KURMAN BAKI HAUSA NOVELS WRITING BY HUGUMA.pdf

Author :  Safiyya Abdullahi Huguma Category :  Taskar Novels

Chapter   8 / 24

21K to 24K   out of 69.9K words

anty?,na gode sosai,Allah ya qara rufa asiri"

"Ameen ba komai" (don Allah mu rage qanqamo,kowa baya banbararki ke ba'a morarki,motsi
kadan kice dangin miji basasonki,sun tsaneki saboda Allah ya miki rufin asiri,ko miji yana
wadataki,ba dole su tsaneki ba babu ihsani tsakaninki da kowa?,kowa idan abinsa ya taso saiki
kama hannu ki rungume,kice sai ya baki zaki basu bayan kina da wadatar da ba lallai saishi ya
baki ba?,karku manta,kyautatawa tana saka d'a ya zama bawa ba tare da ya sani ba,kyauta da
ihsani tana saka soyayyarka a zuciyar mutane,Allah yasa mu dace)".

"Ni anty wallahi banji dadin rashin siyan maganin nan ba,bakiga yadda su anty Zainab ke dariya
ba da sukaga zaki siya turare"

"Au haba?" Ruqayya ta fada tana dariya sanda take zuba turarukanta a babbar ledar da na'ima
ta bata

"Allah,dama sunata gulmar haka kike zaune sakaka,banda asirin ma da kikewa yaa saleem da
tuni ya sakeki"

"Hmmmm"batulu ta fadi kawai ba tare da tace komai ba,don itama abin yana bata takaici.
Zainab ce 'yaruwarta,amma har ga Allah yadda takejin ruqayya a zuciyarta take kuma burgeta
Zainab bata taba burgeta ba,tun zamanin 'yammatanci ma,saboda ko a sannn din Zainab din ta
fiya rawar kai da zaqewa,ga shiga abinda shekarunta basu kai ace ta shiga din ba tun a lokacin.
"Ashe ni ban cika mace ba amma ban sani ba,indai sai na siya irin wadannan tarkacen lallai ko
bazan taba amsa sunan mace ba,Allah yasa kuma bakwa kwasar ire irensu " ta fadi tana duban
idanunsu.

Girgiza kai batulu tayi da sauri

"Nikam bani da juriyar irin wannana abun ma,fruit kawai sun isheni"

"Kefa?" Ta fada tana duban fatima. Dariya tayi a kunyace

"To aunty mu duka duka yaushe muka shigo sabgar ma,haihuwar fari fa nayi yanzu"

"To duk ku zauna" ta fada tana gyara zaman babyn dake kan cinyarta.

Basu musa ba kuwa suka zauna din kowa yana bata hankalinsa

"Fruit kadai basu wadatar dake ba batulu,haihuwarku uku,haka kema Fatima bazaiyiwu ki

zauna haka ba,dukkanku don baku da kishiya ne shi yasa a yanzun ba zaku fahimci komai
ba,saboda hankulanku a kwance suke,baku da maraba da mutumin dake dakin mamansa a
kwance yana bacci" idanu suka zuba mata suna dubanta,sai ta saki murmushi tana gyada kai

"Eh,a baya nayi tunani irin naku,bayan auro zainab naci gaba da rayuwata daga abincina sai
fruit,sai a hankali na fara karantar canji daga wajen saleem. Ban rasa tsafta iya girki haquri
ladabi da biyayya ba,hakanan bai taba muzantani da ki cusgunamin da gangan ba,amma a
aikace ina lure da rawar qafar da yakeyi akan zainab,sai daga baya na gane cewa tabbas
dukkan mace tana buqatar gyara,amma gyara wanne iri?,ingantaccen gyara da bai wuce qa'ida
ko hankali ba,gyaran da ko meye zataci tasan me taci,kome zata sha tasan me tasha,Allah ya
sakawa anty deeja da alkhairi,bazan taba mantawa da ita ba cikin babin rayuwata,itace mutum
ta farko data fara dorani akan hanya. Ta tunasar dani hatta iyaye da kakanni suna amfani da
magungunan gargajiya gurin gyaran diya mace,kamar bagaruwa,ganyan magarya da sauransu.
Inno kakata ta gayamin,yadda muke samun qaruwa(yagewa) yayin haihuwa haka suma suna
samu,amma saidai su basusan wani dinki ba,ana gyara mace ta koma fes da bagaruwa da
sabulun salo ta hanyar tsarki da shiga ruwan bagaruwan. Na baku misali mana"

"Muna jinki" suka fada a tare saboda yadda bayaninta ya fara musu dadi da tasiri

"Zai yiwu ki siya mota ya zamana kullum kin hawa kina sabgoginki,ko engine generator kuna
kunnashi kullum amma ba'a masa service?" Kai suka girgiza a tare alamun a'ah

"Idan hakan ya kasance wataran ba za'a wayi gari ya tashi a aiki ko yana aikin dai amma
lallabawa kawai akeyi ba baya bada abinda akeso?"

"Tabbas" batulu ta fadi

"To kamar haka yake a wajen mace,kiyi gyara saffa saffa da ingantattun itatuwa da abubuwa
natural,karki tsaya a gyaran qasanki,ko ina na jikin mace yana buqatar kulawa da gyara,saidai
kuma komai da zakiyi gyaran dashi ki tabbatar ingantacce ne. Shi kansa engine din idan aka
yawaita yi masa service din da juyen mai haka ba gaira ba dalili ba tare da alamu sun nuna
yana buqatar hakan ba me zai faru?" Kai batulu ta jijjiga

"Gaskiya akwai matsala, za'a yita sakwarkwatashi ne ana raunata qarfinsa"

"Wani notin ma idan aka kwance ba lallai a iya mayar dashi wajensa a daure,shikenan sai ya
fara rawa,sanadin hakan sai wani gurin ya kuma saki" fatima ta qara dorawa

"Yauwa,alhamdulillah,komai idan yayi yawa yana da illa ga jiki da lafiya,hatta natural ways din
idan ka dauke 'ya'yan itatuwa da su basa yawa ga lafiya"

"Gaskiya ne" batulu ta fada

"Duk shan maganin matanki ko acan da ake hadawa saikin kiyaye wasu abubuwa sannan
zasuyi tasiri,suma masu kyan ba daka ake shansu ba ai"

"Kamar me da me?" Fatima ta fada tana komawa ta zauna

"Yauwa,dole ki zama mai tsafta,babu ta yadda zaki tuttuli magani ki nemi kasancewa da me
gida amma ko ina yakai hari sai a koroshi waje....." Bata qarasa ba suka sheqe da dariya su
dukka biyun. D ido ta bisu tana son jin ba'asi,batulu ta yanke mata tunani

"Kamar dai zainabunki?"

"Banaso, ba'a gulmar 'yaruwata a gaba na"

"Ita tayi taki ai,har ta taya a zageki" batulu ta fada tana tabe baki cikin jin takaicin sakarkarun
halayen zainab. Murmushi ruqayya tayi

"Taga zata iya ne" ta amsa a taqaice sannan ta dora

"Abu na gaba ba yadda zakisha maganin mata baki da lafazin baki,ladabi biyayya haquri da
juriyar zaman aure wanda sune jigon zaman ba wai maganin ba,shan magani kawai yana
armasa auratayya ne da hanata ta gunduri abokin zama"

"Gaskiya ne wannan,na yarda da haka" batulu ta fada tana jinjina kai

"Sai kuma babban abun,mata ne ku ba kunyarku zanji ba........shan maganinki bazai taba miki
amfani ba ba tare da kin iya sarrafa me gidanki a turaka ba,dole ki koyi salo da dabarun
kasancewa da me gida sannan tasirin maganin zai fara aiki a jikinki,wannan dole ne,ba kuma
kiyita gyara kanki shi bakya gyarashi ba indai akwai fahimtar juna da sauqin kai a tattare da shi"
"Suma ana gyaransu kenan" fatima dake dan qunshe dariyar kunya ta fada

"Eh,sosai ma" ruqayya ta fada tana kallonta

"Kinga maggi?,kinga maggi?,yana bala'in taka muhimmiyar rawa wajen qarawa maza
rauni,zaqi,maiqo,yawan yi musu ta'ammali da man gyada,shan sanyi,shan abubuwan da suke
da sinadari caffeine da yawa a ciki,shan lemukan nan masu gas irin coca-cola da sauransu,ki
yiwa miji natural drink kamar zobo,karkice zaki zuba tiara ko baby mix ko cola a ciki,ki dafashi
natural da cocumber ginger cinnamon cardamom na'ana'a scent leave (daddoya) kanunfari da
abarba,ki tace kisa masa sugar kadan yafi ki bashi wadan nan lemukan kaf dinsu,ku daina
jibgawa mazanku magungunan qarfin maza,kashesu kawai kukeyi, za'a kai jallin da ba zasu iya
tsinana komai ba muddin basusha wannan maganin ba,ke kanki idan kika ta'allaqa rayuwarki da
shansu akwai matsala wataran zakiyi expire wallahi" dariya dukka ta basu,har itama suka saka
ta dara(akwai hadin salad da na baku a last page,shima yana da matuqar muhimmanci wajen

qarawa maza kuzari a turaka)

"Eh mana,sanda kike da buqata kiyi service kiyi,service me ma'ana da hankali,ko meye na
gyara zaki iya siyan kayayyakin a ganyensu ko asassaqensu guda ki dafawa kanki,idan ba zaki
iya ba ki karba a gurin wadda kike da tabbaci a kanta hundred percent. ammafa kome zakisha
indai ba zaki dinga ci kina qoshi ba akwai matsala, ba'a son ki dinga zama da yunwa,ko a
abincinki ya zamana babu wani abu da zai qareki a lafiyar jikinki".

"Amma matsi fa mata na sonshi Anty" murmushi ta kuma saki,mata da yawa sun halaka ta
sanadiyyar matsi

"Akwai natural ways shima"

"A bamu anty" fatima ta fadi da sauri sai kuma kunya ta kamata.

"Zaki samu sassaqen bagaruwa,kanunfari,bagaruwa sai magarya,ki tafasasu ki dinga shiga ciki
idan ruwan ya huce,kunga duk a ciki meye me cutarwa?,meye wanda baku sanshi ba?"

"Babu wallahi anty" fatima ta fada cikin gamsuwa

"To kun gani,ku damu kanku da sabulun tsarki,bayan babu sabulun da yakai sabulun salo indai
kin samu original din"

"Gaskiya ne" batulu ta fadi

"Allah yasa mu dace" ruqayya ta fada tana miqa batulu babyn

"Zaki tashi muna qaruwa dake" murmushi ta saki

"Muna gaisawa da hajiya na shigo banko zauna ba,kuma inason na leqa gidan umma binta,zan
jira shukra zata kawomin su iftee zasu wuce gida dasu"

"Anty kafin nayi arba'in zanzo gida na sameki don Allah a bani sauran sirrikan"

"Saikinzo fatiti,kawai dafe dafen nama kala kala da zakiyiwa kanki,a baki da dadi a jiki da aiki ba
wani sauran fargabar meye a ciki" cike da murna tace

"Zanzo in sha Allah"

"Qafarki qafata" batulu ta fada tana dariya

"Duka sai kunzo" ruqayya ta fada tana murmushi.

La'asar liqis ta baro gidan sunan tayi sallama dasu don ta qarasa gidan umma binta
kamar yadda tace. Qanwace ga mahaifiyarta kuma a nan bayan layin gidansu fatiman take.
Don haka cikin qasa da minti daya ma ta isa tunda a mota take.

https://chat.whatsapp.com/EKyzZCUEGyRAEGGAnTHmGF

*_KURMAN BAƘI_*⚫⚫⚫

*HUGUMA*

PAGE 10



Hankali kwance cikin nutsuwar ta ta macen da tasan kanta ta tura kanta cikin gidan
bakinta dauke da sallama. Sai da tayi sallama sau biyu kafin a amsa. Daga can cikin daya daga
cikin dakunan dake hannun hagunka.

"Da alama umma bata nan" ta fadi qasa qasa ta wucewa dakin da take jiyo ana amsa mata
sallamar.

Labulen ta dage tana sake jaddada sallamarta. Ido hudu sukayi da matashiyar dake
zaune saman abun salla. Sanye take da hijab har qasa,baka ganin komai sai fuskarta da tayi
wani haske dauuuu,irin hasken da kana masa kallon farko zaka san cewa ba natural haske
bane. Hannunta da yanayin hasken fatarsa yasha banban da hasken fatar fuskarta na riqe da
carbi tana ja daya bayan daya,bakinta yana motsawa mis mis da alamun wani abun take
karantawa

"Iskancin banza,ashe kina ciki kina jina naketa kwada sallama" ta fadi tana dan jifanta da harara
hadi da zare takalminta ta shigo dakin gaba daya tana cewa

"Yo wannan basai a shigo ayi muku sata bama?" Tayi maganar tana zama gefan kujerar guda
daya dake dakin idonta akan matar.

Hannunta ta dora saman bakinta alamar tayi shuru,sannan taci gaba da jan carbinta.
Sasakai ruqayya tayi tana binta da kallo,sai kuma taja tsaki ta maida dubanta ga dakin.

Kayan ado ne jere sama madubin,mayuka kala kala da turaruka,harda kwalabe da
gwangwanayen supplement kala daban daban.

Kan supplement din hankalinta yakai,ta miqa hannu daga inda take ta dauki wata
zungureriyar kwalba dake dauke da syrup a ciki.

Tun a rubutun farko ta fahimci maganin qara qiba ne,saita daga kai tana kallo fuskar
matar dake zaune akan sallah. Tabbas,ta qara qiba qiba data jima tana mamakin ya akayi
wasila siririya da ake tsokanarta da sunayen tsokana kala kala saboda rashin qiba lokaci guda
tayi irin wanna qibar?. Mamaki ya hanata magana,saita mayar da kwalbar ta ajjiye dai dai sanda
idonta ya gano mata wani tablet din dake nuna whitening yakeyi. Kai ta sake jinjinawa tana
maido dubanta ga wasilar,dai dai nan ta shafa hannunta akan fuskarta da alama ta gama.

"Ke kuwa me kika zauna yi har rana tana shirin faduwa bakiyi sallar la'asar ba?"

"Haba ni da nake da tarin buqatu?,ta yaya zan bari sallar ta kufecemin? la'asar dinta liman yana
sallamewa ina sallame tawa,wannan wani wuridi aka bani nakeyi"

"Wuridi ko addu'a"

"Duk daya ne ai" ta amsa mata tana ninke sallayarta

"Addu'ar ce idan anayi ba'a amsa sallama?,nidai a iya sanina salla ce kawai ya haramta idan
anayinta ayi magana" Ruqayya ta sake jifanta da tambayar

"Ke wannan ba irin addu'ar da kika sani bace,wannan ta neman miji ce,yazo ayi aure nima na
ganni a dakina na huta kamar kowacce mace" ta fadi tana zare hijabin jikinta t wurgar
gefe,hakan ya sake bayyanawa ruqayya qibar da ta tsammata daga wasilar,saidai ashe hijabi
ma ya rufe wani abun.
Kasa shuru ruqayya tayi tana duban wasilan tace

"Yanzu wasila wannan wacce irin qiba ce haka da uban fari da fuskarki tayi?,ga kunnenki duk
kin bula kin cikashi da barima?" Gefen ruqayyan ta zauna tana daukar wayarta

"Ba zaki gane bane,ke don kina dakinki asirinki a rufe,yanzun rayuwar sai da updating sai kina
gyara,idon mazan a bude yake,saisu rainaka ko kiga wanda baikai ajinka ba yazo yace kai
yakeso saboda rainin hankali"

"Yanzu qibar da farinma kenan yayinsu akeyi"

"Ke,qwarai kuwa,mace 'yar duma duma ai duniya ce,farar mace kuma itace alkyabbar
mata,lantarkin gida,ajebo kalar hutu,sadakinsu ma daban yake,hakanan sunfi shiga" hangame
baki tayi tana kallon yadda wasilan ke magana da confidence. Tare sukayi yammatanci da
wasila,tunda can tana da surutu da rawar kai,amma yanxun kamar an qara mata da wasu
sabbin halayen

"Indai hakane kice mu da bamu samu mashinshini ba"

"Da kenan,sanda kukayi aure ai duniya a kwance take,shekara bakwai zuwa takwas baya
fa,kema ba yadda banyi ki goge baqar fatar nan ba kikaqi,ai gashinan kina zaune kina ji kina
gani mijinki yaje ya dauko farar,wadda ma bata fiki komai ba" dariya wasilan ta bata yadda take
nuna jin zafi da jin haushinta duk sanda akayi zancan zainab
"Wai tsaya,kin manta bleaching haramunne?"

"To ya za'a yi?,neman wanda zamu shige daga ciki kawai mukeyi?"

"Tabdijan,wasila?,a haka?,kina abinda Allah bayaso amma ke kina neman ya dubeki?shaidanne
fa yayi alqawari da kansa Allah ya fada mana cikin suratun nisa'i aya ta dari da sha tara,cikin
alqawarin da yayi yace zan sanyasu su dinga canza halittar Allah,cikin canza halittar Allah
wadan nan abubuwan suna daga cikinsu,kisha magani ki qara qiba,kisha magani don ki sirance
bayan qibar ba matsala take kawowa ga lafiyarki ba,ki shafa mai kiyi haske ko ki shafa mai don
kiyi baqi duk da mu an jarabci mutanenmu da son suyi haske ne kawai,duk da ana samu cikin
turawa da yahudawa masu maida fatarsu baqaqe,duk me ya kaiki wannan wasila?"

"Ina zuwa" ta fadi tana dagawa ruqayya hannu sakamakon kiran da ya shigo wayarta.

Da kallo ruqayya ke binta da shi har ta gama amsa wayar tana gatsine gatsine hadi da
amsa maganarsa da qyar. Wayar ta wulla gefe tana jan siririn tsaki

"Sirikin namu ne?" Ta tambayeta tana ciro tata wayar daga jaka ta kirayi shukra taji yaushe zasu
iso

"Wa?,Allah ya kiyaye,sulaiman ne fa" tsayawa ruqayya tayi da abinda takeyi tana duban wasila
cike da mamaki

"Sulaiman dinne abun Allah ya kiyaye?,badai sulaiman wanda yazo duba umma sanda aka
kwantar da ita a asibiti ba"

"Shine,amma ke kinga mijin aure a nan?" Ta jefawa ruqayya tambayar tana kallonta

"Ni kuwa naga mijin aure nagartacce ma,me sulaiman ya rasa?" Baki wasila ta tabe tana jawo
carbinta ta saka a yatsarta ta fara ja tana cewa

"Abubuwa da yawa mana,haba ruqayya kamar makauniya?,yana da rufin asirinsa yana da hali
me kyau,amma gaskiya kamar bai qarasa irin mijin da nakeson aure ba" Mamaki ya qarasa
kashe ruqayya

"Amma yanzu bake na samu kina wasu wuridai ba duk akan Allah ya kawo miki miji kiyi aure ki
huta ba?"

"Eh amma mijin ai ba kowanne iri ba,irin sulaiman ina dasu sun kusa hudu,amma wanda
yadanfi hakan rufin asiri nake nema,bance saimai shahararren kudi ba,amma ina laifin miji
kamar naki saleem din,ke ba motar hawa gareki ba yanzu ke da kishiyarki?" Kasa cewa komai
ruqayya tayi mamaki yana ci gaba da kamata
"Kuma ma dazu dazu na dawo daga gurin wani bawan Allah,yayimin istihara ya gayamin aure
na da isma'il babu alkhairi a cikinsa sam sam,mijina yana nan zuwa,dan kasuwa ne a kantin
kwari,kinga kuwa ta yaya zan tsaya ina dagawa kaina hankali akan wanda nasan ba mijina
bane"
"Shi din Allah ne da har zai fadi abu ki yarda?"

"Amma istihara ai ba qarya bace"

"Wacce irin istihara yayi miki?"

"Normal istihara da aka saba,carbi ya ajjiyemin yace na zabi daya,da na dauka na miqa masa
ya karba na wasu mintuna sai yayi min bayani,babu qasa a wajen bare dai kice min duba ne"
wasila ta fadi cikin gamsuwarta da abun.

Cike da takaici ruqayya ke girgiza kai tana duban wasila

"Wai duk yawon islamiyyar da muka dinga yi ina naki karatun yayi wasila?,dama haka annabi ya
koyar da istihara?,suna fakewa da duba suna canza masa suna da istihara?,wallahi sai sunyi
shari'a da annabi,ba wani wanda zai maka istikhara kai zakayi abarka da kanka,bayan kinyi
sallar raka'a biyu zaki karanta
*_Allahumma inni astakhiruka bi'ilmika,wa'astaqdiruka bi qudratika,wa'as'aluka min fadlil
azeem,fa'innaka taqdiru wala'aqdir,wa ta'alam wala a'alam,wa'anta allamul guyub,Allahumma in
kunta ta'alam anna hazal amra(saiki fadi buqatarki)kairul lee,fi diny wamu'ashy wa'aqibatu
amry,fayassirhu ly summa barikhly ly fihi,wa'inkunta ta'alam anna hazal amra(saiki fadin
abun),sharrully fi diny wamu'ashy wa'aqibatu amry fasrifhu anni,wasrifny anhu,waqduriliyal
khairu haisu khana,summa ardini bihi) annabi yace ba wanda ya taba istikhara irin wannan
bayan yaji ya gamsu da abun ya zartar da shi,daga baya kuma abun ya zame masa
nadama,idan kayita kayi shawara

8 / 24