Kuruciya Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Untichlobanty Category :  Complete Novels

Chapter   5 / 45

12K to 15K   out of 134.5K words

look like.........

Then the looks and presence of those horrible and terrifying,wicked dogs

The dogs chasing her is the biggest fear of her life

Her falling into the pool.

That one is called helplessness....................

Wata maid me suna tala (mai shara)ce ta sa'a tsumman a ruwan zafin ta matse sannan ta fara goge ma fiskanta

Wani nifashi taja kan ta sauke hawayen wahala suka fara zarya a idonta yadda kasan ruwan sama

Cikin 2 min harta jika hijabinta ta fara jika pillow da hawaye

Maid uku ne Dama a dakin da take daya da first aid,daya bowl din warm water,daya kuma tea and toasted bread

Dukkansu idonsu ya ciko da kwalla musamman da suka ga yadda minal take kuka

Wani mahaukacin atishawan data watsa ne ya dawo dasu saga duniyar da suka fada na halin da take ciki

Katrina wacce take baturiya itace first aider na gidan

First aid box din ta bude sannan ta ciro su cotton,dettol,spirit,iodine,and Bandage.

Treating ciwon ta fara aiko ana fara goge jinin minal tafara yarfa hannu

(nace tabdi tun ba'a saka alhaji dettol da oga iodine)

Yamutsa fiska take yadda kasan mai nakuda

Dettol aka saka domin ayi disinfecting aiko wani kara ta sake ta mike a take tana Cewa

Dan Allah Kiyi hakuri,wallahi ni Ba mai lafi nace karki min mugunta

Itadai Katrina ganin bats gane Ba sai ta kalli sauran with a questioning look

Fassara mata sukayi kamin tace oh sai tacewa minal din

No no my dear am gonna harm you,impact am being gentle with you

Minal dai anzo gurin domin bata gane ko Abu daya data ce Ba

Hasali ma banda harm babu abinda taji sai ta dauka Cewa tayi me yasa ta Tara gashin hammata yana damunta da wari

Nuna kanta tayi da yatsa cike da takaici tace yanxu bayan cinzarafin da oganku yamin,da iriyar muguntan da kike mini shine harda cin fiska?

Ina ruwanki da gashin hammatana?

Tala ne tace Kamar ya?

Minal tace inba wulakanci Ba shine zatace hammata na yana wari Wai na tara gashi.

Tala ta dan dara kamim tace kai da abin dariya kike wallahi ai Ba haka take nufi Cewa tayi..................

Kara kai minal tayi alamun gamsuwa tace kiyi hakuri.

Katrina ta gane me tace domin zama a cikin su tala.

Dukda Cewa dakinsu daban amma ta Dan Koyi wani Abu a Hausa

suma dai su tala dasu maimuna dasu Rabi a primary suka tsaya zama da irinsu Katrina dasu Susan yasa suka koyi English

Sai tace is okay

Cigaba tayi da treating ciwon Inda minal keta tsala ihu tana raki

Lokacin da ta gama minal ta Dade da wanka da ruwan majina da hawaye

Zata fita ne ta tana fiskanta domin tace mata take care amma me zataji zafi radau Kamar garwashi.

Atake tace oh my god your temperature is so high I must give you an injection

Dan! Dan!! Dan!!!........

Minal tasan sunan allura ta English gashi matsoraciyar allura ne

Aiko zazzare ido ta fara kama mushriki yaga mala'ikan mutuwa.

(Wasu they prefer injection but to me that's a total and absolute NO. )

Ciro allura Katrina tayi ta soma jan ruwa. Wani wawan tsalle minal ta daka daga kan gadon Wanda yasa ta fado kasa tare da kwale kafanta ihu ta kurma.

Ta diba a guje binta sukayi aiko ta fada bandaki ta masa key sannan ta zare

Bubbuga kofar suka fara itako Cewa take wallahi ko su baba basu iya sawa ayi mini allura .

Ko agida har saman bishiya nake hawa har Katanga nake haurawa Dan na tsira sai nan da yakeda wurin buya masu yawa? juyawa tayi domin taga Inda ta Shiga

Sink ta fara daura idonta akai wanda ya mata Kamar tasan abin amma ba'a haka tasan shi Ba

Jacuzzi ta kalla sai tace laa irin bahon gidan aunty fauziyya amma na masu kudi

Toilet din ta kalla tace la wannan ma irin salgan bayinta Saide shima na masu kudi ne

Yasin gwanin kyau bayin Kamar kayi bacci a ciki.

Bude kofar bayin da akayi yasa ta juya Katrina ta gani da allurarta ta a hannu tare da tala,da Rabi.

Wani mahaukacin ihun data kwalla yasa su murja, atine, meramu, safiya, Hauwa, Jenifer,Susan,Emma,rabecca,sanjana,suyunjin and others shigowa dakin domin in kaji ihun zaka rantse yankata akayi

Yazeed's pov

Yana kwance a gadonshi yana nazari har bacci ya kwasheshi.

Sama sama cikin baccinsa Kamar a mafarki yakejin ihu hakan yasa nauyin baccin ya fara saukowa daga kanshi amma bai tashi Ba

Ihun da ta kwalla yasa yayi wani mugun zabura yana zazzare ido yana muzurai domin shi ya dauka wani abin ne ya faru har ya zama ready to fight.

sai ya sake jin an kwalla wani kara,iska yaja yace ya Allah wannan wata iriyar yarinya ce haka

ta mayar min da gida Kamar mental asylum

Fita yayi ranshi a bace jijiyan kanshi duk sun tashi

Minal kuwa lokacin ta nuna Kamar tayi surrender ta fito saboda ta fahimci basuda imani zasu iya matseta karfi da yaji a danna mata karfe a jika

Rabi ne tace ko ba ke Ba fah kinga lafiya zaki samu Indian Anyi allurar

Kuma sir yace kije ki sameshi gashin bayason jira danma yasan asume kike

Katrina ce ta matso da allurar zata mata domin har ta fara gajiya da wannan hali irin na minal

supan data watsa izuwa kan gado tare da kwala ihu yayi daidai da shigowar yazeed

Fuskar nan murtuke babu annuri ko kadan yanda kasan bai tana dariya tunda aka haifeshi

Ihu daya bazo mata shi yayi sanadiyar makalewar tata sauran ihun

Shiga dakin yayi sannan ya fincikota daga kan gadon yayi wajen da ita janta yake..............

Finally!

thank you so much for bearing with me

Good night

17 June 2019

Your sweetheart

Mzz untichlobanty馃挄

[1/11, 1:47 AM] Mzz_Untichlobanty馃挒: 馃弳馃弳KURUCIYAR MINAL馃弳馃弳

By miss untichlobanty

*CHAPTER 13*

Janta yake tana turjewa "Dan Allah oga sir kayi hakuri ka rabu dani wallahi bazan kara ba, na tuba,na tuba!"

Abinda taketa fada kenan tana kokarin zare hannunta daga nasa domin tasan idan ya kaita Inda sai kaita bazataga da kyau Ba.

Store room yayi niyyan kaita.

Atish!aaaaatiiiish!!aatish!

Atishawan da take sirnanowa yasa ya fasa kaita domin yasan ta fada ruwa sanyi ya kamata ga kuran store kuma?

Maybe ma she is asthmatic. Hakan yasa juya ya canja hanya zuwa side dinshi.

Ihu take tana bashi hakuri amma Allah cikin ikonsa wannan Karen ma hawaye sun dauke kafa

(Nace kekam minal kinga ta kanki sanda ake bukatar hawaye sai su kafe sanda ba'a bukatarsu kuwa yanda kasan ruwan sama me saka ambaliya)

Bakin wata kofa wacce take barin dama da dakinshi kuma next to it ya bude. Wulla ta ciki yayi ta fada kasa sannan shima ya Shiga.

Bakin gado ya nema ya daba mazaunansa sannan ya kalleta yace knee down!babu bata lokaci tayi Kamar yadda ya umarta jiki na rawa

Sai alokacin yakalleta da kyau yarinyace sosai.

Sama da kasa yamata aranshi yace kwailace ma amma she has the guts to..........iska ya fesar a bayyane yanaci gaba da kallonta.

Itako ganin ya tsare da ido yana mata kallon tsana yasa jikinta yayi sanyi Ashe bazata kara ganin innarta da baba Ba? gashi ya Abubakar ma ya kusa dawowa nanda wata shida shima bazata gansa Ba?

Gashi dije ma takusa dawowa saga boarding Ashe bazasuga juna Ba?

Ashe ajalinta ne ya fito da ita?dama mafarkin mutuwa da taga tayi Ashe zai zamto Gaskiya?

Maganar da yazeed yayi yasa ta dawo daya tunanin da take.

Ke?kin iya up and down?

Harara ta banka mai yasin bazanyi Ba

Kallonta yayi da mamaki da kuma takaici Wai ita bakinta baya mutuwa ne?shi tunda yake banda zakiyya babu mai iya kallon idonta ma tamasa magana balle tsiwa ko zakiyya ma tasan lokacin da take haukanta. hmm zaiyi maganin yarinyarnan da alamu kanta yana rawa.

Hannu yasa ya dalle Bakin Wanda yayi sanadiyar fitar jini kamin yace

Mike ki fara up and down!

Jikinta na rawa ta fara kwanciya yayi ya rufe idonsa fuskarsa na kallon sama.

Sanda tayi kusan na Minti Biyar alokacin ta gama had a gumi sannan ta dubeshi tace oga sir kayi min rai

Wallahi bani kara maka rashin kunya jin shiru ba'a amsa mata Ba yasa ta tsaya da punishment din ta sansado ta leka fiskarsa ganin idonsa a rufe yasa tace

Kutma lallai ma mutuminnan Dan rainin hankali ne.

wato ga inji ko?inyita aiki shi yana bacci,wallahi Allah ya isa na.

Sanda takeyi harta iso Bakin kofa zata fita taji yace

Da izinin zaki aikata hakan?kuma Waye Dan rainin hankalin?

Juyowa tayi a zabure tana zare ido dama Ba bacci yake Ba?

Wayyo Allah bakinta yaja mata.

Zama yayi yace dawo ki zauna.

A hankali take takowa Kamar kazar da kawai ya fashewa a ciki harta tsuguna

Gabansa ya Muna mata ta matso tana zare idanu harta rame Kamar Ba ita ba.

Yazeed yace dago kanki dagowa tayi amma idonta a kasa.

Yace Nayi kama da sa'anki? Ta girgiza kai.

Yace kinada matsalar kwakwalwa ne?ta sake girgiza kai. Tsawo ya saka mata yace use your fucking mouth聽!

Itadai bata gane ba saboda accent dinsa ya mata tsauri amma sai tayi shahada wajen Cewa kayi hakuri.

Yace kintaba ziyartar gidan mahaukata ne?domin kinyi kama dasu

A ranta tace kutma wallahi ni banyi kama da mahaukata ba Saide kai ne mahaukacin.

Kaine mahaukacin shi ya bayyana azahiri wadda bata聽masan ya fito ba

A fusace ya mike ya yarfe ta da mari yace nine mahaukacin ?tana girgiza kai tace tace a ah dan Allah na rokeka kayi hakuri subutan baki ne bazan kara Ba. Ball yayi da ita ya fita tare da sawa kofar dakin lock yana ma fadin zan nuna miki hauka yar budurwa!

Koda ya fita waje idonshi yayi ja lukman ya gani yace ya kawo masa igiya

Cike da mamanki lukman din ya dauko igiyar yana nazarin me ogan nashi zaiyi da igiya? Dan shi baiga alamun saniya a gidan Ba lol.

Saniya minal za'a daure

Jin shiru bai dawo Ba yasa ya kwada masa kira domin ya tsani waste of time.

Da gudu yazo a kasa da da'ki'ka 2 domin Dan tazarar dake tsakanin聽 side dinsu da kuma main one

Miko masa igiyar yayi yana Cewa oga yaushe za'a mayarda yarinyar?

Yazeed yace my friend, get out of my side!

Har lukman ya fara tafiya yazeed yace zonan.

Dawowa yayi yace masa ya batun Jamal din Ba nace a dauko shi Ba? Lukman yace su bala ne suka tafi Daukoshi.

Juyawa yazeed din yayi ya tafi Ba tare da ya tanka masa Ba.

Shiga dakinsa yayi ya samu minal Inda ya barta tayi jugum

Ba Komai ke damunta Ba illa wani bahagon yunwa domin tana fashin sallah,Kamar dai yadda kuka sani minal muguwar acici ce.

Mu hadu a next chapter domin jin yadda zata kaya tsakanin minal da yazeed.

Thank you!

18 June 2019

Mzz untichlobanty馃挄

[1/11, 1:51 AM] Mzz_Untichlobanty馃挒: 馃弳馃弳KURUCIYAR MINAL馃弳馃弳

馃尮By miss untichlobanty馃尮

*CHAPTER 14*

Tsugunawa yayi a gabanta yace kawo hannuki !

Kallonsa take a ranta tana Cewa dama oga sir Dan iska ne?

Dama yawanci sojojin nan mazinata ne ga shan giya da sigari

Dan iska me zibin samudawa

Tafadi hakan a zuciyarta domin it a atunaninta wani abin zaiyi da hannunta domin tun batakai haka Ba inna ke ce mata duk namijin da ya tabata bada sannin innar Ba to Dan iska ne amma banda baba da ya abubakar

Tsawa ya daka mata aiko ta miko hannun nata. Igiyan ya fara shirin kulla mata ai atake ta fara kuka da hawaye

Kallon ta yayi kamin yayi murmushin gefen baki yace:

Ashe de baki cika jarumar Ba

ai nadauka taurin kanki bazai bari kiyi kuka Ba.

Ajiye igiyan yayi a wajan ya fita daga dakin ya jirkita pin din ya rufe.

Kuka ta fashe dashi tana burburwa a kasa har ciwon dake hannunta ya fara jini bata saniba

Wani sautin da cikinta ya bayar shi ya tuna mata da cewar bataci abinci domin sau biyar takecin abinci banda kananun kwamulashe da take yi

Tunawa tayi da wani lokaci

Flash back

Inna Wai haryanzu baki gama miyar bane nifa kinsan bama er mutunci da yunwa

Inna dake kitchen tace Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un

kinga ni ki rabu dani kinfiso Nayi irin wannan miyan naku na 'ya'yan yanxu

Amina ce tafara waka tana buga gwannon hannunta da

Iyya yunwa batada kara,iya yunwa ba'a mata lahaula,iya yunwa batada Sabo wayyo iya yunwa na iya karwa Iya yun..........

Muryan inna ta jiyo wadda ta leko tana kallon ikon Allah

ta Ce to ai bazansan kinajin yunwa Ba sai kin fara bin makwabta

Turo baki tayi tana guna guni ta mimmike kafa a kofar daki tace

inna shiyasa nace kiban na dafa kika ki ki Duba fa yadda dare tayi

Inna tace wai karfe biyar kike so na dinga gama abincin dare ne ?

Kara turo baki Amina tayi tace inna to ai.........

Sallaman da baba ya Watso shi ya sa ta antayo da guru tana Cewa baba sannu da zuwa

Yayinda take turo baki ta huhhura hanci

baba yace :

Uwata ya akayine?

Minal tace inna ce had yanxu bata gama abinci Ba gashi yunwa nakeji gashi had dare yayi

Murmusawa baba yayi yace uwata yanzun ne dare yayi?karfe 6:30 ai beyi Ba

kinga dauko mana taburma

Taburman taje daukowa yayinda inna ke Cewa

mallan an shigo kenan,ya aikin?ai wannan sususun bata ma bari min gaisa Ba

Baba yace Alhmdllh ,uwartawa ce Ba tada dama muryarta suka jiyo ta leko ta taga(window) tana Cewa

Allah ya kawo Mani har kunnena gulmata akeyi ko?

Dariya suka fashe dashi yayinda baba yace ja'irar yarinya kasa kasa

Inna tace malam bara in kawo maka ruwa

Sai a lokacin Amina ta fito ta shimfida tabarmar yayinda baba ke Cewa

ina Kanwar taki deeje ko duk gajiyar makarantan ne?

Tace Ba wata gajiya baba tana can de tana abinda aka saba baccin asara

Baba ya Dan dara yace gaba de baccin asara ai tana kokari kayi kusan wata hudu a makarantar kwana (boarding) baka ganin iyayenka ga wahalar labour ai dole tayi bacci

Labulen da aka banko ne yasa suka dago dukkansu suka kalli kofar

Deejeh ce ta fito tana watsa hamma Amina ta dauje bakin tace ke dallah rufe mana shegen bakin naki me zubin sokawe

Dije tace a ah salga ne Ba sok..............

Ai bata karashe Ba taji bugu.

Babane yace uhm yarannan bara kuga, ya mike ya tafi waje domin yayi alwala yaje masalti ya samu falalar jiran liman domin yasan idan suka fara Toh sai Allah.

Kayi magana Kamar kana zugasu kayi duka su dau gaban duniya su daurawa juna

Inna da ta dawo da ruwanta a hannu ta taradda tabargazan dake faruwa nan ta saita ma kowanne notin kansa

Nan suka ballawa kuna harara wadda yake nuni da mun daura gaba.

Innako takaici ya mata yawa

Amina akwai gajan hakuri,saurin hannu da tsiwa

itako khadijah fitsara ta mata kaka tuku a tsuliya

Bayan baba ya dawo daga masallati nan ya dauko ledan daya shigo dashi dazu yace

Uwata d'azu dazan dawo isubu mai gashi yaban tsirannen yace na kawo miki. Minal tace kace Allah ? Tana mai jin dadi.

Inna ce ta shigo da farantin tuwo malmala biyarne a ciki ta ajiye.

Washe hakwara Amina tayi tace kai inna kin kyauta wallahi Dan Nasan bazan iya kara minti 30 me kyau Ba yunwa zata kar ni

Bude naman baba yayi yanke 5 ne Dan haka ya mikawa minal yanka uku ta karba tana Washe baki sannan tace na gode. Yanka biyun ya mikowa deejeh wacce keta cika tana batsewa,Inna na zabga mata harara.

Juya kai tayi tace bataci tunda na Amina ne girgiza kai baba yayi kamin ya mikawa Amina yanka daya.

Karba tayi ta ajiye akan ukunta alokacin har ta cinye Mara daya ta yanko wani loma kenan baba yace

Haba mana uwata ci ahankali ai Mara biyun duka naki ne wannan lomar aiko katan gardi meji da karfi a jika albarka.

Itadai Amina ko ta Kansu bata bi Ba wani loman ta yanko Wanda yafi na farko zatakai baki idonta ya fada akan iyaye nata

Gani tayi sunata fafatawa da yanka daya Ashe ma me kitse ne.

Hawaye ne suka cika mata idanu kawai sai ta dauki daya dake gabanta takai baki.

Wani kara ta saka duk hankalin su ya dawo kanta

Ajiye musu musu ukun tayi kuma manya ne tace baba gashi kuci banaci hakorina

Inna tace kici dai sai kici ta dayan gefen tace a ah na koshi

Mikewa tayi ta fita ayayinda take leko su

Allah ya gani tanason ci amma bazata iya cinyewa iyayenta suci kitse Ba.

Wanke hannunta tayi taje ta kwanta Dan already tayi sallan issha'i

Can wajajen karfe 10 lokacin gidan yayi shiru alamun sun kwanta.

Sanda tayi ta bude kofa ta shigo falon iyayen nata Inda aka rife guntun abincin aka ajiye a saman fridge tunda Ba nefa danma garin da sanyi

Ahankali ta bude farantin aiko taga sunci sun bar yanka 2.

Dauka tayi ta gutsira wani lumshe ido tayi harda girgiza kai tana murmushi sannan ta dauki cabbage ta harba tare da kuli kuli.

Inna da baba dake labe Suna kallonta domin sunji sanda ta bude kofan suka kalli juna komawa ciki su kayi suka zauna bakin tsohuwar gadonsu hawayene fal idon inna.

Tace ashe babu abinda ya sami hakorin nata kawai dama so take iyayenta suci?

wani kaunar minal ne ya Kara dabaibaye mata zuciya. Baba yace aini Nasan Ba abinda ya sami hakorin domin naga sands ta dago taga abinda mikeci idanunta suka ciko da kwalla Nasan zatayi wani abun

Shi yasa nace miki mubar yanka 2.

Rungumesa innar tayi kamin ya rarrasheta suka kwanta zuciyarsu fal cike da son

5 / 45