A Duniyata Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Huguma Category :  Complete Novels

Chapter   86 / 119

255K to 258K   out of 356.9K words

WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*

*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*

*_HAIHUWA KIKAYI?_*

*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*

*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*

_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_

08104553105
08127084190

*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*


*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*

___________________________


128



ma'u tana tayashi. Parlor abba ya fita don amsa waya,sai sukaci gaba da tattaunawa a tsakaninsu.

Zukata sunyi sanyi sun kuma samu nutsuwa daidai gwargwado,sauran abinda ke cikinsu bashi da yawa,godiya kawai sukema Allah daya tsallakar dasu daga fuskantar wannan bala'in.

Idanunsa yake saukewa a kansu,kowa cikin walwala yake da farincikin samun kubutarsa.....kowa kuma a cikinsu soyayya da qauna ce irin ta fil'azal tsakaninsu,amma abu guda dake taba zuciyarsa shine sam ba MAAMAH ba dalilinta. Maman daya kamata itace a gaba kafin kowa?,maman daya dace a bisa mizani na hankali dacewa da kamata ace itace damuwarta ta dara ta kowa.....ta d'ara ta babarsa anni.....ta d'ara ta 'yan uwansa,ta kuma d'ara ta matarsa......saidai sabanin hakan maamah din itace halittar da tafi kowacce halitta rashin damuwa da yanayin nasa,sai ya maida idonsa ya rufe yana jin wannan zafin har tsakiyar zuciyarsa.

Saddiq ya gama da kowa farouq ya dubi musaddi

"Zubawa dude ka bashi ko kadanne ko zai karba". Harara fu'ad ya zubawa farouq,yaso ace su anni basu wajen da ya bashi amsa daidai dashi. Idanunsa ya juya a hankali inda sabreen ke zaune tana juya zoben dake yatsanta,don ita ba kowanne abinci take iya ci ba.

"Ke ba zakici abincin ba?" Ya fadi da wata murya can qasa yana mata kallon qurilla. Sau daya ta dago kai ta kalleshi ta mayar qasa tana ci gaba da juya zoben hannun nata.

"Na qoshi". Motsawa yayi kadan yana son gyara zamanshi.

"Zubo kizo nan" Ya sake fada ba tare daya dubi inda anni take ba.

"Yauwa....gwara ka tilastata taci,ko ba yawa aizai zauna,ta yaya kina da lalura amma cin abinci ya zama yaqi ameenatu?". Idanunsa ya sake maidawa kanta,sunan ameenatu yana masa dadi sosai,idan ya kalli fuskarta yakuma ambaci sunan sai yaji tayi bala'in dacewa da sunan,musamman idan ya tuna tarihin asalin me sunan.

A kunyace ta miqe,ta zuba komai dan kadan kadan sannan ta dawo.

"Zauna a nan" Ya nuna mata gefansa. Dan satar kallon anni tayi kafin ta zauna din tana bada tazara kadan tsakaninsu sannan ta ajiye plate din a tsakiyarsu.

Spoon ta zura masa a ciki ta kalleshi,sai ya langabe kai yana bata fuska.

"Bazan iya ci ba.....aikinsan bani da lafiya ko?" Sai kuma yayi qasa qasa da muryarsa yana satar kallon farouq.

"Idan kuma so kike farouq yayi mana dariya ya yadda da gaske ba zaki iya bani kulawa ba to".

"Anni muffin.....anni a gurin"

"Kada ki damu,ita hirartama take dasu saddiq,ita kanta zatafison taga kina kula dani......oya bani abinci" Ya fada yana lumshe idanu saboda yadda yakejin wani yanayi yana ratsashi.

A d'arare ta debo abincin ta taho dashi bakinsa,sai ya kauda kai yana kallonta.

"Eat first" Ya fadi yana tsareta da ido. Fuska ta bata,batasan ta shagwabe masa ba tace

"Hamma.....bazan iya ci ba".

"Zaki iya.....zakici in sha Allah,kada kiji tsoro" Ya bata tabbaci yana kallonta. Da kadan da kadan ta dinga miqa cokalin bakinta har ta juye abincin,ta soma taunawa tana rolling idanunta cikin tsoron kada amai ya biyo baya,sai taji zuciyarta ko cikinta basu wani hautsine ko juya ba yadda suka saba ta hadiyeshi tsaf.

"Good girl.....am next" Ya fada yana gyaran zamanshi. Debowa tayi ta miqa masa,ya bude baki ya amshe kaman qaramin yaro.

"Hmmmm........dadin abincin daya fito daga hannunki daban yake......ban taba jin abincin da yayi dadin wannan ba......Allah ya qarawa hannuwanki da rayuwarki albarka". Ya fada yana lumshe ido a kanta.

"Ameen" Ta amsa tana sadda kai tana satar kallon dakin. Wayam ta gani,ba wanda ta samu a dakin duka sun fice ba tare da tasan sanda suka fice ba,saita dawo da dubanta kan fuskarsa idanunta a warwaje. Dariya me qaramin sauti ya saki

"Sun gudu......they can't wait to see" Fuska ta tabe ta kyabe baki kaman zata saki kuka

"Kaga irinta ko?"

"Wayyo Allah hannuna" Ya fada shima yana karyar dakai gami da riqe hannun da daya hannun. Tuni ta watsar da komai tayi wajen tana riqe masa a rude.

"Sannu.....da zafi ko?,fama maka nayi?,yi haquri.....ko a kira Doctor" Yadda ta fadi doctor din sai labbanta suka masa wani mugun kyau. Lallausan kiss ya saukar mata saman lips din yana dariyar yadda ya cita wasan,ya samu hanya mafi sauqi na sake kusantar da kanshi da ita.

Sai kusan dare can sosai sannan su anni sukayi niyyar wucewa masaukinsu. Ya tsareta da ido ganin tana hada jakarta da tarkacenta,a ransa yakejin muddin tace zata wuce tabi su anni saidai su tafi tare,don kuwa bazai zauna ba shima tana wani gurin yana wani muhallin na daban.

Kamar anni tasan abinda yake tsarawa,ta ciro wani babban envelope ta aje mata a gefanta.

"Ga magungunanki nan.....kada ki kwanta baki sha ba.....mun wuce gida mu,sai gobe idan Allah ya kaimu.....saiki kula dashi....muhammad Allah ya qara afuwa,sai da safe". Har baisan sanda murmushi ya kubce masa ba,yasa hannunsa me lafiya ya shafi kansa.

"Ameen anni,na gode sosai,Allah ya qara girma" Ita kanta annin tasan godiyar da biyu ake mata ita,batace komai ba dai ta shanye,har sunkai qofa ta waiwayo.

"Ki kula da kanki da kyau,kada ki manta da abinda likita ya fada" Ta qarasa maganar tana sauke dubanta kan fuskar fu'ad. Ko batayi maganan kai tsaye ba ya fahimci shi anni ke ajiyewa saqon,saboda haka suna fita ya jawota jikinsa yana cewa.

"Ni za'a yiwa gulma?,wai anaso ana kaiwa kasuwa......kinsa anni ta tsareni da warning,wannan maganar da biyu aka yita,kuma dani ake nasan......ita anni ta jikokinta kawai take bata ta d'anta" Ya fadi yana sansana kunnenta,abinda ya sanya tsigar jikinta xubawa,ta yunqura da niyyar gocewa a jikinsa,sai ya fake kaman yadda ya saba.

"Wayyo hannuna" Dawowa tayi da sauri ta zauna tana masa sannu.

"Muga hannun.....idan yana ciwo a kira likita mana" Ido daya ya kashe mata yana kallonta.

"Kece likitan ai.....jeki kulle qofan da key ki dawo na nuna miki abinda zakimin ya rage zugin da nakeji" Ya fada yana karya wuya kaman da gaske zugin yake. Da zuciya daya taje ta rufe din ta dawo,saidai kafin ta ankara ya jawota jikinsa ya matseta da kyau,kota ciwon ma bayayi.

"Kada ka fama ciwonka fa.....hannunka muffin" Taketa fada cikin damuwa,bata kula sam da yanayinsa ba sai daya riqe fuskarta da hannunsa daya,sannan ta maida dubanta fuskarsa. Gaba daya idanunsa sun canza launi zuwa kalan ja,kaman yadda numfashinsa yake fita a wani hautsine,take ta fahimci inda lamarin ya dosa.

"Sabrrrrr" Yadda sautin ya fita saida tsigar jikinta ya tashi,ta runtse idanunta tana jin ya saukar mata da wani azababben yanayi a dukka sassan jikinta. Sunan da muddin ya kirata dashi tabbas akwai wani abu me girma akanta cikin zuciyarsa kenan. Idanunta da sukayi laushi ta zuba masa tana kallonsa itama,tana jin wani abu yana tasiri sosai a jikinta da ruhinta

"I can't hear you,you have too many clothes on" Ya fada muryarsa can qasan maqoshi. Idanunta ta maida ta lumshe,ta gani rigima ce fal idanunsa,ta yaya kuma zai nema rigima irin haka a irin wannan yanayin da suke ciki?.

"Please ki rage wannan kayan.....hutawa nakeso nayi". Maganan ya sake mata nauyi,ta bude idanunta a kansa.

"Hamma......asibiti muke fa?" Ta fada a narke da wata irin shagwaba data sake kunnashi.

"Shshshsh" Ya fada yana dora yatsansa akan lips dinsa,idanunsa suna sake narkewa. Sake zuba masa ido tayi har sai daya karya lagonta,a hankali ta motsa labbanta.

"Me kakeso?" Tafin hannunta ya kama sosai ya saka cikin nasa yana murzawa,laushin tafin hannuwansu ya ratsa juna da wani irin dumi da jikkunansu sukayi.

"A lot things duniyata...i missed you badly.....but ukunnan....long hug....deep looks....slow kisses,i want you in the worst way...." Can qasa yayi da muryarsa cikin salo na rad'a

"Your taste....scent,and feel of your skin next to mine,Duniyata......our bodies could be skin on skin.....i want it all tonight,karki hanani yin komai.....if not" Sai ya girgiza mata kai yana kada mata yatsansa.

Gaba daya kalamansa sun gama tsumata,sun gama tafiya da tunaninta da nutsuwarta,sai ta zame hannayenta a hankali daga nasa,ta fara tafiya da baya da baya kafin ta juya tana fadawa toilet.

Tsaiwa tayi na wasu sakanni tana maida numfashi......tana sake ji da gaske fu'ad DUNIYARTA NE.

"Nothing is hotter than a romantic man" Ta furta tana sakin murmushi ita daya gami da rungume hannayenta a qirji tana jin duniyar tana shawagi da ita.

Cikin nutsuwa ta fidda kayan jikinta ta shige jacuzzi ta sakarwa kanta ruwa me dumi bayan tayi brush,koda ta gama cikin tattausan babban towel ta lullube jikinta ta yafa wani saman kanta.

Dole ta fita a haka saboda kayanta suna dakin,ta soma takawa a hankali tana ficewa.

Zaune ta sameshi saman zagayyar sofa din da aka aje don hutun majinyaci. Kwarjini ya mata da yawa,don ba komai a jikinsa sai boxer. Faffadan qirjinsa me cike da gargasa da dukka muscles dinsa a bayyane suke,saita danji nauyi ya kamata,qafafunta suka dan fara rawa. Ya gani,ya kuma lura,saboda tunda ta fito idonsa yana kanta,ta masa wani irin kyau,kyan da bai taba lura dashi ba sai yau.

"Sabrrrr" Ya kirata a hankali sanda take kici kicin neman kayan da zata saka. Waiwayowa tayi a kunyace ta dubeshi,yantsansa ya kada mata yana lumshe idonsa.

"We don't need any night wear.....skin to skin contact....it's where words fade and our souls speak" Ya qarasa maganar yana shafa qirjinsa saitin zuciyarsa idanunsa suna sake rusuna..

Ba musu ta watsar da kayan,ta jawo hijab ta zura tana jan under wear dinta sama. A hankali ta tako inda yake,qamshinta yana kado masa har saman fuskarsa tun kafin takai ga qarasowa. Idanunta taketa kaudawa gefe,batason su hada ido.

"Ka shirya na taimaka maka ka kwanta?". Shuru ya gifta na wasu daqiqu,har tayi tsammanin amsawa ne bazaiyi ba,saidai sanda ta daga kanta sai taga iya ya zubawa ido yake kallo idanunsa a kanta kaman zai cinye namanta.

"Am ready my world.....but kafin sannan ki kashe duka wutar dakin.....ki ragemin AC dinnan,ki ajemin ruwa saman drawer dincan......sai kizo ki taimakamin din" Ya fadi yana canza ma'anar maganar daga qarshe. Duka ga ganoshi amma tayi biris,tayi dukka abinda yace din sannan ta tako gabansa a hankali tana miqa masa hannunta. Ido ya zuba mata,shi kadai yasan kalar soyayyarta sake dawainiya dashi......ya yadda da gaske so zai iya zama ajalin mutum.......yana kyautatawa Allah zato.....yadda ya yiwa soyayya mummunar qi da mummunar fassara da kuma mummunan zato......baya saka ran sabreen zata zama cikin jerin jarrabawarsa a rayuwa. Sai daya gama qare mata kallo sanna ya dora hannunsa saman nata a hankali,ta hada qarfinta tana jin zai iya dogara da ita ya miqe,amma inaaaa wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa..gaba daya ta rikito jikinsa wanda yafi kyautata zaton da gayya yayi mata haka.

"Subhanallah" Ya furta da raunanniyar muryarsa yana boye dariyarsa.




*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862


๐ƒ ๐” ๐ ๐ˆ ๐˜ ๐€ ๐“ ๐€
_Zafafabiyar_

ฬถBฬถOฬถOฬถK ฬถ2

โฑงษ„โ‚ฒษ„โ‚ฅโ‚ณ

๐™‹๐˜ผ๐™‚๐™€ 129


*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*


*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*


*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*

*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*

*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*

*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*

*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*

*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*

*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*

*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*

*_HAIHUWA KIKAYI?_*

*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*

*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*

_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_

08104553105
08127084190

*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*


*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*




129



Tashi tayi tana zumbura baki alamun fushi

"You do it knowingly" Sosai ya sake boye dariyarsa,bayaso ya bata rawarsa da tsalle da wuri,sai ya daga hannunsa irin na surrender.

"It won't repeat itself"

"You're not kidding right?" Kai ya gyada mata kawai dondai yasan wannan alqawarin bazai dauku ba.

Sake bashi hannun tayi,ya miqe din saidai ya maqale a jikinta yana narke mata.

"Hamma?" Ta kirashi a shagwabe.

"Sabreen" Shima ya kirata da salon data kirashi,abinda ya sanya ta saki dariya kenan ba tare data shirya ba.

A hankali ya haura gadon,ta saka masa pillow daidai da yadda taga yafi kwanciya ya maida bayansa ya kwanta a hankali,tana niyyar janyewa ba zato ba tsammani ya jawota gaba daya cikin jikinsa tamkar baya tuna akwai ciwo a hannunsa,take ta samu kyakkyawan masauki a jikinsa.

"Karkimin musu....karkice komai.....wannan shine cikakken ma'anan jinyan da nakeso kiyimin......that's why nace banason jinyan kowa sai naki,am craving you so bad....you're my place" Ya qarasa fada sanda yake zame Undearwear din da ya rage a jikinta,sannan ya sabule hijabin jikinta ya maye gurbinsu da jikinsa.

Bata hanashi ba,saboda tasan zai wahala a yadda hannunsa yake ya iya wani abu me dogon zango,ta barshi yayi birgimarsa yayi rigimarsa yadda yakeso,skin to skin connection ya sameshi har fiye da yadda yake buri,saidai dukkaninsu ya jefasu wani irin yanayi da ya sanya da qyar suka iya bacci,kowa na qoqarin kai zuciyarsa nesa.

โ˜…Wani zazzafan mari ya saukewa fuskarta,yana dubanta da wani mahaukacin fushi da bata taba gani kan fuskarsa ba

"How dare you zaki hari mutum kaman muhammad jadda?,have you lost your mind?" Ya qarashe maganar jijiyoyin kansa suna tashi,yana jin kaman zaiyi qaramin hauka.

Da zallar mamaki ta dora hannunta saman fuskarta tana duban mahaifin nata,karo na farko daya taba dora yatsunsa biyar saman fuskarta kenan da sunan mari bada sunan soyayya da lallabawa ba,wani abu da bai taba shiga tarihin rayuwarta ba sai yau.....yau ita mahaifinta ya daka saboda fu'ad?.

"Abba?.....maman naka ka daka saboda wani?" Ta tambayeshi tana nuna qirjinta da yatsanta cikin jinta cikin zallar tozarci dumu dumu

"Wani?,wani fa kika ce?,shi wannan din da kike kira wani kinsan wayeshi?,nace kinsan wayeshi?,kinsan rufin asirin da ya yiwa.mahaifinki?,kinsan cewa banda shi da baki isa ki tsaya a inda kike tsaye ba a yanzu?,kinsan waye boss na mahaifinki?,to MUHAMMAD FU'AD JADDA NE!". Shock taji sosai irin wanda bata taba ji ba,ta cire hannunta daga kan fuskarta tana dubansa idanunta dukka a warwaje.

"Kinsan tsakanina da talauci a yanzu takun taqi kadanne zan afka cikinsa!......kinsan anyi freezing duk wani account nawa....anyi banning all my properties?,duba nan...." Ya fada a hargitse yana cilla mata wata takarda.

"Takardar sanya hannu ne na dukkanin wanda keda ruwa da tsaki na saukeni daga muqamina.....duk a silarki fareeda!!!,ki gayamin meye ya rage mana yanzu?!" Ya tambayeta a tsawace yana watsa mata jajayen idanunsa.

Wani irin tashin hankali taji yana sauko mata,kalar tashin hankalin da bata taba jin makamancinsa ba,ta koma da baya ta zauna tana jin ta fara gani.bibbiyu.

Anyi banning duka properties na abbanta,harda motarta suturunta,gidansu da suke taqama da alfahari dashi.....anyi freezing accounts dinsa yana nufin harda nata daukacin accounts din......an sallameshi daga muqaminsa yana nufin daga yanzu an cire mata tittle na diyar AMBASSADOR KHALED MUSTAPHA?".

"This is insane.....unbelievable" Ta fada tana girgiza kai da qarfi don kwanyarta ba zata iya daukan wadannan abubuwan duka lokaci guda ba.

"Ba zaki gane insane bane sai lokacin da arrest warrant ya iso cikin gidannan da zummar kamaki a mazaunin masheqiya.....don tabbas!.....ina me Tabbatar miki jadda baya shurun banza......all these yayi ne tauna tsakuwa kawai don aya taji tsoro.....ina me Tabbatar miki bazai raga miki ba......kinyi yunqurin yin kisan kai......kuma bazan goya miki baya ko na hana a hukuntaki ba". Kowanne halitta na cikinta sai data kada tsananin tsoro

"Dad......na dauka ko meye na dauko kai me tsayamin ne?,abba yau da kanka kake wannan maganar?". Wani banzan kallo ya watsa mata,ya matso gabanta yana dubanta sosai.

" Ki taba kowa....ki tsokano kowa amma banda muhammad jadda.....mayunwacin zaki ne......damisar da tafi qarfin wasa......fareeda!!!!!.....wai mema kika sha?,still kina shaye shayenki da alama har yanzu ko?,magana ake miki na talauci yana bakin qofa yana qwanqwasa mana qofa fa!" Ya sake fada a gigice kuka na dab da qwace masa.

"I can't take it......bazan iya jura ba......rasaki da hukuncin duk da jadda zai dauka a kanki yafimin sauqi akan rasa dukiyata". Sai ya jawo wayarsa yana lalubar number muhammad jadda yana fatan samunsa ya nemawa kansa gafara da sassauci.

Zata iya cewa kaf tsahon rayuwarta bata taba jin wani abu daya gigita hankalinta irin wannan maganar ba,duban dad din nata takeyi ta koma kaman gunki,kowanne sashe na zuciyarta ya cika da tsoro da nadama da tashin hankali,ta yaya zata tunkari wannan babbar musibar dake tunkarota?.

โ˜…Tare sukayi sallan asuba shi da ita,ta lafe a jikinsa suna azkar tare ita dashi,a haka a haka har bacci ya

86 / 119