Author : Huguma Category : Complete Novels
gaba da gyara mata lullubin,a nutse yace.
"Har yanzu ba zaka daina yimin kutse ba kenan farouqu.....wannan....." Bai qarasa ba saboda idanun da sabreen ke juya masa tana masa nuni da bayansa. Da ido shima ya tambayeta,tayi qasa da muryarta kamar me rada.
"Like kaman shi da fannah ne hamma" Shuru ya danyi sannan ya dage girarsa yana sauketa,yaja da baya daga gabanta sannan ya waiwaya.
Fannah dince,tana a gefensa kanta a qasa,kunya kaman zai kasheta. Tasha labarun soyayyar sabreen da dude enshi,amma bata dauka haka sukejin DUNIYOYIN nasu daga su saisu ba sai a yau din. Tun daga nesa data hangi yadda guard dinsa sukayi musu qawanya take mamaki,ta dauka zallar tsaro ne suke bashi,ashe su suna qarfafa tsinkar fule da fulawar da akeyi ne daga tsakiya. Abun ya bala'in burgeta,sun kasheta sun kuma tashi kanta,har ta dinga murmushi duk da kunya da nauyin FU'AD da take danji,don yana mata kwarjini sosai.
"Qaton banza......ka taho da diyar mutane amma ba zakamin magana ba?" FU'AD ya fada yana hade girar sama data qasa shi a dole babba. Fannah ta qwaci farouq da dariya ta hanashi bashi amsa.
"Barka da yamma hamma". Qasan ranta tana mamaki dama yana taba barkwanci haka?,idan kaga face nashi a news ko a news paper ko a wani taro na kasuwanci ba zaka dauka yana murmushi bama bare akai ga barkwanci,kaman bashi ba.
"Barka kade amarya.....ya baqunta da sabon guri?" Ya fada cikin kulawa da girmamawa.
"Alhamdulilah hamma....yame jiki?,Allah ya qara lafiya yasa kaffara ne" Fannah ta hada duka ta fada don kwarjininsa ya mata yawa.
"Ameen" Ya furta yana jin kalmar kaffara din data fada tayi daidai da a roqawa maamah ita din.
Gaba yayi suna jerawa da farouq bayan fannah ta qarasa wajen sabreen suka jera suma suna gaisawa. Karon farko kenan da suka fara ganin juna face to face,saidai kowaccensu yanayin nutsuwar dayar tayi mata.
"Ayi mana afuwa,bamu samu haduwa ba,yanayin yazo da ciwon boss,ba daman nayi nisan zango na barshi,sai yau Allah yayi muka hadu" Sabreen ta fadi tana dan murmushi.
"Aiba komai.....ana tare ai,shekaru masu yawa a gaba muna fatan hakan,yana da kyau a kula da boss sosai ai.....kema kuma dole ki rage zirga zirga ai saboda naki yanayin" Fannah ta fada tana murmushi. Mamaki yadan kama sabreen,wai cikinta ya soma fitowa ne?duk da fannah din midwifery ta karanta dama,saita dora hannunta saman cikinta.
"Cikin 'yan uku daban yake ai adda.....sauri girmansa da kuma yawan satittikan da yake dauka a haifeshi,baya kaiwa dadewar cikin twins ko single baby" Ta fada da muryarta maras hayaniya. Kai sabreen ta girgiza,bayanin na fannah ya gamsar da ita,ta kuma fahimta,da alama kuma zata amfana da ita sosai.
A hankali suke takowa shida farouq din suna tattaunawa.
"Mun jima a asibitin,gida zamu wuce.......amma kunyi cikakken magana da likitan da yake ganinta?" Farouq ya tambaya da dan alamun damuwa kan fuskarsa.
"Banganshi ba.....bansan wanne likita ke ganinta ba.....sai yau na samu shigowa asibitin".
" Why?" Farouq ya tambayeshi yana nuna rashin jin dadinsa,duk kuwa da cewa yasan komai,saidai muddin dai maamah tana raye....muddin dai maamah din sunanta mahaifiyarsu ko sau daya bayajin akwai Randa zaice yayi mata wani rashin kirki ko me tayi.
"Farouq.....Allah ne ya kiyayeni......da taimakon Allah da taimakon sabreen,banda hakan nima da tuni yanzu ina nan inata checking BP na......saura kadan jinina ya hau,ciwo zuciyata ta dinga yi,banda dauki da Allah ya kawomin na bani mace ta gari......hutawa nayi na kwana uku farouq,bansan da wanne fuska zan kalleku ba kuda anni.....mahaifiyata ta zama silar da saura kadan anni ta rasa diyarta......wannan sakayyar ya kamata ta samu ta bangarenmu?" Ya qarashe maganan da alamun abun yana masa mugun d'aci.
"Dude.....na taba zaginka?.....inajin zan fara wannan karon" Farouq ya fada ba tare daya dubi FU'AD ba.
"Ashe har akwai banbanci tsakaninmu da ku?,ashe har akwai abinda zamu yiwa anni ta tsanemu kenan indai zata tsaneku ko.taji haushinku akan abinda baku kuka aikata ba.....ka saka a ranka ma tun wuri ka sake gayawa kanka cewa....ni dakai mahaifa daya muka kwanta aka haifomu tare,kaman yadda musaddiq da saddiq suka kwanta mahaifa daya aka haifosu tare......har abada ba wani banbanci". Shuru kawai FU'AD yayi,har abada baisan da meye zaiwa wadannan bayin Allah sakayya ba.
"Ya kamata ka duba yanayin jikin nan nata da kyau,anni nata yimin fada tun jiya......ina ganin ma kamar qasar ya kamata a fidda ita....saidai kaje zaka gani,hawan jini yayi mata mummunar kayarwa" Ya qarasa fada da sautin jimami a muryarsa. Kai ya kada yana nazarin abun,hawan jinin da baida labarin sadda ta sameshi,ya sake kada kai yana tuna wata kalma data taba fadawa abbansu randa ya dawo result din kamuwa da hawan jini.
"Kadanma ka gani......shi talauci in gaya maka idan ya samu ciwo yaga gurin zama kenan....duk talaka da hawan jini yake qarewa,kaga somi somin daukan hanyar mutuwa kenan,ciwon qoda,hanta,zuciya,lalacewar hanji duka daga hawan jini yake farawa......bari na fara tanadi don kaina" Tayi maganar tana miqewa abinta ta barsu a dakin da takardarsa da magungunansa a leda.
Bai amsawa farouq ba,illa wani nannauyan numfashi daya sauke bayan ya gama tuna wannan,sai shima farouq din bai sake cewa komai ba. Ya sanshi,a dabi'arsa ba komai yake baka amsa ba,idan kuma kaga bai baka amsar ba to lallai baka da buqatar bada amsar ne.
Dab da zasu shiga reception na asibitin da zai sadasu da sassan asibitin,sanda guard dinsa ke clearing masa hanya ya tambayi farouq.
"Inasu saddiq?" Harara ya balla masa.
"Zama zasuyi jiranka?,kwanan amna daya a asibiti abba yace kowa ya dauki matarsa su wuce gida". Ido yadan fitar.
"Me yasa abba bai bari amna jikinta yayi qwari ba?" Ido farouq ya zuba masa sannan ya bushe da dariyar mamaki.
"Kana tsoron kada ayiwa qanwarka abinda ka yiwa diyar mutane ko?,to abba yace ta qarasa warkewa a dakinta..
..kaga malam ka barshi shima ya shana......wannan lamari baya buqatar shamaki ko shishshigi fa" Farouq ya fada yana dan shafa gemunsa cikin nishadi. Dunqule hannu FU'AD yayi yakai masa duka
"Sai yanzu kasan haka kenan?"
"Fes kuwa" Ya amsashi yana dariya. Mur FU'AD yasha ganin su sabreen sun kusa da inda suke,farouq kuma yaja tunga.
"Wucewa zamuyi gida.....zamuzo muku ziyara once kafin mu wuce honeymoon" Ya fada cikin salon tsokana yana bawa FU'AD hannu.
"Sai kunzo....Allah yasa muma ku samemu" Ya amsa masa yana bagararwa.
"Iyeeee.....lallai mutumin nan.....baku gaji ba?"
"Kai ka sani" FU'AD ya fada yana danne murmushin daya taso masa.
Tsayata yayi a bakin qofar amenity din,suka gama sallama da fannah,sukayi exchanging phone numbers sannan ta tako ta sameshi. Hannunsa ya sanya cikin nata ya riqe gam kamar wadda za'a qwacewa ita,har sai data daga idanunta ta kalleshi suka hada idanu,idonsa ya dauke,sai mamaki kadan ya kamata,kaman ya manta gaban surukarta maras lafiya zasu shiga?,bazaiyi alkunya tafin hannunsa cikin nata ba,ta bishi kawai yana tura qofar gami da sanya qafarsa a ciki.
*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
π π π π π π π π
_Zafafabiyar_
ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2
β±§Ιβ²Ιβ₯β³
ππΌππ 153
*_NACE BA......._*π§π½π§π½
*_Hajjaju a ina kike siyan turare?....._*
*_NACE A INA KIKE SIYAN TURARE?_*
*_Ga wani fa........TASTED AND TRUSTED ne.......mun gwada munga ingancinsa_*
*_Da yardar Allah saikin godemin_*
*_KUNSAN DUK INDA QAMSHI YAKE ZAKA SAMENI A GURIN,MAGANAR GASKIYA KENAN AHTO_*ππ
Golden oud
Hawi
Sandal balls
Sandal flakes
Cotton bakhoor
Kabbasine mix
Khumra(alba,alsuma,ebony,monarch,musk)
Deep crush (luxury khumra).
Signature oil
Kuleccham
Kabbasine spray
*_YA SUBHANALLAH.....hajiyata dukka wadannan zaki samesu a_*
*_PRIME SCENTS(the scents of royalty_*
*KE DAGA JIN SUNAN KINSAN ZA'A ZUBDA QAMSHI ME AJI DA DAUKAN HANKALI*
*SUNA NAN A*
*_No 3,kabiru sani lawan street,farawa layout,Maiduguri road kano_*
*BA'A KANO KIKE BA?*
*_karki damu,tuntubeta ta nan,TABBAS kayanki zasu iskeki a duk inda kike cikin aminci da yardar Allah,NA BAKI TABBACIN HAKA_*
*DANNA RUBUTUNNAN DON YIN MAGANA DA ITA KAI TSAYE*ππΎππΎ
wa.me/+2348103155915
KO KI KIRATA TA NAN
08103155915
153
Har yanzu da take zaune saman wheel chair din bata daina qoqarin motsa kowacce gaba ta jikinta ba,duk da hakan baida wani amfani ko qanqani a tattare da ita,kaman yadda bai kawo wani ci gaba a yanayin da takejin jikinta ba. Ta sake tattara duk qarfinta a karo na babu adadi don ta samu koda bakinta ne ta motsa tayi magana,amma kamar dai mintunan da suka shude ko motsi bakin baiyi ba bare akai ga fitar wani sauti.
"Innalillahi......na shiga uku!" Shine abinda ta furta cikin zuciyarta,don babu damar yin magana a bayyane bare wani yaju furucin nata.
"Wai da gaske ne?,da gaske ne ni mariya?,bazan iya yiwa kaina komai ba?,da gaske ne ni mariya bazan iya tafiya ba?,da gaske ne ni mariya bazan iya yin magana da kowa ba bare a jini ko a fahimceni?" Tambayoyin kenan da suka cika mata kwanya da qirji tsahon kwanaki ukun kenan,kuma bata da wani me iya jin tambayoyin bare ya amsa mata.
Tun daga kwanaki ukun zuwa yau ko sau daya bataji ta gamsu ko ta nutsu da maganganun likitocin ba da suketa maimaita maganar hawan jini ne wai ya kamata ba. Tafi amincewa da cewa tabbas wannan abun daya sameta jifa ne......asiri ne kawai akayi mata saboda kada taci arziqin d'anta. Mutum biyu take zargi,hajja harira ko ameena hamza kibiya.
Duk duniya wadannan mutanen biyu bata da wani abokan adawa sama dasu,bata da wani abokin takun saqa sama dasu. Duk da kuma tana zargin ameena din,amma zargin nata yafi qarfi akan hajja.
"Na rantse da Allah na warke hajja bazaki sha ba.....ba zaki tsira ba....ko ke ko ameena duk wanda yake da hannu cikin maida rayuwata abun tausayi cikin qididdigaggun daqiqu" Taci alwashin cikin ranta tana jin wani abu yana tokare mata a wuya me tsananin zafi.
Checking nata likitan yakeyi yana rubuta bayanan cikin folder dinta yana hada mata da bayanai duk da yasan bawai zata iya bashi amsa bane,amma yasan tana ji tana kuma fahimta,maidawar ne ba zata iya ba. Duk abinda yake fadi sam bata bashi hankalinta bama bare ta tantance ma'anarsa,a nata ganin maganin warware sihiri tafi buqata fiye da wadannan tarkacen na'urorin da aka zube mata aka. Tayi imani ba wani hawan jini daya sameta,kawai komai da akeyi din wani bata lokaci ne na daban,tunda ko hanyar bakin zaren bata ganin alamun daukoshi.
Kaman kowanne kebantaccen dakin asibiti me cike da tsari shima haka yake. Gadaje guda biyu qananun sofas guda uku da plastic chairs guda biyu suma.
Yadda idanunsu suka sauka a kanta haka itama idanunta suka sauka a kansu. Wani zazzafan abu ya taso ya lullube mata zuciya.
Sosai ta kafe sabreen da idanu tana dubanta ba tare data dauke dubanta daga kanta ba ko na second guda. Ita kadai tasan me takeji akan yarinyar......tana kallonta a matsayin silar komai.....tana dubanta a matsayin wadda ta assasa mata dukkan wata musiba da take ciki. Gaba daya maganganu akanta da boka ya gaya mata suka fara dawo mata d'aya bayan d'aya.
"KINYI KUSKURE!" Kalmar farko da ya fadi mata kenan a kanta,ashe tabbas da gaskiyarsa......da gaske yake kuskuren tayi.....to amma koma meye wannan kuskuren zata tabbatar ta maidashi kansu muddin lokaci da dama suka sake waiwayarta.
Abubuwa ne da yawa suke yawo a zucoyarsa da idanuwansa sanda suka iso gabanta. Kallon da take binsu dashi tana raba idanunta tsakanin fuskarsa da tata kadai ya gaya masa komai. Akwai maganganu masu yawa saman harshenta,akwai saqonni masu nauyi cikin zuciyarta wanda dama bata bata daman furtasu ba......saidai duk wani yanayi nata.....duk wani motsi nata karantaccen abune a wajensa da koda da idanu tayi magana zai wahala ya gaza fahimta.
"Sannu" Ya furta mata yana dubanta. Ido ta lumshe sannan ta budesu,qwaqwalwarta na dawo mata da haduwarsu ta qarshe. Maganganunsa da sam basuyi mata ciwo ba kaman yadda babbar damar daya bata ta kubce mata tayi mata ciwo......wata irin gagarumar dama da bata tunanin zuwanta da subucewarta haka lokaci guda ba.
"Barka da zuwa sir" Likitan ya fada cikin girmamawa.
Waiwayawa fu'ad yayi ya kalleshi.
"Yauwa sannu da qoqari" Ya fadi yana jawo kujera gaban gadon maamahn.
Sabreen ya waiwaya ya kalla sannan ya kalli kujerar.
"Zoki zauna" Ya fada cikin nuna kulawa. Nauyi abun yayi mata,sai takejin kamar idanuwa ne da yawa a kansu. A darare ta matso tana tsarkake sunan Allah ta zauna,tasbihin da tunda ta shigo dakin takeyinsa da kallo daya data yiwa maamah. Tsaf kamannin maamah din suyi wani irin juyewa,qasa da awa saba'in da hudu kacal?,iya wannan ya ishi bawa girmamawa ga ubangijinsa da kuma sallamawa lamarinsa. Tsoron Allah taji yana sake shigarta,wani bangare na tausayin maamah din ya karyo mata.
"Sannu.....ya jikin?,Allah ya mayar kaffara" Ta furta a hankali tana son karantar yanayin kallon maamah din a kanta.
Kafe sabreen din tayi da idanuwa,tana jin wannan dubiyar da addu'ar gaba daya akwai isgili a cikinta. Akwai maganganu masu yawa data jima tana tanadin gaya mata,akwai maganganun data tanada saboda rana irin wannan.....ranar sa sabreen din zata tona mata asiri,ta kuma yaye lullubin sirrin dake tsakaninsu wa fu'ad......a ranar ta tanadi abubuwan fada masu yawan gaske a kanta. Saidai kuma ranar tazo mata da wani babban akasi......akasin da babu daman cewa komai gareta,sai kallo da da idanu,dukkan wasu kalmomi nata suna mata kai kawo tsakanin qirjinta da wuyanta amma fitarsu ya zame mata wani jan aiki.
Kallon fuskar sabreen din kadai wani gagarumin baqinciki yake ajiye mata,saidai sanda ta dauke idanun nata da zummar kauda kanta sai suka fada kan dan matashin cikin dake kwance a jikinta wanda batasan sanda har ya fara bayyana kansa ba.
Kulle idanun nata tayi tana jin yadda bacin rai yake hautsinewa a qirjinta yana kuma bin kowanne sashe da jini ke gudanar mata yana aike mata da saqo kowanne sashe na jikinta. Batajin zata iya ci gaba da kallonta zaune haka a gabanta,inda tana da baki da zata gaya mata cewa ta tashi ta matsa daga gabanta ne,amma bata da wannan damar yanzu haka banda ta kulle idanun.
Sallamar da aka sakeyi ita ta tilasta mata sake bude idanun nata. Musaddiq ne a gaba,amna na biye dashi a baya sanye da baqar abaya data fito da hasken amarcinta da kyau,duk kuwa da 'yar rama kadan dake tattare da ita. Kallo daya tak zakayi mata ka karanci a tsorace take,tana daga bayan musaddiq din,duk inda ya tsoma qafarsa ya dauke nan yake ajiye tata. Hannunta riqe da nashi hannun daya bar mata shi ta baya a haka suka shigo.
Kan hannun nasu idanunta suka fara sauka,wannan karon yunqurin miqewa tsaye tayi ta gwada tata jarumtar na UWA kuma wai MAHAIFIYA,saidai kuma kash......ba wani abu nata daya motsa balle akai ga batun tashin. Gumi sosai ya dinga karyo mata saboda abinda takeji a zucoyarta,bala'i da masifa ne fal idanu da zuciyarta,donme musaddiq din zai debo mata diyar alhaji hamzan yazo mata da ita?,auren da sukayi kadai bai ishesu ba?,har sai sun qara qunsa mata baqincikin ganin kasantuwarsu a tare?.
"Akwai buqatar ki saka nutsuwa da kauda duk wani bacin rai daga zuciyarki don a samu a ceto lafiyarki yadda ya kamata" Likitan ya furta yana dubanta,gumin dake fita a fuskarta kadai ya gaya mishi akwai wani abu daya motsa zuciyarta,duk da baisan ainihin meye ba.
Tana labe a bayansa suka qarasa gabanta,ya gaidata gami da yi mata sannu. Leqowa amna tayi daga bayansa tana mata sannu itama,suna hada idanu ta koma bayan mijinta ta lafe. Ko kusa ko alama bata qaunar ganin matar,anni ce ta kirata ba tare da sanin musaddiq din ba tayi yaqi da ita akan ta bishi idan zaije ta dubata.
"Komai lalacewar tuwo ba'a sauya masa suna.....musaddiq baida wata uwa bayan mariya,koda ya nuna miki baya sonta wannan wani yanayi ne ya kawo haka.....batun abinda tayi miki kuma darajar addu'a bata samu galabar komai a kanki ba,sannan kuma hakan ya zame mata wani sanadi ne na tonuwar kowanne sirri....kina tunanin ke kika yiwa kanki haka?,ko kadan,darajar addu'a ce da duban zukata da Allah S W T yayi". Wannan maganar ita ta sanya amna yin qundumbala ta biyoshi.
"Any progress?" Fu'ad ya tambaya yana duban likitan. Ajiyar zuciya kawai ya sauke sannan yace.
"Idan zai yuwu muje muyi magana daga office ko?" Juyawa fu'ad yayi ya yiwa musaddiq inkiya,shi kuma ya waiwaya yana duban amna. Muryarsa can qasa cikin sigar lallashi ya fara magana.
"Calm down dear......ga adda sabreen ku zauna tare da maamah......ba abinda zai sake faruwa,yanzun zamuje mu dawo.....okay?" Ya fadi yana dage mata dukka girarsa gami da riqe fuskarta tsakanin hannuwansa. Kai ta gyada masa,sai ya sake mata murmushi yaja da baya yana juyawa gami da bin bayan fu'ad. Saura kadan numfashinta ya qwace mata,wani tashin hankali ya sake sauko mata.
"Shima musaddiq din haka yake?" Maamah ta tambayi kanta. Wani irin yanayi ne da batasan musaddiq dashi ba,soyayya muraran da mace a gabanta?.....wacce irin baqar rana ce wannan take gani?. Dukka yaranta guda biyu da iyasu ta mallaka a duniya,kowannensu ya dulmiya cikin soyayyar wata diya macen daban ba ita ba?,wani irin so me zurfin da bataga kwatankwacinsa a kanta ba a cikin idanunsu?.
Shuru dakin ya dauka,sabreen tayi qarfin halin sakin murmushi ta kalli amna.
"Ga guri ki zauna amarya.....kada angonki yazo ya tuhumeni na bar masa me a tsaye" Ta fadi tana ganin yadda amna din taqi sakewa. Ita kanta ta zama tamkar baquwa a gurinta. Murmushi ta maida