Author : Untichlobanty Category : Complete Novels
karbo sannan suka tafi operation area. Text bokan ya Mata na yadda zatayi domin bukata ta biya.
Zakiyya tana cikin kuka mota kayansu yayi faci fitowa tayi domin taga me ya faru aka doke Mata kai wani powder aka hurawa minal daga nan bata kara ganin komai ba.
Ahankali zakiyya ta fara bude idon ta amma me ganinta tayi daure a kujera likimo tayi Dan taga Wanda ya kamosu. Aiko ayush da goje suka shigo suna dariya ko a jikinsu. Tashinsu sukayi zakiyya tama kasa magana saboda tsananin mamaki kawai kuka takeyi.
Tsk.tsk.tsktsk shine abinda ayush ta maimata kamin tace my darling sister are you surprised? Zakiyya tace me muka miki ? Idan na miki wani Abu ne me yasa zaki azabtar da mai ciki? Fuskar tunani tayi kamin tace may be me cikin da cikin suma sun min laifi ne.
? Tunda muka taso kike samun duk abin da kike so, ni fa? Banida komai. Iyayenki sunfi nawa kudi kin fini Ilimi, malamai suna sonki, Kin Sami farouq,kin Sami yazeed,kin Sami kudi,nayi kokarin rushe farin cikinki amma a banza.
Ba kashe farouq,na tabaki da yazeed, na koma boutiques dinki,nayi abubuwa da yawa aciki harda hatsarin yazeed amma me yanzu ma kin samu wani miji ga kina rike da mukamin da nakeso kinga dole ne na salwantar dake. Idan har bazan Sami abu ba toh babu Wanda ya isa ya samu.
Ke kuma, ta naushi bakin minal sai jini, kece dadi miji ko? Kowani lokaci kiuita like masa toh yau ne na karshe. Doke kan minal tayi da sanda take ta sume sannan ta dauko garin dake cikin shantun ta raba biyu kamar yadda boka mugu ya umarce ta.
Rabi ta zuba a tulun yayinda ta barbarda Rabin a tsakiyar kan minal Rabin kuma ta zuba a shantun ta jijjiga sai ta fasa. Sannan ta taka da kafar hagu. Kallon zakiyya tayi tace bakiyi mamaki ba Dana barki kike gani? Nayi haka ne domin kisan abinda ke wakana saide bazaki iya yin komai akai ba, Wannan shine hukuncin ki.
Yanzu haka your dearest mom tabi duniya don yanda na fasa shantun nan haka kwakwalwarta ta rushe sannan kishiyarki zata manta komai, zata dawo kamar yanzu aka haifeta. Kowa zai manta da ita banda ke da ni da mijina da boka na da.........
Kofa ne ya bude sai ga mummy (maman zakiyya) ta shigo, zaro ido zakiyya tayi hawayen dake zubowa a idon ta suka tsaya cak tace mummy dama baki mutu ba, colin samun Kwarin guiwa tace mummy help us ayush ta haukace,ni ban San wannan ba mummy ba ayush din my bace. Zama mummy tayi yayinda ayush ta rungume ta tana fadin mummy saura kiris kiyi missing kuwa.
Bakin zakiyya na rawa tace tare kuke aiki ? Mummy tace what do you expect?look young lady idan ma baki sani ba ki sani ayush ce kadai yata ke da yayarki a gidan marayu na dauko ku meaning? maman su safwan ma is not your biological sister that is you are all alone.
Zakiyya tace mummy me yasa zakiyi min haka? Mummy zakiyyan ki ne fa! Mummy...... yatsa mummy ta daura Mata a baki tace ya isa please no complaints. Riko hannun ayush tayi tace baby go ahead. Wani allura suka soka Mata a take ta zama paralyzed.
Mummy tace dont forget after three three months zakina yin wani okay? Tace okay mummy. Ya batun gidan anyi settling komai ? Tace yes nasa anyi photoshopping pictures din the guy is an American so ya iya aikinshi sannan umma hani ma bazata iya musa duk wani Abu da zamu ce ba tunda boka yayi mana maganin bakin ta.
Ayush tace wow mama na you are too great wallahi,naga pictures din. Nuna Mata tayi tace wow bazaka tana cewa hada hotunannan akayi ba. Tunba wannan da muke yara ba. Let's hurry up mu kama hanyan Abuja nasan yazeed ma I mean bro ya suma already muje kamin ya tashi.
Dariya mom tayi tace sh*giyar yarinya wai bro, suka fashe da dariya. Zakiyya tana gani kuma tana ji amma banda ?yafta ido babu abinda zata iya yi.
Ko hawaye saide idonta su ciko. Wheel chair suka daura ta goje ya turata ya fitar da ita. Sannan suka fitar da minal ma.
Dadai maraba gaban karo international market suka yarda minal suka barta kwance Shabe shabe kamar macacciya..........
IS ANOTHER UPDATE
KOWACCE TA TOFA ALBARKACIN BAKINTA.
KUN TABA TSAMMANIN AYUSH CE MUNAFUKAR?
YA LAMARIN ZAI KAYA NE WAI? INA TSIMAYIN COMMENTS DINKU.
KARKU MANTA KUYI SHARING DOMIN WASU SU SAMU.
TAKUCE KARAMARSU BABBARSU
Miss Untichlobanty ?
14th March,2020
*??KURUCIYAR MINAL??*
?by miss Untichlobanty ?
*?CHAPTER 78?*
*RECAP*
Zakiyya tana gani kuma tana ji amma banda ?yafta ido babu abinda zata iya yi.
Ko hawaye saide idonta su ciko. Wheel chair suka daura ta goje ya turata ya fitar da ita. Sannan suka fitar da minal ma.
Dadai maraba gaban karo international market suka yarda minal suka barta kwance Shabe shabe kamar macacciya..........
*CONTINUATION*
Cikin garin Abuja suka shiga inda suka nufi gida direct yayinda ayush ta tafi hospital saboda already an kirasu cewa yazeed is unconscious.
Koda ta isa asibitin dakin da yazeed yake aka kaita, kwance yake cikin kayan asibiti, fuskarsa tayi fayau ya Dan rame kadan. Baki ta tabe tare da yin murmushi tace soon I will be ruling everything sannan ta Sami waje ta zauna.
.....
Ummu Amina ce ta fito daga gidan ta damuwa dauke a fuskarta ta shiga makwabtan su. Sallama tayi uwani ta amsa tare da yi Mata barka da zuwa gaisawa sukayi a tsatstsaye uwani tace ummu amina haryanzu yarannan shiru? Anya lafiyar su kuwa ? Dan tsanani kwana uku suke dawowa gida amma yanzu dubi satin su daya ba ko labarin su. Ummu amina tace ai shiyasa nazo mu fita mu nemosu, Dan garin habujan nan? tsoro yake bani masu kudin nan yawanci yan shan jini ne balle yaran mu sun fito daga kauyen habuja yanzu sai a rudesu ga maraban nan badai mutane ba. AI muna samun su kawai tisa keyarsu zamuyi mu tafi Suleja? ko ya kika ce? Uwani tace nima dai haka nake gani amma zan shawarci me gidana, Allah dai ya shirya mana zuri'a. Ummu amina tace ameen. Nan uwani ta zaro mayafin ta suka baza cikin gari domin neman 'ya'yan su wato sabi'u da lado.
Uwani dai itace mahaifiyar lado yayinda ummu amina take mahaifiyar sabi'u Wanda ake Kira da sabi nigga. Ummu amina batada burin daya wuce ta haifi dariya mace tasa Mata amina saide Allah bai bata ba sai da daya data Haifa wato sabi niga Wanda ya Santo mata ala?a?ai, dahaihuwar sa gara babu.
Yan jihar nasarawa ne amma a maraba suke zama, sai lokacin noma yayi suke komawa nasarawa su noma doya sai su dawo su siyar.
Shi da lado basuda aiki sai yawo a garin su daki wancan,su sari wancan, su ?wace kudin wancan, ayi bangar siyasa dasu, su tsokano yan sanda. Kullum dai cikin matsala suke gashi suki aure. Toh ko zasuyi ma wa zai basu yarsa?
??
Hadiri ne ya hadu baki kirin, sai tawa da cida ake yi hakan yasa ummu amina da uwani labewa a zauren wani shago aiko ruwa ya barke ba kakkautawa.
Ruwa daya fara dukanta yasa ta bude idanun ta da sukayi Mata nawi. Gaba daya jikin ta ciwo yake Mata dakyar ta zauna kawai sai ta fashe da kuka domin gaba daya ji take zuciyar ta mata nawi ga bakin ciki da takeji. Kokarin tuno wani Abu tayi amma taji dib banda sunanta ba abinda ta sani kamar yanzu aka cillota duniya. Jin motsi a cikin ta yasata kallah, me zata gani cikin da ita. Toh fa anan ake yinta.
Tunani ta fara wai shin hatsari tayi ne? Cikin waye? Tana ma da aure? Su waye iyayenta? Waye mijinta? Daga ina take? Ganin babu amsa yasa ta kara fashewa da kuka. Tsananin kukan da take yasa hankalin su uwani yayo kanta. Ummu amina tace Allah sarki wancan mahaukaciyar kyakkyawa ko wani azzalumi aka samu ya dirka mata ciki ? Ga ruwa na dukanta ka bibiya yunwa ma takeji yasa ta kuka. Uwani tace har ta bani tausayi amma yanda kika ganota da kyannan kika bibiya hamshakiyar karuwa ce. Ummu amina tace kai nide ban yarda ba, uwani li fadi ALKHAIRI ko kiyi shiru. Bari in dauko ta in shigo da ita kasar rumfannan kar abinda ke cikin ta ya lahanta.
Nufo minal din tayi jiki na rawa Dan tsoron kar mahaukaciyar ta rufeta da duka. Daga dan nesa nesa tace baiwar Allah, minal tana dago kanta cak, ta tsaya da kukan lokaci daya taji kaunar ummu amina ya kamata babu bata lokaci ta fara kokarin mikewa. Taimaka Mata ummu amina tayi ta Mike a take ta rungume ta. Tare da kokarin fadin umma ? amma me sai taji ta kasa magana. Jan hannun ta ummu amina tayi ta kaita kasan rumfan. Haka aka gama ruwa tace mu tafi ko ? Ummu amina ta kalli minal tace toh baiwar Allah mu zamu tafi ki tafi gida, kema ki tafi gida kar zazzabi ya rufe ki. Riko hannunta minal din tayi uwani ta yarfa tare da fadin sake Mata hannu Dan Allah. Kema ummu amina laifinki ne daga ganin mutum waike uwar taimako ko? Haka uwani ta rufe ido tanata masifa wai ummu amina ta fita shiga harka da ba'a gaiyace ta ba.
Ummu amina kuwa fadi take haba uwani ki bari ko abin ci mu bata mana, mai ciki fa abin tausayi ne.
Minal kam yunwa takeji ga sanyi, haka ta dinga karkarwa ga zazzabi daya rufeta. Tashi tayi ta fara tafiya ga jiri dake dibarta. Wani suya spot ta gani taje gefen wajen ta tsaya sai hadiya yawu take tana kallon yanda mai ke diga daga jikin naman. Wani guntun biredi aka bata aiko ta hau mamuka har tana ?warewa.
Kowa idan ya gama cin abinda zaifi sai ya bata guntun. Mai suya dai abin ya fara bashi haushi dan haka ya cika yayi fam saura fashewa.
Former lieutenant sabir (Wanda ya rasa aikin sa na dan sanda saboda yace bazaiyi rashin gaskiya ba)ya siyo doya Wanda za'ayi breakfast a gidan da yake gadi ya hau babur dinsa kawai yaji yana marmarin suya hakan yasa ya tsaya tukuban da minal ke gefe. Haka aka kawo mai yana ci yana kallon ta, ji yake kamar ya San ta amma da ta fara tunani sai kansa ya fara ciwo kawai sai yaji ya kasa ci saboda kallon naman da take ta yi.
Mai tukuba kam ganin kamar saboda ita sabir ya kasa ci yasa shi fara Koran ta kuka ta fara masa tana cijewa Dan bata koshi ba ya fara hankadeta. Sabir ne ya saka masa tsawa. Kwalarsa ya damka rate da fadin kai wani irin wawa dabba ne? Bakasan Kima da darajar mace bane, bakaga ciki ne da ita ba zaka na hankade ta? Ko muharramar ka ce da zaka taba ta?
Duk cakwakiyar nan da ake yi minal bata sani ba Dan har taje ta dauki naman da sabir ya bari ta fara ci. Sabir kuwa lura yayi da bata wajen hakan yasa ya saki mai nama ya juya daidai lokacin kuwa ta danna albasa a baki. Murmushi kawai yayi ya zauna a gefenta. Yace ya sunanki? ?uri tayi da ido tana kallonsa,murmushi ya sake Mata yace yunwa kike ji? Ta daga kai daidai lokacin wayarsa tayi ringing.
Yace hello hajiya. Tace sabir ina ka tsaya ne yace ganinan dawowa daga nan ya kashe. Tashi yayi tare da cewa yar uwa sai gobe ki? Murmushi? tayi ta daga kanta. Daga nan ya dale babur dinsa ya wuce itama daukar ledan ta tayi ta fara tafiya. Tana cikin tafiya ta taka kaya hakan yasa ta tsalla ihu.
Ashe daidai ginin yan shaye shaye ne lado yace tattabara daga sama gasassa.
Sabi ne yazo ya sunkuce ta bai ajiye ta ko ina ba sai cikin ginin. Kuka ta fara musu ga zafin kayan da takeji lado ne ya ajiye kwalbar giyan dake hannunsa ya fara zare belt. Baya baya ta fara yi daidai lokacin Allah ya taimaka Mata aka dauke wuta dan haka area din gaba daya yayi duhu. Kwalbar ta raruma ta kwalawa ma wani sannan ta Mike fa fara bin gini aiko ta taka kwalba. Toshe bakin ta tayi tana fita aka kawo wuta hakan yasa suka bita a guje ashe sabi nigga ta kwalawa kwalbar.
Gudu suka dinga yi kamin ta samu ta labe a lungu sai haki take taji an dafa kadar ta juyowa tayi suna hada ido ta zaro ido tare da kwala ihu...
*I know that wasu haushin abin da ya samu minal sukeji. Hakuri zakuyi labarin ne yazo da haka.*
*Su o o har ankusa zubda kwalla saboda tausayin minal.*
*Karku manta kuyi VOTING,COMMENTING tare da following Dina sannan kuyi SHARING da followers dinku domin kar a basu labari.*
*ONE LOVE?*
Miss Untichlobanty ?
28th March,2020.
*??KURUCIYAR MINAL??*
*?by miss_untichlobanty ?*
INSTAGRAM:@miss_untichlobanty
TWITTER:@miss_untichlobanty
WATTPAD:@miss_untichlobanty
*?CHAPTER 79?*
*RECAP*
Kwalbar ta raruma ta kwalawa ma wani sannan ta Mike ta fara bin gini aiko ta taka kwalba. Toshe bakin ta tayi tana fita aka kawo wuta hakan yasa suka bita a guje ashe sabi nigga ta kwalawa kwalbar.
Gudu suka dinga yi kamin ta samu ta labe a lungu sai haki take taji an dafa kadar ta juyowa tayi suna hada ido ta zaro ido tare da kwala ihu...
*CONTINUATION*
Ba kowa bane illa sabi nigga, aiko ya wanka Mata wani jahilin Mari Wanda ya sata faduwa ba tare da bata lokaci ba.
Dariya ya sheke dashi harda rike ciki, hakan ya bata daman rarumar dutse ta tashi a hankali sannan ta kwala masa.
Ihu ya saka yayi da ta fita a guje tana mai tallafo cikinta Wanda ke Mata zafi a halin yanzu.
Sauran yan daban ne sukayi saurin karasawa wajen sabi'u sakamakon ihun sa da sukaji. Tambayan sa suka fara yi lafiya ? Ya nuna musu hanyan da minal tabi. Biyu daga cikin su ne suka bi hanyar yayinda lado ya tsaya, ya tallafa masa ya tashi sannan ya fara kokarin kaishi gida.
Minal gudu ta sharara har sanda kafar ta suka daina gudu kamin ta Sami zauren wani gida ta shiga. Itacen girki ta gani a jibge gefe guda dan haka taje ta jingina a jiki babu bata lokaci tayi bacci dukda ko a jikinta? tanajin akwai abinda ya dace tayi Wanda batayi ba.
??
Yazeed bai bude idanun sa ba sai wajajen karfe Goma na dare. Akan fuskar ayush suka fada ta sakar masa wani murmushin munafurci tare da fadin brother sannu da tashuwa. Kallon ta yayi da alamar tambaya yace brother? Tace eh karka damu dama likita yace min zaka iya manta wasu abubuwa so karka damu, San baka dukkanin information da kake bukata. Jinjina kai yayi alamun toh yana kare Mata kallo Dan shi bai ma yarda da ita ba yace wacece ke? Murmushi tayi tare da zama a bakin gadon sa ta riko hannun sa. Dan janyewa yayi tace karka damu ni muharramar ka ce,ni kanwarka ce, your baby sister ka tuna?? sakan jiki kadan yayi yace toh me yasa aka kawo ni nan? Tace saboda tun sanda mahaifin mu ya rasu kake cikin damuwa hakan yasa kake samun wani ciwon kai me tsanani Wanda yakan sumar dakai wani lokaci ko ya sabbaba maka manta wani Abu toh wannan karan da alamu alakarka da mutane ka manta.
Jinjina kai yayi domin maganan ta kama kwakwalwar sa. Yace munada mahaifiya tace eh tana gida yanzu kaga hotanta. Ta fadi hakan tana mai nuna masa wallpaper wayanta. Hoton su ne su hudu, shi da ita da mummy da umma hani. Yace toh ai Mata biyu ne wajen waccece ita? Tace me kwalliyar nanne mana. Wancan kuma umma hani ce nanny din mu. Ajiyan zuciya ya sauke yace bani ruwa insha, Darius tayi kamar shasha tace au na mance na tsaya ina maka surutu.? Murmushi kawai yayi tare da karbar ruwan yasha.
Nan dai taci gaba da masa bayanan karya shi kuwa Allah sarki bai sani ba sai shiga yake tare da rike komai da take fada masa.
??
Gidan mahaukata sukasa aka kai mom bayan an haukatar da ita. Mai kawo abin ci ne tazo tana wulla musu hara ta iso dakin mom Wanda yake na karshe. Tana kallon mom taji kamar ta Santa kuma lokaci daya taji mahaukaciyar ta kwanta Mata a ranta. Wulla Mata nata abin cin tayi mom taso ta dauka ta kyalkyale da dariya kamin kuma tace na gode.
Fara co tayi tana yamutsa fuska da ka ganota kasan bata Saba shan wahala ba. Tsayawa kallonta tayi kawai sai taji hankalinta ya kwanta da mahaukaciyar. Bude dakin tayi ta shiga sannan ta rufe, a take mom ta fara ja da baya tana fadin karki matso kusa dani! karki matso kusa dani! Matar tace kwantar da hankalin ki ba abin da zan miki.
Zama tayi a gefenta kawai sai mom ta fashe da kuka. Matar me suna senior hauwa tace me aka miki kike kuka? Mom tace ?a na, zasu cutar min dashi! Senior hauwa tace ina yake kuma yaya sunan shi? Shiruuuu mom tayi kamin tace nima ban sani ba, na manta sannan ta sake fashewa da kuka.
Rarrashin ta senior hauwa tayi haka sukayi hirar su dukda cewa wani lokacin mom din takan Mata hauka amma dukda haka tana zargin wani Abu tana ganin haukan mom din ba haka kawai bane.
??
Washe gari da safe aka sallamo yazeed kuma har wannan lokacin ayush tana like dashi, mummy ne tazo tayi musu oyoyo, taci ado ta kashe saurin dankwalin shaddar nan, gwala-gwalai ta ko ina abin nema ya samu.
Daidai lokacin wayan ta yayi ringing hakan yasa tayi excusing kanta kamin ta haura sama. Goje ne ke kiran ta, tace baby ya akayi ne? Yace lafiya kalau wifey dama so nake mu hadu tace okay no problem ka