Kuruciya Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Untichlobanty Category :  Complete Novels

Chapter   18 / 45

51K to 54K   out of 134.5K words

ta nufi dakin yazeed domin yi masa tausa Kamar yadda ya umarta.

Koda tazo kofar dakinshi bude kofar tayi a hankali domin so take ta bashi tsoro Kamar dai yadda yara keyi.

Abinda kunnenta ya jiyo mata shiyasa ta tsaya cak tabbas Ba karya bane yazeed ne ke waya yana magana Kamar haka:

"Great aikinka yayi kyau ina alfahari dakai" wani aiki ne yayi kyau?

Wai tayaya kukayi ne?sukayi me?karde abinda nake tunani ne?kai noo yazeed bazai tana kokarin kasheni ba. Wata zuciya ne tace mata kin manta ya tsaneki? To amma in so yake ya kasheni me yasa ya CeCe ni? Kuma ai shima yasha.

"Shekewa yayi da dariya yace kadan ma tagani" tabbas damirin sunan mace yake aiki dashi towai me yake magana akai?

Ganin bazata sami answer dinta Ba yasa tazo gabansa tace ya yazeed dama so kake ka kasheni?

A zabure yazeed ya dago yana kallonta ido cikin ido..............

馃尮馃崁馃尮馃崁馃尮馃崁

Zakiyya zaune gefen wata farar budurwa fat sai sharar kwalla take,Ba laifi tafi zakiyya kyau amma da kaga farinta kasan Ba na Allah da annabi bane.

I am sorry sis! Shine abinda taketa maimaitawa tana shafa bayan yarinyar wacca bazata wuce shekara 21 Ba.

Budurwacce ta kuma share kwalla tace Wai yanzu haka lukman dina yana tareda wata ko?

Girgiza kai zakiyya tayi tace baya tareda ita tunda kince baya sonta nima yazeed dina yayi auren amma ko kallon arziki baya mata ranan da na taho har jibganta yayi. Kidena kuka kinji sister AYUSH?

Let me kuku run for my life before ayi min duka dan yau Nasan zanbar fans Suna tsimayi na

Expect me soon!

Anyway result dinmu ya fito kuma it was masha Allah no problem.

Thanks for your du'as love yah馃槝

@mzz_untichlobanty 馃挄

26 November, 2019.

[1/11, 2:28 AM] Mzz_Untichlobanty馃挒: 馃弳馃弳KURUCIYAR MINAL馃弳馃弳

馃尮by @mzz_untichlobanty馃尮

*CHAPTER 46*

Wasu hawayenne suka kuma zubowa Daga idanun ayush sannan ta girgiza kai tace sister zakiyya karki bani fake hopes Dan Allah kinsan namiji abin tsoro ne ta iya yuwuwa yanzu haka yana tare da amaryarsa ya manta dani.

Shafa kanta zakiyya tayi cikin murya mai laushi da nuna Cewa ta damu da yanayin da cousin dinta ta Shiga tace little sis have faith kinji ? I know that you are brave, ko sanda parent dinki suka rash you were so brave right ? Gyada kai ayush tayi zakiyya tace Toh kin bani you can go through it and kinyi trusting lukman dinki ko? Ayush ta kuma gyada kai tare da Cewa eh kamin wani hawayen ya silalo zakiyya tace good since have trusted him and you are sure that he loves you then there is nothing to worry about dago da manta tayi ta kalli zakiyyan tace are you sure?zakiyya tace 100% sure now give me a smile kinji?

Murmushin dole tayi zakiyya tace ko Ba ke bafa now tashi muje kick abinci.

Girgiza kai tayi tace banajin yunwa, hararanta zakiyya tayi tace zaki tashi ko yaya? Mikewa tayi tana Cewa sis wannan kallon ai sai ki cinyeni dariya suka fashe dashi kamin suka wuce dinning area domin cin da'am.

馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

What!? Minal me kike nufi me zaisa in kasheki? Harara minal ta aika masa kamin tace abubuwa dayawa. Wato dama duk wannan abubuwan dakake min kanayine saboda in na mutu kar a zargeka?minal ta fadi hakan tana mai daga murya.

Tsawa yazeed ya daka mata ya daka mata yace banson hauka fah kodan kings ina Daga miki kafa shine zaki kawo mini rain in hankali ? In da inason na kasheki ne da tuni na kasheki.

Hararar sa tayi da rinannun idonta muryarta na rawa alamun zata iya fashewa da kuka at any moment tace amma wallahi bantaba nadamar aurenka Ba irin yau Nayi kuskure Dana yarda dakai Ashe Dama kai me kisan kaine? Ashe kasan abinda ka tanada shine harda cemin Wai mu zama abokai,Dama zaka iya min haka? zuciyata ta raurawa har yanzu na kasa yadda Cewa kanason ka kasheni, ya yazeed ka tasheni kacemin mafarki nake Ba dagaske bane,Ba kasheni kakeson yi Ba.

Tsintsiyar hannunta yazeed ya kama ya jata har izuwa bakin kofar dakinsa sannan ya wancalar da ita yace Anyi kokarin kashekin Kiyi abinda zaki yi sannan ya rufe kofarsa.

Wani irin zafi zuciyarsa ke masa Wai yau shi YAZEED ABDULMAJEED UMAR aka Cewa yana kisan kai? Da alamu sakarwa yarinyarnan fuskar da yakeyi ya janyo masa matsala.

Zaiyi kokari ya nisanceta ko tayaya ne domin ta fahimci kuskurenta sannan ta fada hakuri kamin ya yafe mata.

Wata zuciyar tace uhm tunda kuke da zakiyya ta taba baka hakuri ne inba tanada wani agenda ba.

Sai alokacin ya tuna da zakiyya yace ko ina ta Shiga oho bako waya? I will call her tomorrow.

Da sake sakennan ya fara bacci tare da aiyana irin azabar dazai ganawa Jennifer harsai ta fada masa Wanda yasata wannan aika aika.

.................

Minal ko yana rufe kofarsa ta fashe da kuka. Sanda tasha kukanta ya isheta sannan ta mike taja kafafunta jiki a sanyaye taje dakinta. Itakam ta Shiga uku da rayuwarnan da badan kartayiwa Allah butulci Ba da tace inama ta mutu Dan wallahi sanda wannan abun ya farune ta fahimci ta fada tekun son yazeed dukda ko bata tana yin soyaiya Ba amma dai ai tasha jin abubuwa akanshi gashi ita Ba takaddun Hausa take karantawa ba, wannan sai zaliha wani ajiyan zuciya ta sauke me nawi tunawa da zaliha da tayi ko yanzu a wani hali take oho, sai yanzu ta fahimci ciwon da zaliha keji.

Yanzu da ace ya yazeed ne ya zatayi? Dukda ko yayi kokarin kasheta wallahi itanasonshi a hakan ma. To kode tayi kuskurene? Kode bashi yakeson ya ya kasheta ba? Kode wani zancansa daban yakeyi ? Kai ya cancanta ta bashi hakuri sannan ta nemi Karin bayani tunda ko a musulunci babu kyau zato.

Kallon sama tayi tace astagfirullah Allah na tuba,nikam naga takaina karfa in mutu yau mijina na fishi dani.

Mijina? Kai Ahe ban taba kiransa da mijina ba ta fadi hakan tana Washe hakora Kamar ba ita ta gama drama yanzu ba.

Kai Gaskiya bani iya bacci in banbashi hakuri ba ta fada a magana zuci. Saukowa tayi Daga gadonta tare da Cewa gadona kar kayi kewata yanzu zan dawo kaji ? Kamar gadon yana jinta (typical me馃槀 yeah I have that kind of connection with my bed and phone.)

Sautin tafiyarta Kadai ke tashi saboda yadda gidan yayi shiru. Koda ta iso kofar dakinsa knocking tayi a hankali taji shiru ta sake knocking still shiru

Murda hannun kofar take shirin yi sai alokacin ta lura Cewa Ashe kofar batada Hannu sai wurin saka pin ta ciki ne akwai handle.

Nambobi ta fara daddannawa amma koda tayi sai uku duka wrong sai kofan yace bazata iya sa'a ba sai after 15 second itako da ba ganewa tayiba taci gaba da dadaddanawa.

.........................

Yazeed kwance a dakinsa har bacci ya fara daukarsa yajiyo taku na kara matsowa kusa da dakinshi kuma Idan ba kuskure yayi ba takun minal ne tayaya ta Shiga side dinsa ? Gush Ashe ya manta be rufe koda ba thank goodness kofar dakinsa in a rufe ba'a iya budewa ta sake sai ansaka pin da ace ba minal bace fa ?

Dawowa yayi daga tunanin da ya shiga jin minal ta fara knocking kamin kuma ta fara daddanna pin.

Yanaji machine din nata dit dit dit dit dit zu! Har sai uku alamun pin din ta is wrong amma yaji minal ta cigaba da daddanawa.

Tasowa yayi yazo bakin kofar yadda zaiyi magana ta jishi ba sai ya daga murya ba saboda girman dakin.

Yace ke dallah kibar nan wurin karki batawa mutane kofa aiko minal tanajin yayi magana tace ya yazeed Dan Allah ka bude Dan Allah baice Komai ba ya Koma yayi kwanciyarsa.

Minal ko jin shiru bai kara magana ba yasa ta jingina da kofar kamin tace Dan Allah kayi hakuri Nasan Nayi kusukure Dana zargeka ta fadi hakan tana shirin zubda kwalla.

Mamaki ne ya cika yazeed Wai hakuri ta bashi kuma ma da wur wuri haka ? Chabdi ai inda zakiyya ne wallahi saide ya mutu.

Baice Komai bayayi kwanciyarsa,can yaji Kamar shesshekan kuka wani zafi yaji zuciyarsa tamaisa amma ya daure wajen Cewa in kin gama kukan kibarmin side dina sannan karki sake ki kara zuwa inda nake.

Kuka ta fashe dashi tace Dan Allah karkayimin haka ya yazeed kayi hakuri bazan karaba.

Jin shiru yaji kulata yasa ta Koma dakinta zuciyarta cike da damuwa yanzu ita ta yaya zata bashi hakuri bayan yace bayason ya kara ganinta? Wani kukan ta kuma bingirewa dashi har bacci barawo ya saceta.

Good morning na cika alkawari,please make sure you spread a smile on my face comment and vote fah

Have a good day bye

Miss untichlobanty馃挄

28 November, 2019

[1/11, 2:28 AM] Mzz_Untichlobanty馃挒: 馃弳馃弳KURUCIYAR MINAL馃弳馃弳

馃尮by @mzz_untichlobanty馃尮

*CHAPTER 47*

Da safe jiki babu kwari minal ta fito ta fara aikinta koda ta kammala,tayi wanka sannan lokaci zuwa lokaci takan sauko ta Duba dinning table ko yazeed ya sauko domin ta share dakimshi tunda yace bayason ya kara ganinta.

Komawa tayi dakinta ta zauna Jim kamin ta janyo wayarta sai alolacin ta tuna batada numbern zaliha kawai sai kawai taje gaban madubi ta shafa powder da lipstick saboda rage lokaci Kuma tayi kyau Ba laifi.

Fitowa tayi daga dakin aranta tana Cewa Nasan ya fita ma tunda safe kuma ko na hadu da shi ma nuna masa zanyi ina fushi dashi muga yadda zaiyi. Murmushi tayi kamar wata shashasha ko yadda yara keyi Idan sun kulla wani abin.

Laundry room ta Shiga ta dauko kayansa set 2 data goge dazu ta nufi part dinsa koda ta Shiga Ba kowa kuma parlourn nasa ma da duhu alamun babu kowa tace Ahe duk jirannan danayi na banza ce bayanan ma.

Ta bangaren yazeed kuwa Kamar jira yake ta Koma daki sai gashi ya sauko, kitchen ya nufa ya dauko hollandia yoghurt plain flavour saboda na fridge din parlourn sa ya kare sannan ya dauki cup ya fita.

Dakinsa ya Koma yasha yoghurt dinsa Dan baya mood din cin abinci. Kwantawa yayi abinsa ruf da ciki yana mai kashe wutan dakin sannan ya rufe idanunsa once in a while yana murmushi.

Da confidence dinta ta tura kofar dakin Dan ba'a rufe kirif take ba sai ta dauka ko ya bar mata ne Dan tayi shara Kamar yadda yasaba bari Dan haka bata kawo Komai cikin ranta Ba ta shigewarta.

Hijabin dake jikinta ta cire tayi cilli dashi akan gado sai kan fuskar yazeed Wanda dama tun dazu yaji takunta kuma yasan ta shigo dakin amma ita batasan da zamansa Ba. Baice uffan Ba balle ya motsa yayi luf cikin bargonsa sai kansa dake waje wanda yanzu yake lullube da hijabin minal. Tunani yake aransa yarinyarna badai sa hijabi Ba kam. Allah yasa da kyakkyawar niya ce.

Ajiye kayan tayi akan stool kamin ta dafe goshinta da hannunta tace ni yanzu ya zanyi ? Kullum yananan yana budemin wannan yar iskanci kofar dakin kayan nasa to yau kuma bayanan.

Kicin kicin tayi da ido tace Idan na kamo yaya yazeed dinnan sai na naushi bakinsa. Sai kuma ta kyalkyale da dariya tace Wai wayaganni na danne ya yazeed sai jibgarsa nake.

Wutan dakin ta kunna kamin ta dauko kayan aikinta. Ganin bargon NASA a wargaje yasa tace kai Ashe ya yazeed dinma kazami ne fadin jumlar tayi daidai da janye bargon aiko atake ta kwala ihu zata arta a guje yayi saurin wantsalota ta fado jikinsa kokarin tashi take tanata tuttureshi amma ya riketa gam hannunshi ta fara mintsini tana Cewa ya yazeed ni ka sakeni nifa Ba yar iska bace. Bai kulata Ba illa ma tashi da yayi zaune sannan ya ajiyeta akan gadon couch ya Koma ya zauna sannan yace rosy cheeks gyara gadon kizo in fada miki wani Abu. Dan hade fuska tayi tace me zaka fadamin? yace sirrine a kunne ma zan fada miki tace toh..........

馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮馃尮

Zakiyya zaune a parlourn gidansu Amarya tana oiling ma ayush din gashi Wanda Ba yabo Ba fallasa.

Wayanta ne ya fara ringing ta dauka kamin tayi magana akace madam the boutique has been on fire mun kira fire service sun kashe but we couldn't retrieve our goods.

Zakiyya da batasan sanda mike Ba tace what?how comes? Are crazy? incoming call taji hakan yasa ta Duba ganin sectary dinta ne yasa ta datse da gaggawa tana mai Cewa hello maryam wani irin nonsense nakeji Wai boutique ya kam..........

Bata karasaba Maryam tayi Sauri Cewa Ba nonsense bane ma munyi gobara, the came out of no where. Yanzu haka ina hospital saboda na none a gefen hannuna amma Ba wannan Ba new boutique dinma an Shiga an kwasge kayan tas sanna aka rusa ginin.

Take zakiyya ta yanki jiki ta fadi kasa sumammiya. Ace sukiyar da tayi shekara kusan 5 tana Tarawa cikin minti 5 babu su?ina impossible.

Inda Allah ya taimaka baki nasu wani hallara Ba tunda har yanzu saura 4 days a fara shagalin bikin ma Dan haka akayi asibiti da ita.

Sanda tasha drip 6 a rana daya dukda ko bata farfadoba saboda tsabar shock.

Yan gaisuwa kam sun kasa karewa an mayarda asivitin Kamar gidan Suna sai Shiga da fice ake.

Ayush zaune akan wani kujera a gefen gadon zakiyya taga Kamar hannunsa yana motsi. Rike hannun tayi ta fara jijjigawa tana kiran sis?sis sannu kinji ? A hankali zakiyya ta bude idanunta aiko babu bata lokaci hawaye sukayi sallama suka bemi mazauni a idanunta.

Mamanta ne tazo kusa da ita tana lalkashinta kamin tace Kiyi hakuri zakiyya akan namiji kike Neman kashe kanki? Sakinki yazeed din yayi ayush ne tayi saurin Cewa gaba mama saki kuma ? To mema zakiyyan tayi da za'a saketa?

Mama tace to inva saki Ba mezaisa ta sume har gadon asibiti caraf akaji zakiyya tace dukiya, dukiya itace abin da ta janyo.

馃槶mama dukkan dukiyan Dana Tara sun tafi,mama tace ban ganeba, zakiyya tace Nayi gobara babu abinda ya fita a boutique dina.

Dakin dake cike da mutane ne ya kaure da Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un.

Nanfa Yan Jaje ma suka fara rububi anata kawo gudun muwa.

馃尮.....................

Abangaren malama zaliha kam Ba kanta Dan yanzu tadan dawo daidai Inda tace Allan katafur sai an nemo lukman ya saketa, ita bazata iya cin amanan Sulaiman Ba. Mahaifinta da aka sallamo washegarin faruwar abin ya nuna farinciki sosai dajin Wanda ya aureta.

Ganin dai kowa yanason auren yasa ta saduda amma da sharadi bazatayi zaman aure dashiba. Side ido suka zuba mata Suna kallon ikon Allah so saikace hauka? Allah dai shi kyauta ya kuma bata lafiya Dan gani suke ta tabu.

馃尮..........................

Laila na zaune a dakin da mahaifiyarta ke kwance rai a hannun Allah. Aunty kuma ta Koma gida bata dawo ba goje ya bankado kofar dakin. Harararsa tayi tace me ya kawoka? Murmushi yayi cikin muryarsa ta Yan shaye shaye yace rayuwar Abubakar na cikin hatsari.

Laila tace what? Wani Abubakar din ? Yace Abubakar Yusuf dai da kika sani Kiyi sauri.

Batasan Inda take wulla kafunta Ba hankalinta tashe tana rokan gone da ya hanzarta kar wani Abu ya sameshi

Koda suka fito farfajiyar asibitin babu kowa Duba da Cewa magriba tayi wasu masallatan ma har sun kira sallh matse bakita yayi kamin ya cusa mata tsimma ya daure sannan ya sakata a Booth.

Figar mortar yayi yabar farfajiyan asibitin wani gida ya kaita ko ince irin dakunannan da samarin yanzu Yan Abu yarima ashana kida,Yan zaman kashe wando keyi. Banda warin sigarin ,hamamin amai da zarnin fitsari babu abun da dakin keyi Ba Komai bane a ciki illa katifa sai karamar TV da wata akwati daya sai kwalaben giya a gefe da dusan sigari.

Cirota yayi Daga booth din ta hada gumi tayi jagab ya fara janta zuwa cikin dakin, turjewa ta farayi ya gaura mata mari take ta fashe da kuka. Hankadata ya dingayi har ya wullata kan katifan sannan yace zan since miki baki domin ya zama dole in dan dana su amma Idan kika sake kikayi ihu kinga wukannan daina Burma mini ita da fatan kinajina ? Hararsa tayi yace wallahi wannan kallon wani irin shauki yakesamin.

Since bakin yayi kamin ya kara da Cewa gara kiban hadin kai muyi mu gama lafiya asirinmu a rufe.

Tace wa'iyazu billah aini ina Neman gafarar ubangijina na shigowa wannan dakin da kuma zama a wannan katifar da bansan sau bawa akayi zina akanta ba. Ka since min hannuna! Bara kaji Wallahi tallahi karshenka bazatayi kyauba.

Kuma haihuwarka asarar nakuda da ragon Suna ce.

Wani mari ya kuma dauketa dashi wannan karan harbakinta sanda ya fashe. Ihu ta kwala tana kiran sunan mahalliccinta. Bata ankare ba taji goje ya danneta yana kokarin kai mata kiss kakkauda kanta ta fara yi babu abinda take tunowa sai yadda ya Abubakar zaiji inya riski wannan labari.

Cikin rashin sa'a goje ya cafki bakinta yana kokarin tura harshensa ciki. Ganin ta rufe bakin kam yasa ya matse mata bakin da hannunsa badan task ba ta bude ta mai ja masa Allah ya isa.

Aiko harshensa yana Shiga bakinta ta fara kwaranyo amai.

Cire bakinshi yayi Daga nata ya fara zabga mata Marika sanda ya ajiye mata takwas lafiyaiyu daidai lokacin Allah ya taimaka mata hannunta ya since

Kokarin Daga mata Riga goje ya fara aiko nan suka kama kokuwa Kamar ba gobe.

Yaga rigar yayi ya fara kokarin rabata da pant dinta amma taji yarda tun tana iya tureshi har ta kasa hakan yasa yayi nasarar zare wandon nata yayi wulli dashi.

Wani irin zafi taji a mararta ta kwalla ihu YA UBAN GIJI NA daganan bata kara ganin komaiba.

馃槶馃槶馃槶 oya join me along let's cry!kuzo muyi kuka tare this chapter is so heart touching.

Long chapter ne so I expect you to to share kuma Ku cika min comments section da COMMENTS.

me kuke tunani game da wannan chapter?

Sai anjima wallahi bacci nakeji yau ba update din

18 / 45