma,ebony,monarch,musk)
Deep crush (luxury khumra).
Signature oil
Kuleccham
Kabbasine spray
*_YA SUBHANALLAH.....hajiyata dukka wadannan zaki samesu a_*
*_PRIME SCENTS(the scents of royalty_*
*KE DAGA JIN SUNAN KINSAN ZA'A ZUBDA QAMSHI ME AJI DA DAUKAN HANKALI*
*SUNA NAN A*
*_No 3,kabiru sani lawan street,farawa layout,Maiduguri road kano_*
*BA'A KANO KIKE BA?*
*_karki damu,tuntubeta ta nan,TABBAS kayanki zasu iskeki a duk inda kike cikin aminci da yardar Allah,NA BAKI TABBACIN HAKA_*
*DANNA RUBUTUNNAN DON YIN MAGANA DA ITA KAI TSAYE*ππΎππΎ
wa.me/+2348103155915
KO KI KIRATA TA NAN
08103155915π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 173
*_HUGUMA CLOSET ON TIKTOK_*
*follow us diaries*π₯°π₯°ππ½ππ½
https://www.tiktok.com/@huguma.closet?_t=ZM-8y1pf9yfIVZ&_r=1
173
Wani ajiyar zuciyar numfashi ya sauke yana lumshe ido gami da sauke nannauyan ajiyan zuciya.
"Sai yanzu zuciyata zata koma aiki daidai......welcome home your royal highness" Ya fadi cikin salo na girmamawa yana hada hannuwansa guri guda. Murmushi tayi tana girgiza kai,kullum sabuwa ce a wajensa kaman yadda yake sabo a wajenta.
"Giya nake roohi......hayaty kulliha" Ido ya fidda waje yana tashin motar tasa.
"Wannan ranks din nifa bana gane musu sosai yanzu.......jira nake naga nan gurin ya tasa" Ya fada yana taba lafaffen cikinta kaman bata taba daukan ciki ba.
Itama waro idon tayi tana kallonsa. Mamaki yake bata yadda har yanzu 'ya'ya basu isheshi ba,yara goma cas tara dukkaninsu maza mace daya?,me kuma yake da buqata?.
"Muffin......fauzan fawwaz da fawad ba graduation dinsu next week immediately ana gama bikin nadra da haneefa?". Dubanta kadan yayi sannan ya tada motar hankalinsa kwance.
"What's that supposed to mean? And what's the point?......kin daina haihuwa?". Ganin yadda yayi maganan yana nuna da gaske yake fadi,saita karya wuyanta tana narke masa.
"Hamma......yanka sau hudu fa?...."
"Yanka hudun yana nufin kin gama?" Ya sake tambaya yana tsume fuska. Sosai tayi calming down kanta tana saukar da kanta.
"Ni na isa?" Ta fada a sanyaye. Wani abu data lura dashi yana da bala'in son tara yara,Allah ya taimaketa ya dinga bata bibbiyu har sau uku bayan ukun farko da tayi,iffa ce kawai tazo ita daya abinta,shi yasa idan suka tashi tsokanarta suke cemata me baqinjini,ita ba wanda ya rakota,su kuwa saida suka rako juna,duk da cewa a zahiri kusan farinjininta daban yake,kowa yasan wannan,farinjinin diya mace cikin yara maza.
Shurun da tayi ya sanyashi satar kallonta kadan sannan ya kauda kai,bayason damuwa a tare da ita sam sam,don ta gama yi masa komai a rayuwa.
"Bani labari.....How'd the trip go?". Numfashi ta sauke tana son wadata fuskarta da murmushi,saidai kafin tace komai ya sake magana.
"Banga mamana bafa.....a ina kika barta?"
"Tana hannun Nan najma(kaman yadda iffa din take kiranta)" Kai ya gyada
"I missed her so much......da safen nan abinci sam bayamin dadi idan na kalli gurin xamanta naga bata nan". Baki Sabreen ta tura tana bata fuska.
"I don't know me yasa kakeson min kishiya da iffa ne.......zan bayar da ita fa?". Ido ya waro kaman zai saki steering motar yana dubanta.
" What?,yarona ko daya bazan iya badawa ba koda cikin gari ne dani......in fact ma ni koda mutuwa nayi ban yarda a rabamin yara ba bare ina raye".
"Mu ajiye batun mutuwar nan hamma....." Ta fada tana maida aljihun motar data bude ta dauko mint sweet ta saka a bakinta.
"Komai ya tafi daidai hamma......kuma dukka lambobin yabo dana karramawar da suka bayar naka ne....kaine ka cancancesu......ni 'yar tayi ce,Allah yakai kadan kabarin abba.....sun saka kudade masu yawa a asusun gidan,duk da nace bamu da buqatar wannan,amma sunce zasuyi don neman lada,sannan cikin daliban da muke yayewa duk shekara,a dinga ware mutum goma,maza biyar mata biyar yearly zasu dauki nauyin karatunsu har zuwa degree,har masters ma idan suna buqata har sama da hakan". Kai yake jinjinawa,ya jima yana ayyukan lada dana alkhairi kala daban daban,amma wannan din yafi kowanne yi masa dadi da qara masa walwala da nishadi. Uwa uba kuma wani abu daya lura dashi,tun daya sanda gidan ya fara aiki dukiyarsa kaman amai take,wani irin mahaukacin hauhawa takeyi,wani irin bangajejen budi yake qara samu da shi kansa kai tsaye yanzun bazaice ga adadin abinda ya mallaka ba.
Ci gaba sukayi da tattaunawa shi da ita da wani irin yanayi da zai gaya maka zallar soyayya da tausasawa da jin qaine ke wanzuwa tsakanin ruhi da zukatan wadannan masoyan.
Suna isa ya karbi mamarshi ameenatu iffa,don ta farka a sannan. Ita dinma da gudu ta nufoshi tana fadin.
"Miss you abbee...."
"Mamana.....My incomparable mother.....a mother without equal" Ya dagata yana juyata abinsa,ba ruwansu shi da ita da al'ummar dake farfajiyar gidan,wadanda kusan dukansu sun fito ne saboda tarbar Sabreen din,wanda wasu lokuta suke mata title da THE MISTRESS OF THE VILLA.
K'ananun shekaru gareta amma ta zama babbar qarfi da yaji cikin gidan,duk da ta tasamma shekaru arba'in daidai a duniya......amma tsananin kula da kai da gyara jiki da kuma shan natural abubuwan gyara ga diya mace ya sanya zaka yita daukanta a shakarunta ashirin da biyar ko da takwas take. Bugu da qari idan ka kwatantata da su anni da suka kasance manya a gidan,ba laifi idan ka kirata da yarinya. Kusan duk wani dawainiya da matsaloli da zaa kaiwa annin ta hana isarsu Gareta,ballantana maamah da ba cikakkiyar lafiya gareta ba,yau da lafiya gobe babu.
Girman ya karbeta da kyau,yadda ta tafi dashi kuma cikin adalci da mutuntawa ya sanya kowa yake biye da ita da tarin qauna.
Ko a wajen bata wuce ba sai data duba lafiyar duka ma'aikatan,fuad na biye da ita dauke iffa yanata shan surutu,daya hannun nasa kuma handbag dinta ce. Wannan dabi'ar tasa kowa dake jadda villa ya santa,tun suna kunya har ya zame musu jiki. Ko zaman kwana uku kawai kayi cikin villa din zakasan cewa akwai wata mahaukiyar soyayya irin ta hanta da jini a tsakaninsu.
Tare suka jera cikin gidan bayan gamawa da ma'aikatan yana tsokanarta.
"Hajjaju da kanta......yau masu gidan sun dawo kowa ya shiga saitinsa" Yayi maganar yana maqalewa a bayan fuskar iffa yana mata gwalo. Murmushi ta saki tana mintsinar hannunsa.
"Ka daina mantawa fa da cewa yanxun baban samari ne kai.....in suka ganka kana tsokanar ummensu tabbas xakaji kunya".
"Suma sun jima da sanin cewa ba'a raba hanta da jini......yadda nakeso susan zallar madarar soyayyar dake tsakanin abbeensu da ummeensu alhamdlh sun fahimta" Kai ta gyada,ita kanta tasan da hakan,hakan kuma ya taimaka sosai wajen bawa yaran qwaqwalwa da rayuwa me kyau,hakanan kuma suma sai suka tashi da qaunar junansu sosai.
"Banga kowa ba cikin dukka yaran gidan nan ba.....sauban dai ancemin yana gurin anni".
"Kin rigani fade ne......duk da kaman su nadra sun tafi siyayya dasu sahl samr suhail duka sun bisu". Murmushi ta danyi tana jinjina kai,tana sake jin rayuwarta tayi mata dadi idan ta tuna yau zata aurar da nadra da haneefa gaba daya,ragowar abinda ya rage mata kenan take addu'ar Allah yakai mata ranta.
"Kaman yaushe zaku fara bikin nan?" Fuad ya tambaya sanda suke dab da isa sassan maamah. Umarnin anni ne,duk sanda suka dawo daga wata tafiya ko kuma suka tashi da safe zasu shiga su gaisa ita ta yafe zuwan farko,su fara zuwa wajen maamah tukunna su dubata.
"Don itace me lalura,tafi buqatarku a akaina,ni da lafiyata har yanzu da sauran qarfina.....kuma alhamdulillah zan iya yiwa kaina komai"
"Hamma abubuwa kadan zasuyi fa......zasuyi the day of qur'an da dalibai da malamansu na mu'assas.......then zasuyi bridal shower.......sai waleema da anni ta shirya shikenan,dukkansu suda mazan basason dogon biki". Kai ya jinjina,yana jinjinawa yaran,suna da wani irin hankali da nutsuwa na daban,komai nasu moderate ne,shi yasa ya yuwa rayuwarsu wani tanadi na musamman da ba wanda ya sani sai ranar da aka daurawa kowaccensu aure.
"Ma sha Allah.......Allahumma barik" Ya furta suna sanya qafa makekiyar balcony din da zata sadaka da falon.
Idanunta akan tashar saudi sunnah da suke hasko masallacin ma'aiki tare da karanto hadisansa masu tsarki girma da alfarma,zuciyarta takejin tana tsananin kewa da qishirwan gurin,kaman bata taba zuwa ba tunda take a rayuwarta. Sukanje tana bin jama'ar gidan da suke da kebantattun lokuta da jirgin jadda majesty jet yake jigilar kowacce halitta dake birnin jadda villa din bayan kowanne hutun makaranta da za'ayiwa yaran. Wannan damar suke amfani da ita suke ziyartar fauzan fawad da fawwaz dake karatunsu a madeena king Abdul'azee international School wadda suka kammala kuma za'ayi bikin yayesu sati me zuwa.
Kaman saukar nannauyan dutse daga qirjinta haka taji sanda sukayi sallama a tare,ta motsa bakinta tana amsa musu da sautin da ba'a fahimtar abinda take fada sosai sai wadanda suke da matuqar ganewa kaman sabreen din,don shi kansa fu'ad din sometimes sabreen ce ke gaya masa abinda tace din.
Idanunta ta janye a kansu tana maidawa kan yarinya ta biyu da Allah ya jarabceta da masifar son yarinyar......yarinyar da duk gidan kowa qaunarta yakeyi saboda kasancewarta jika diya mace qwaya daya kaf cikin jikokin gidan ashirin da wani abu. Ameenatu iffa ta sakarwa maamahn murmushi tana zamewa daga jikin fu'ad ta tsallako da gudu tayo wajen maamah.
"Har yanzu baki tashi kin fara tafiya ba?,kikace zaki fara tafiya kafin mu dawo?" Ta fadi cike da quruciya cikin maganarta. Murmushi kawai maamah din ta sake,yarinyar ta tattaka qafafun maamahn ta haye cinyarta tayi dare dare tana bata labarin su hamma fauzan suna gaisheta.
Tayi kewar 'yan ukun sosai,su na dabanne a zuciyarta,duk da gidan cike yake da tagwaye amma nasu qaunar daban yake. Har yanzu suna iya kira video call su dukka ukun su sakata a gaba da hirarraki har sai sun sakata dariya sanna,har zaman jiran kiransu takeyi kulli yaumin,koda basu kira ba zata sanya a kira mata su.
"Barka da warhaka maamah.......ya qarfin jikin?".
" Alhamdulillah " Yau sautin amsa gaisuwar sabreen din ya fita da kyau har sai da sabreen ta daga kai ta kalleta a mamakance.
"Ya taro?" Ta fada da sarqaqqen harshenta.
"Alhamdulillah.....mun kammala cikin nasara"
"Allah ya taimaka" Ta sake fada da qyar tana fuffusgo kalmar.
"Ameen" Sabreen ta amsa tana sadda kanta tana tattalin hawayen farincikin dake son ballewa cikin idanunta.
Kamar yadda maamah ta zata din,sabreen din saidata tabbatar komai yana tafiya daidai a sashen,daga masu kula da ita har kalar abincin da ake bata sannan suka wuce sassan anni.
Suna zaune da mutuminta sauban a courtyard din da ya zamana shuru saboda fitar duka yaran da rashin motsinsu wanda anni batasan me ya kawo hakan ba.
Murmushi ya sakarwa ummeen nasa da abbeen nasa,ya zare headphones din ya ajiye ya tako da nutsuwar nan tasa yana fadin.
"Sannu ummee.....abbee sannu" Ya fada yana kamo iffa wadda tayi tsalle ta daneshi. Akwai sabo sosai tsakaninsu,don wani irin sassanyan kulawa yake bata ta hankali.
"Anata karatun sauban?" Sabreen ta fadi bayan ya gama gaidasu,fu'ad ya dora hannunsa saman kansa. Yana jin yaron sosai a jininsa saboda yadda yake da maitar karatu,yana da buri sosai akanshi,kowanne yaro nashi yana bashi karatu daidai da abinda ya fuskanci yafi karkata akai.....kaman yadda ta fannin neman kudi ma yayi alqawarin zaibar kowa yayi kalar neman kudin da yafi sha'awa muddin bai sabawa addini ba.
Da wani irin alfahari qauna da soyayya anni ke kallonsu a gabanta,har suka gama gaisawa suka fara taba hira
"Kije ki huta takwara,anjima akwai general dinner a babban dining room na gidan nan,sai a qarasa hirar a can" Murmushi tayi a kunyace sannan ta miqe,fu'ad ya tayata da jakar suka rankaya dukkaninsu wannan karon har sauban suka fice.
Tun kafin sukai ga bude qofar sassan taga kaman parlor din farko yayi duhu da yawa,bangaren sitting room ba ba wani wadataccen haske. Tanata so tayi magana amma kuma Allah bai bata iko ba har sai da suka shiga parlor din.
Duduun ba wani haske,abun da ya basu mamaki kenan daga ita har fu'ad din,ta bude baki zatayi magana fitilan