KURMAN BAKI HAUSA NOVELS WRITING BY HUGUMA.pdf

Author :  Safiyya Abdullahi Huguma Category :  Taskar Novels

Chapter   7 / 24

18K to 21K   out of 69.9K words

zai fara miki aikin da idan hadin Allah kikayi musu sai yayi
wata uku mace tana sha bataga canji ba,yanzu zakiji an bata miki kasuwa ana cewa bashi da
kyau,bayan shine me kyan,tsabar gaggawa ce dasu to kinga gwara kawai kayi musu abinda
sukafi ganewa,wanann garin duk yawansa bazaikai jibi be qare ba" ta fada hautsina garin
masarar dake cikin botiki,da niqan aya da saqe saqen da batasan adadin yawa da kuma dame
dame ta game waje daya ba. A hakan garin masarar yafi yawa,ganin yayi haske da yawa saita
debi garin kala me dan duhu ta watsa

"Yauwa,sai a dauka tsabar soyayyar ayace da ta wadata" hajiya ta fada a ranta tana qissima
yawan ribar da zata fitar a wannan hadin da tayi.

*******A nutse ta kammala komai,hatta da abincin dare harda farfesun kayan cikin da saleem ya
aiko daga kasuwa. Ta shirya tsaf cikin atamfar black prince me kyau data dace da kalar fatarta.
Wani irin sassanyan dressing,ita din gwanace gun hada ado da yakan dace da kowacce kalar
unguwa. Hannunta riqe da key din motarta ta fito babban falon gidan da zai wuce da ita harabar
gidan.

Sauka idanunta yayi akan sassan zainab. A rufe yake gam,ta kusa awa hudu da tafiya
tuntuni. Aike ta dinga yo mata ba qaqqautawa akan ta fito su tafi,ita kuma ta aike mata ta tafi
kawai ta taho. Hakanan al'adar zainab take,indai taji batun fita gurin wani sha'ani ko taro jikinta
har rawa yake,ba kasafai ranar abincinta ke ciyuwa ta dadin rai ba idan ma ta tsaya tayin. Wani
murmushi ya qwace mata data tuna wani abu,ta girgiza kai kawai tana isa ga motarta,tabbas ta
yarda wasu matan basu da wayo kam.

Minti talatin ya kaita unguwar,suna akeyi na 'yar qanwar mahaifiyar saleem din. Kana
gani kasan gidan cike yake,don kuwa duk da gidan yalwatacce ne amma har ta waje kana iya
hango zirga zirgar jama'a. Tunda ta ajjiye motarta ta fito taketa gaisawa da mutane cikin
mutuntawa da ganin kima,can qasan zuciyarta mamaki yana dan mamayarta,tana sake gasgata

cewa tabbas ME HAQURI YAKAN DAFA DUTSE HARMA YASHA ROMONSA. Mutanen da
wasunsu a baya suka daina magana da ita,wanda ita tasan ba komai bane ya jawo hakan sai
saboda zainab da saleem ya auro da suke ganin 'yaruwarsu ce sunfi kusa da ita akan
ruqayyan,duk da tarin kyautata musu da ruqayyan keyi amma suka shafawa idanunsu kwalli,sai
gashi lokaci yanata nuna kansa, gaskiya kuma tanta halinta bayan ta watsar da damuwar kowa
ta maida hankalinta ga addu'a da mu'amala da kowa da zuciya daya.

Gaisawa ta dinga yi da mutane,bata kuma zauna ba har sai data lalubi dakin da
surukarta take da wasu daga cikin qannen hajiya din.

Da sallama ta shiga cikin kamala da kuma kunyar da har yanzu batajin ta gushe a
tsakaninsu,duk da irin abubuwan da suka faru a baya,da irin ababen da ita hajiyan tayi mata
masu dimbin yawa dake da soya zuciya da saka me rauni ya tsani mutum. Taji babu dadi ta
kuma koka matuqa da gaske,saidai ko sau daya bata taba jin ta tsaneta ko zata iyayi mata
rashin kunya ba,saboda me?. A koda yaushe tana duban hajiyan a matsayin wani tsani na
dukka matakin da tahau a rayuwarta,duk tsiya duk kuma inda za'a je a dawo itace dai ta haifa
mata saleem din da zuciyarta ke matuqar so take kuma son ta kyautata masa wanzu tare ila
yaumil qiyamati,ta bashi tarbiyyar da har ta burgeta ta kuma zame masa silar mallakarta,tana
ganin wadannan dalilai kadai sun isa babban dalilin da hajiyan ta cancanci dukkan wani uzuri
girmamawa da dagin qafa daga gareta.

Sallamar ruqayyan yaja hankalin hajiyan. Sai ta far gyara zamanta cikin fara'a da kuma
d'ari d'ari,kunya da nauyin yarinyar a yanzu takeyi

"Maraba,qaraso ciki mana,na tambayeki abokiyar zaman naki tace kina gida kina girki"
murmushi cikin jin nauyi ruqayya ta saki. Hukumullah ta fada a ranta,duniya juyi juyi,wai yau
itace hajiya ke tambaya?,ita din da a baya hajiyan kan fadi cewa kada a sake zuwa mata da
ita?,ita din da a baya take cewa ta gaji da ganinta,yadda ta ganta jiya haka zata ganta gobe da
jibi ma?. Kauda wannan tunanin tayi,ta zauna saman pillow din da hajiyan ta tura mata ta soma
gaidata cikin tsantsar ladabi da kunya. Amsawa tayi cikin kulawa itama,ruqayyan ta waiwaya ta
gaida sauran 'yan uwanta dake falon. Waiwayowa hajiya tayi ga wata dake a tsaye

"Lu'ubatu a kawo mata abinci ko?" A ladabce ruqayyan tace

"Bari naga me jegon tukunna hajiya"

"Gasu can acan dakin sun cikawa jama'a kunne da hayaniya" dan qaramin murmushi tayi tana
miqewa. Tunda ta shigo take jin tashin hayaniya sosai a dakin,saita ratsa ta isa ga dakin.

Za'a iya cewa a cike yake dakin,saidai girmansa ya sanya kowa ke zaune a sake ba
tare da an takura ba. Hira suke qwarai ba qaqqautawa,zainab na daga cikin 'yan committee na
hirar don da alama ita ke bayarwa ana amshewa. Sallamarta tasa hayaniyar ta ragu,sai idanu
kuma sukayo kanta,wasu na amsa sallamar yayin da wasu suka buge da qare mata kallo ciki

harda Zainab dake tunanin yaushe ruqayyan ta dinka atamfar nan?.

Raliya dake zaune daf da zainab ce ta tabota murya qasa qasa

"Kin ganta kuwa sai yanzu,lallai ita me aji" waiwayo zainab tayi sannan ta tabe bakinta

"Tana can miji ya maidata jaka,sai data gama girki da gyaran gidan,kinsan ni duk ranar girki ne
lallabani yakeyi,kada na gaji dare yayi ya kasa morar dadi,duk ran girkinta a wahala take
qarewa,uban kayan ciki ya hadata da dahuwarsa,a dafa mana,mu koma mu kwashi banza ba
tare da mun tsinana komai ba" ta qarashe zancan tana kwarara dariya raliya na tayata suka tafa
ji kake fass. Dariyar tasu taja hankulan wasu a wajen,banda ruqayya data tattara hanakalinta ga
dan jaririn fatima. Fatima mutuniyarta ce qwarai,zata iya cewa cikin dangin mijinta ba wadda
suke dasawa da ita kamarta. Tana riqe da yaron tana duba ciwon idanun da fatiman tace kamar
yaron yana yi.

Batulu ce dake gefansu ta dubi zainab dake dariya saman fuska,amma qasan
zuciyarta kamar an watsa garwashi,don sosai black prince din jikin ruqayya ta tsone mata
idanu,sai wani sheqi takeyi da daukar idanu

"Wato ke sauqaqqan girki ake baki ko?,sharp sharp"

"Ashe dai kin gane" ta fada tana watsa mata wani kallo. Dariya batulu ta saki

"Yo ni ai banga wani gata a nan ba,hasalima gani nakeyi kamar ya raina sanwarki ne da
iyawarki,shi yasa yake dabara ya kawo ranar girkinta don yasan bazai bata kudinsa ba" da sauri
ta waiwayo tana duban batulu,dama akwai 'yar tsama kadan tsakaninsu. Batulun irin matan nan
ne da basu barin ko ta kwana,hakanan basu da tsoro
"Eh,ai gaskiyar maganar kenan,sanwarta tafi taki dadi,ai na tabacin farfesun naki,hakanan
nasha cin girkin anty ruqayya ko wajen hajiya kuwa"

"Hajiya kuma?" Ta tambayi batulu

"Eh,lokaci lokaci ai ruqayya nada qoqarin wannan aiken kam,sai aka dace hajiyan nason
sanwarta" sosai maganar ta daketa,don bata taba tunanin kaiwa hajiya koda silin taliya ba a
matsayinta na 'yar 'yaruwarta,hajiyan mada tudu biyu a wajenta,babarta kuma uwarmijinta,bata
kuma san ruqayya tana yi ba,asalima ita din tana cikin matan da suke ganin kaiwa uwar miji ire
iren wadan nan abubuwan ba komai bane sai tarin bautar da kai. Tunda dai komai saleem yana
siya yakai mata ai ba buqatar sai an kai mata dafaffe koda sau daya a wata ma kuwa. Idan
Allah ya kawota baqunta taci,idan batazo ba haramiyarta a kuma sauka lafiya.

Ci gaba da hirarta batulu tayi suna gaisawa da ruqayya kuma cikin fara'a da sakin
fuska. Sallamar basira ita ta katse sauran tunanin da Zainab keyi ta tattarashi ta watsar,farinciki

kuma ya maye gurbin bacin ranta,ganin basira kawai ta tabbatar yau din akwai harka. Muryarta
kuwa tafi ta kowa dagawa

"Kaga basira me kayan harka,Allah ya barmu dake ki jima kina yi" mamaki yadan kama
ruqayya,don ta tabbatar har yanzu su hajiya na zaune a falon,kuma tayi imani suna iya jiyo
komai

"Ai inata sauri hajiya zainab karki tafi"

"Wa?,ni?,Allah ya kasheni musulma naga kayan harka na tafi ban kwasa ba,ke a banza nake
zaune a gidan alhaji saleem?,banda wadan nan abubuwan da tuni boka da malam sun jima da
tsigeni a gidan" ta fada tana tafa cinya gami da kallon gefen da ruqayya ke zaune a sace tana
gogewa babyn idonsa da magani.
Zaman dirshan basirar tayi ta kuma zazzage jakarta,take mata akayi caaa,na waje ma
da basusan me ake ciki ba sai gasu da daya da daya suna gangarowa. Yawancinsu amare ne
auren watanni masu haihuwa daya zuwa uku hudu. Yaran mata sosai da sukejin ludayinsu yana
kan dawo suka cika cacim.
"Duk wadda bata da kudi ma kada ta damu,har adashi inayi,sai na saka kowa a wassuf guruf"
basira ta fada cikin jin dadi da farinciki. Tunda take fadi tashi da buge bugen sana'o'i bata taba
cin karo da sana'ar dake da wani irin mugun farinjini da kawo zallar madarar kudi a nan take ba
irin wannan sana'ar
"Ni wallahi wanann nakeso,da alama aikinsa yafi na dukka magungunan nan" zainab da
hankalinta ya dauku ta fada tana daga kwalbar dake cike da wani abu me danqo,an lullube
kwalbar da wani rubutun hatimi da wani tsinke a maqale

"Yana da kyau akwai kuma aiki,amma gaskiya duk nan ba kaya me tsadarsa,tafiyayye ne tun
daga sakkwato" sai tayi qasa qasa da muryarta

"Kinsan Allah daga gidan malamin aka karbominshi ana kawomin shi na jefashi a jakar nan na
fito nayi nan,wannan ma na wata hajiya ne,idan kinaso zan yiwa malamin magana yayi miki
naki hadin na musamman" a take Zainab taji qaunar maganin ta shigeta. Kai ta girgiza

"Wallahi ko na uban waye saidai tayi haquri,bani da kudi amma ina da kayan kudi,zan bayar a
barmin shi,nawa kudinsa yake?"

"Fisabilillahi a bisa sauqi shi da wannan ruwan....." Ta fadi tana miqa hannu ta dauki wani ruwa
da yasha gamje gamje harda su dan tsami da gishiri da sauran tarkace ya koma brown,tana
zaune kuma idea din hakan tazo mata

"Idan kika hada aikinsu yafi zuwa dai dai,ki bada dubu arba'in da biyar,amma wallahi tallahi na

rantse miki da Allah har dubu sittin na karba a kansa" kai zainab ta girgiza tana juya maganin a
hannunta

"Ai kuma na yarda hajiya,ni dama ba kasafai nakeson maganin dari biyar dubu daya ba,ko a
baki wani sassaqen bagaruwa ko sassaqen malmo ace wai ka dafa tsumi kasha,tsumin
me?,kafin kiga aiki miji ya gaji da jin shuru maqatau?" Ta fada tana daga murya hadi da gatsine
duk don ya isa kunnen ruqayya. Ta jita amma ta bawa banza ajiyarta,hasalima dariya ta
bata,saboda a wajenta wannan hade haden da zainab ke yiwa kanta tabbas abar tausayi ce ita
idan batayi da wasa ba. Kawai fargabarta daya kada ta kwaso abinda zata qunsawa saleem
itama kuma ya sanmata.

Cikin lokaci kadan hannun basira ya cika da kudi dumus,aka kwashe kaya tsaf sai
ragowa. Idanu ta shiga wulgawa a dakin tanason ganin wanda bai siya ba taja raayinsa,don so
take ta fita da kudinta gaba daya. Ruqayya ta hango sai ta dubi zainab daketa shirya
kayayyakinta qasan jaka cike da farinciki. Tasan kishiyarta ce amma ita ba ruwanta neman
kudinta takeyi,don haka ta dan daga murya

"Hajiya azo a yiwa me gida gyara mana,kayanmu ingantattu ne sai an gwada akan san na
qwarai" kamar ta dorawa Zainab guduma aka haka taji,ita basira zata yiwa haka?.

Fatima dake zaune tana cin tuwo gefan ruqayya ce ta zunguri ruqayyan,ba tare data
kalleta ba murya qasa qasa tace


"Don Allah kema anty ki saya mana kiyi gyara" murmushi ta saka bata dubi fatima ba tace

"Hajjaju Allah ya bada sa'a" kai tadan sosa

"To amin,amma ko kudi ne baki dashi ai ina lamuni,idan kika gwada yayi aiki kya biya daga
baya"

https://chat.whatsapp.com/EKyzZCUEGyRAEGGAnTHmGF


*_KURMAN BAƘI_*⚫⚫⚫

*HUGUMA*

PAGE 09


Murmushin takaici ruqayya ta saki,gaba daya babu nutsuwa ga matar bare ka samu
gamsuwar abinda take saidawa

"Kiyi haquri banacin bashi,ma hadu wani jiqon idon da rabo"

"Allah ya qara,mtsweew......banda rainin hankali na gama siyan kaya a wajenki saboda saiki
tallatawa kishiyata,idan baki wasa ba billhuwallazi bazan qara siyan kaya a wajenki ba" zainab
dake jibgawa basira harara ta fada. Ganin zatayi asara ba wan ba qanin saita tura dankwali
gaban goshi
"A'ah me yayi zafi?,idan ma kin ajiye yo ba kanki kika yiwa ba,itama da bata siya ba kanta ta
yiwa"

"Gwara data yiwa kan nata,indai itace zatayi miki cinikin maganin mata zaki daina cin abinci da
kudin magani a duniya,banda taci kayan ganye taci nama da coca-cola batasan komai ba"
Dariya muqarraban Zainab din suka saki. Sarai ruqayya taji,amma hankalinta yana kan fatima
suna maganarsu.
"Ba yunwa kika ce kinaji ba amma zaki balle magunguna ki fara sha?" Raliya ta fada tana kama
haba idanunta akan fuskar zainab

"Bana bori da sanyin jiki nifa,gobe nike da turaka gwara na watsa tun yanzu subi jikina,yunwa
wannan ba matsalata bace,don bata hanani shan magani abuna" tana gama fadi ta fara tuttula
na sha da dama sauran da suke na gari.

Sallama aka sakeyi daga bakin qofar,na'ima ce wadda daya ce daga cikin family din
nasu,kakanni suka hada dasu saleem,saidai ita babarta 'yar Maiduguri ce. Hannunta dauke da
wata babbar jaka tayo sallamar,sallamartata kuma ta hade da qamshi wanda ya cika dakin
lokaci guda.
"Nima ga hajata ayimin ciniki bayin Allah" ta fada tana dariya tare da kutso kai cikin dakin.

"Hajiya zee,a zazzagen bakin jaka" ta fada tana murmushi idonta kan zainab wadda tayi tatul da
maganinta tana jin tabbas gobe zata sake jarraba sa'arta. Ko da saleem baiyi appreciating nata
ba tayi imanin da taimakonsu take zaune a gidan,kuma yana jin dadinta ne,wannan ya hanashi
asirin farraqun da ruqayya keta qoqarin yi musu ya kasa kamashi
"Ai kinzo a makare hajiya niimatu,na cinye kudin jakata harda bashi ma a kaina" zainab ta fada
tana basarwa,don batajin zata wani tsaya siyan turare bayan saleem ne yake siya musu,wanda
yake siya dinma ita idan suka dameta kyautarsu takeyi,ko kuma idan tana da buqatar magani
ayi ban gishiri na baka manda,ta bada su a bata magani hankalinta kwance
"Aikodai ban makara ba,shi turare da kike gani shine mace ai,bari na bude miki su ko baki
shirya ba kikaji qamshinsu saikin siya"

"Allah fa ni bani siya,karma ki buden qamshinsu ya cikan ciki magani na gama sha yanxu" ta
fada tana yamutsa fuska

"Wayyo Allah ya baki lafiya,ko an gamu ne?" Na'ima ta fada tana dariya

"In sha Allah kwanan nan za'a gamun dai" ta fadi tana dan washe fuska,don yanzu duniya kaf
burinta shine ta samu cikin 'yan biyu maza kamar yadda ruqayya ta haifa,idan hakan ta kasance
kuwa gida ya gama tabbata nata ne kaman yadda ta gama sakankacewa da hakan a baya.

Ta danyi ciniki,wasu a dakin sundan sissiya,saidai ko kwatar wadanda suka siya
maganin basu siyi turaren haka ba,wasu dai sun shanshana sun kuma yaba sun aje suna
addu'ar Allah ya bada sa'a.

"A'ah, aunty ruqayya?" Na'ima dake shirin barin dakin ta fadi don sai a sannan ta ganta

"Hajiya na'ima inata miqo gaisuwa ai bakijini ba" ruqayyan ta fadi tana murmushi. Sauya
akalarta tayi zuwa sashen da take zaune

"Wallahi hankalin yayi gaba" ta fadi tana zama gabanta.

"Bari kiga asararriya,duk gefen kama turaka babu ita,ta saki bishiya gaba daya ta kama ganye"
zainab da dariya ke cinta ta fada tana tabo raliya.

"An fara DJ" wata muryar mace data leqo ta fadi,take kuwa kamar ana jansu da majayi suka
fara miqewa suna fita da kadan kadan,sai gashi dakin ba kowa daga ruqayya sai fatima dake
canza kaya sai na'ima da batulu dake ninke kayan da fatiman ke cirewa.

"Ga turare a siyawa yaaya saleem" na'ima ta fada tana murmushi. Murmushin itama ruqayya
tayi

"Ai dole na siya turaren nan,tun kina shigowa naji yamin qamshi" sosai na'ima taji dadi,
ruqayyan nada wani irin karamci da bata taba iya kushe abinka.

"Allah aunty?"

"Allah,wancan da kika bani kyauta yamin dadi sosai,yanzu ma nake son dama na tambaya ko
kinzo?"

"Nazo anty ban shigo bane da wuri" na'ima ta fada tana fiddo mata da turarukan.

Da gaske turarukan masu kyau ne sosai da tsananin qamshi,guda hudu manya
ruqayya ta ware sai humra baqa da fara da kwalaccam sukayi total ta miqawa na'ima kudin.
Tana ta qoqarin neman canji ruqayyan tace

"A'ah ki riqe ki siyawa mutuniyata najma biscuit"

"Har haka

7 / 24