Me Kamar Sarki Book 2 Hausa Novel

Author :  Yusrah Musa Category :  Complete Novels

Chapter   14 / 67

39K to 42K   out of 200.4K words

ki nemi wata uwar" ta karasa maganar tana juyawa da sunguminta kuka sosai lami keyi ta durkusa a gaban Baffah tana cewa "dan Allah Baffah ka fahimtar da ita tayi min afuwa ita fa mahaifiya tace bazan iya jure fushinta a kaina ba hakan barazana ne ga zuciya ta da nasan abinda zai faru kenan bazan bishi ba zanyi ta hakuri ina zama cikin duhun jahilci na馃様.

Kallon ta Baffah keyi cikin tausayawa da rashin jin dad'in ganin yadda take kuka kamar ranta zai fita ya shiga jin wani irin d'aci na masa yawo a makoshi kirjinsa na zafi a fusace ya mi'ke yana zuwa kofar d'akin Ramatu yace "ke Ramatu kina ina? Caraf Ramatu ta bankado labule tana cewa "ga yar mutum biyu jikar mutum hud'u me ya faru ake nema na"? Ran Baffah a 'bace yace "kinsan Allah Ramatu ranki zaiyi mugun 'baci akan yarinyar nan sam babu d'igon imani a tare dake saikin kashe ta da 'kuncinki da kike sanya ta ciki to bari kiji yau kam kin kaini bango kibi a sannu zan iya yin komai".

Shewa Ramatu tai "ahayye nanaye yau ake yinta tofa ran maza ya 'baci lallai malam wato nan din me kake son nunawa zakasa nayi abinda banyi niyyar yiba Lami ce nace na sallama ta yadda ta za'bi tabi bare to yanzu ma haka ta dauka baren ya fini ta koma gunsu nace babu ni babu ita har raina haka abin yake babu kuma wani abu da zai canza".

"Haka kikace ko Ramatu"?.

Tana kad'a kai kamar zata hau bori tace "eh nace hakan malam, meye ko kana tunanin zanji tsoron kane? Nasan karshen abun bazai wuce kace zaka sake niba kuma ni yanzu dama haka nake so na samu 'yanci na nayi yawo a gari naci uban kowa na taka na murshe na wanke biyar na tsoma goma na fantama duk inda raina yake so" shiru Baffah yai na d'an wani lokaci kafin ya juya yana kallon Lami da har lokacin take kuka yace.

"Ramatu idan har baki yafewa Lami ba nima bazan ta'ba yafe miki abinda kikai min ba a rayuwa zaki ga karshen ki shiyasa nake miki kashedi tun wuri ki tuba ki canza kafin lokaci ya'kure miki".

Yana juyawa Ramatu taja tsaki tana cewa "wa'azi da zaka gane da ka dena dan wallahi babu abinda zaka fad'a min yai tasiri a raina ko yasa na sauko daga halina har abada muje zuwa koni ko kai".

Baffah babu yadda ya iya haka yayi ta lallahin Lami da fad'a mata magana me dad'i har yayi sa'a ta daina kukan ta saki ranta suka fara d'an zance yana matukar jin kaunar yarinyar da tausayin ta a ransa yana ganin bai kyauta mata ba daya auri Ramatu ta kasance uwa gare ta duk saiya tattara laifin ya dorawa kansa.

Satin d'aya da dawowar Lami aka daura auren Tanko tayi kuka ta kara harta gode Allah domin a dandali a gaban mutane yaci mata mutunci yace tabi son zuciya da kwadayi ta za'bi zaman wudil a kansa yanzu ya cireta a shafinsa lokacin da Ramatu taji harda dariya haka ta tusa Baffah a gaba da baka'ken maganganu wai ga abinda ya jawo nan batai karatun arziki ba ga wanda take so yayi aure yanzu a saiya ji'ka ta yasha.



Wudil zaune Naja'atu take tare da wani saurayi suna hira da murmushi a fuskarsa yace "wai nikam ba kuyi magana da Lami ba sai yaushe zata dawo nifa ina kewarta sosai duk na shiga damuwa" itama murmushin tayi tana cewa "hum Alpha kenan kaifa ina jin Lami bazata dawo ba domin dam bada amincewar mahaifiyar ta tazo ba inaga ta koma garin su da zama".

"Da gaske kike Najat"?

"Wallahi da gaske nake Alpha zanyi maka wasa da tunani ne".

"To amma wayar dana bata fa idan na kira bata shiga kullum a rufe me yasa"? "Oh ai dama bata tafi da ita ba tana gidan mu sai bayan tafiyar ta ina gyaran d'aki na ganta" dafe kansa yayi yana cewa " to yanzu idan zan ganta ya zanyi garin zaki raka ni ko kuwa? Gaskiya ina son ta da aure ba yaudara ba shin zaki iya taimaka min"?.

Murmushin jin dad'i naja'at tayi tana cewa "me zai hana ni kaina alpha ina son zaman Lami a kusa dani mun riga mun saba bana jin dad'i yanzu da bata nan".

"Ok shikenan karki damu zanyi magana da abbanku duk abinda yake akwai zaki ji" "to nagode sosai alpha" mi'kewa yayi yana mata sallama itama ta mi'ke suka fita tare kowa ya wuce gida.

MRS AL'AMEEN AHMAD CE 馃槝

Sai mun sake had'uwa a gaba masoya na masu yabo gareni godiya 馃挅馃挄馃挌 sosai sosai godiya.

Think before you do 馃え.

#Vote

#comments

#share

#fallow.

yusrahmusa65@gmail.com MAMAN LITTLE ZARAN AUNTY 馃拑馃憣馃憤.

YUSRAHMS ABUBAKAR.

21~AL-BASIT

The extender

22~AL-KHAFID

The abaser

11~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Sajidinah.

馃尮馃馃尮馃馃尮馃馃尮

馃寗DISCONTENT馃寗

Episode 21 nd 22

Wata daya tsakani Musbahu da baban alpha suka zo nemawa masa auren Lami Baffah yayi farin ciki yayi godiya ga Allah ya kara yayi addu'a da fatan alkairi da sanyawar albarkarsa da samun zuriya ta gari sannan ya ro'ki Baffah akan zai tafi da Lami su Naja'atu sun damu ta koma tunda hutu ya rage saura sati daya a koma Baffah kuwa dad'i yaji a take yace ta dauko kayan ta su tafi itama Lamin taji dad'i sosai da sauri kuwa ta had'a komai bata ta shirya ta bisu suka tafi.

Bayan tafiyar su Ramatu ta dawo batasan me ake ba hakkinta na uwa itama dole ya fad'a mata tasan abinda ke faruwa bazai biye halinta ba zata wuce yace.

"RAMATU" da sauri ta waigo ganin kaya turus a gaban Baffah yasa ta washe baki tana cewa "na'am malam gani nazo ne"? "Eh magana zamuyi" kamar an jefota yaga taxo ta zauna tana le'ken babbar ledar dake gaban sa yace "to malam gani nazo in kaji kira an samu amma banda kiran dan sanda".

Shiru Baffah yai yana kallon ta ganin baice komai ba tace "malam ka kira ni kuma kayi shiru"?.

Sauke ajiyar zuciya yai yana cewa "ina fata yanzu kam zaki fahimce ni duk da nasa ke baud'addiyar mace ce wacce ba'a gane inda al'kibilar ki take amma ya zama dole na fad'a miki yau dazu bayan fitar ki Musbahu yazo tare da wani mutum wanda d'ansa yake son Lami sunzo nema masa aurenta kuma na basu duk da banyi shawara dake ba amma ya kika ce kema mahaifiyar tace kina da hakki a kanta ga dai kayan da suka kawo nan da kud'i".

Zaro ido Ramatu tai gani kud'i daure a kyaure dami guda baki washe tayi tana cewa "ayya malam ai bakai laifi ba meye a ciki basai kai shawara dani ba ai kaida kaya mallakar wuya ne" ta karasa maganar tana dauko 'kwallelan goro daga cikin ledar ta soma garza tana cewa "yaushe zasu sake dawowa ne nifa ban gane cewa mutumin nan yana son Lami ba saiyau kace gara daya dauke ta suka tafi gashi harda abin arziki ta samo saurayi d'an birni" kai Baffah ya jinjina lallai kam wato idan akace mutum nada son zuciya sai a hankali yayi mamakin ganin yadda Ramatu ta amince Shi dai farin cikin sa daya Lami zata bar kauyen nan taje ta zurfafa karatun ta tayi ilimi ta cika burinta.

"Malam me kake tunani"? Ramatu ta fad'a tana sake cewa "malam aban nawa kason zan rabawa dangi" .

Cikin mamaki Baffah yace "kason me"? Kud'in dake gefe ta nuna tana cewa "garin su Mariya zanje in an jima nasan kayan lambu sunyi na saro Lami ta fara min talle" "telle kuma"? Baffah ya fad'a yana kallon ta "eh talle saita tara kud'in da za'a saya mata yan kayan d'aki da kayan katako" "a'a indai dan wannan ne ki barshi ni zanyi mata komai".

Daina cin goron Ramatu tayi bakinta daya sauya kala zuwa ja ta bud'e shi tana cewa "amma dai malam zilama ce tasa kace haka"? Wani kallo Baffah ya mata tare da maimaita kalmar "zilama"? Ba kunya Ramatu tace "eh zilama nace kake dashi malam bada zilan zilan irin taka ba da had'ama taya zakace kaine zakai mata kayan d'aki dan karka bani ko sisi shine kace wani kaine zakai mata to wallahi bazan yarda ba domin nice nayi na'kuda na haifeta na fika iko da ita wato dan ka je ka sayi ru'babbun Kaya shine kace a barmaka ragamar komai a hannun ka".

"Ramatu meyasa ko kadan baki da tunani? Ni kike cewa haka? Bansan ranar da zaki hankali ba shiyasa kullum nake godewa Allah da bai sa Lami tayo halinki ba" mi'kewa Ramatu tai "malam me kake nufi kenan karya nayi"?.

Ransa a had'e yace "ban sani ba ban guri" wucewa Ramatu tayi tana cewa "wallahi kome zai faru bazan yarda malam ehe idan kuma ba haka ba saidai a fasa auren" Baffah bai sake kulata ba ya tattare kayan da kud'in ya shiga d'aki.

Nan labari ya kardad'e gari ko'ina sai gulma ake wai Lami tayi saurayi d'an birni zata koma can tabar rayuwar kauye lokacin da labari ya iske Tanko hankalin sa ya tashi haka nan yaji yaji bayaso ta auri wani nan ya fara shiga da fita ya rasa inda zaisa kansa yaji dad'i dan haka ya yanke shawarar zai samu iyayen sa suje nema masa auren Lami ba haku yai ba.

Abokin Tanko Mudi wanda ba'a ganin tsakanin su shi Tanko ya samu yana fad'awa matsalar sa yace kuma ya bashi shawara Mudi yace masa kawai suje su samu Lami idan suka hure mata kunne tuni zasu rusa ala'kar ta da d'an binnin saiya aureta Tanko ya yarda haka zaiyi idan ya samu ya shawo kanta saiya lalla'ba ya saki Karime tunda d'akin sa daya ne.

Lokacin da Tanko ya samu iyayen sa da wannan maganar sunyi mamaki kuma ransu ya 'baci cikin fad'a Delu tace "a lallai Tanko ka raina mana hankali wa ma naji kana zaka aura Lami ko? To wallahi ko Ramatu ce baka isa ba aidai itace ta haifi Lamin ko? gaskiya Tanko ka cika mara tunani Lamin data za'bi birni ta share ka ta manta dakai shine yanzu saboda baka da zuciya kai kuma kake kokarin rufa mata asiri bayan ta tona maka kai kuma sakarai kawai".

Shiru yai yana sauraren su malam balah shima da haushi ya gama cika shi yace "kai Tanko kada ka kuskura naji ka sake firta sunan Lami a gidan nan baka da hadi yanzu da ita ko mutuwa zakai baka isa ka auri Lami ba kuma abinda na yanke kenan" tashi kaba mutane guri shashashan banza shashashan wofi" tashi Tanko yai yana fita a majalisar su ta matasa masu shaye shaye yan iskan gari yaje ya zauna ba sukuni kowa yana harkoki suna ta busa haya'ki amma shi yayi shiru ransa a mugun'bace.

Ta'bo shi Mudi yai yana bashi sigarin dake kunne yace "mutumi na kadan busa ko zaisa ka kadan ji dama dama" kai Tanko ya girgiza batare daya kalli Mudi ba 'kara matsowa kusa dashi Mudi yai yana yin kasa da murya saboda Ilyah na gurin yace "aboki na ko akan maganar Lami ne su baba sun amince"? Kai ya sake girgizawa yace "taya zasu amince sai fad'a suke min da ihu wai ban isa ba kuma wallahi idan kaga ban aure taba to numfashi nane ya yanke domin ina son ta bazan yarda ta auri wani bayan niba ko meye zai faru har kisa zan iya yi" kasa da murya Mudi yai yana cewa "kaga Tanko ka daina d'aga harshen ka dole ne na taya ka cika burinka ka shirya gobe zamuje gurin ta muji ta bakinta in ta amince saika dauketa ku gudu kaje can wani gari ka aureta daga baya kamar shekara biyar sai ku dawo nasan duk tsiya idan kuka dawo baza suce komai ba dole su barku kuyi rayuwar ku wai mutum da ransa da lafiyarsa a hani shi jin dad'i"?.

Tsaki Tanko yai "gane min hanya makaho yaso gulma amma ai su ba komai suke ganewa ba nabar haka a gigin tsofa ke damunsu amma zan saita musu zama" kai Mudi ya d'aga "yauwa aboki gaskiya suna takura maka gara ka nuna musu kaima na zamani ne d'an duniya ne shiyasa ni nake murna da nawa suka gangara tun ba yanzu ba gashi ni kadai suka haifa ba wa ba 'kani ga gadon gonaki sai fanjan fanjan nake da kud'i kaima ina maka fatan haka" kai Tanko ya jinjina yana cewa "idan mutum ya'ki mutuwa sai a 'karasa shi" dariya Mudi yayi yana cewa "kai mutumi na kana wuya ina binka da fetur haka ake so ka nuna kai d'an zamani ne me zama kan uwar d'an yaro, kaga karbi haya'kin nan ka d'an ja zakaji dad'i" karba Tanko yai yana sawa a baki Mudi ya sake dauko wata ya kunna.

Kwana uku da zuwan su Musbahu Ramatu ganin babu Lami babu alamarta yasa tace "malam nifa kwana biyu banga Lami ba ina taje ne"? Kallonta Baffah yai "au sai yanzu zaki tambaye ni inda take duk da baki lura ba? Ta bi ubanta sun tafi" so'ko'ko Ramatu tayi tana kallon Baffah tace "waye kuma ubanta bayan kai"?.

"Musbahu ranar da suka zo ro'kon arzikin ta yace an kusa komawa makaranta kuma yaransa sun damu da rashin ganinta shiyasa nace kawai ta shirya su tafi".

Zaro ido Ramatu tai tana mi'kewa tsaye tace "meeehhh馃槻 sun tafi kuma? Wai komawa gurin sa ta sakeyi kenan lallai Lami ta raina min hankali tabdijan wallahi bazai yuwu ba sai naje na taho da 'yata bana son harkar gidadanci dan yaga wancan karon daya dawo da ita na share shi shine yake neman tashin hankali aiko ya sameshi tunda ya ta'bo ni".

'Daki ta wuce tana masifa ko kayan jikin ta bata sauya ba du'kun du'kun haka ta dauko kud'i ta fito tana cewa "malam nayi wudil zan taho da 'yata tunda naga idan na zuba ido za'a raba ni da ita ayi min haifi in mora ina zuwa zan wuce ofishin 'yan hisba sai an mana iyaka dashi babu shi ba 'yata har abada ehe".

Ci kanki Baffah baice mata ba tayi hanyar fita da sauri da wasu ru'babbun takalma a 'kafarta da kallo Baffah yabi ta baice mata kar kije ba ko dawo ko bada yawu na ba ya share ta tayi gaban kanta "malam bakace min komai ba"? Ramatu ta dakata tare da juyowa tana kallon sa dauke kai yayi daga saitinta bai tanka ba, "malam kana jina kayi shiru wato baka so naje na taho da 'yata ko"? Jin har lokacin yayi mata banza yasa tace "malam ko zakace daga wudil idan na dauko Lami na zarce gidan mu wallahi bazan fasa ba sai naje ballantana baka tanka min nikam nayi gaba malam sai ayi zaune ayita jiran tsamani" tana kaiwa nan tayi gaba.

Shiru Baffah yayi yana sake kallon kofar gidan gashi magriba ta kusa ya tabbata kafin taje anyi sallar isha ba sanin anguwar tayi ba kawai saboda neman rashin zaman lafiya ta d'ebi kafa ta tafi........................

"BAFFAH" jin an kira sunan sa yasa ya d'ago ganin Sabi'u yayi tsaye da murmushi a fuskarsa yace "zauna man" zama Sabi'u yayi yana cewa "Baffah ga tsire inji Habu yace a taho ma dashi daga kasuwa ba yanzu zai taho ba ni kuma ga kayan marmari na sayo maka Baffah kasha" kallon Sabi'u Baffah yayi yana cewa "to sannun ku da kokari Allah ya muku albarka ya 'kara bud'i ya haskaka lamarin ku" "Amin Baffah kuma na had'u da malam Yahuza yace na gaishe ka" "ina amsawa sosai Allah yai albarka" mi'kewa Sabi'u yayi yana cewa "Amin Baffah" kafin ya dauki buta ya d'ebo ruwa yana mi'kowa yace "lokacin sallah yayi Baffah" kar'ba yai cikin jin dad'i yace "Allah yayi albarka abun da kuke min Allah ya baku 'ya'ya masu hali irin naku su rama muku Allah yasa su faranta muku" "Amin Amin Baffah mun gode da addu'ar ka garemu" "a'a ba komai Sabi'u jeka maza kayi alwala ka taho masallaci kar lokaci ya 'kure" to Sabi'u yace yana shiga d'akin Salamatu itama ya bata nata sannan ya fito yana daukar butar da sauri jin ana neman shiga sallar.

'karfe sha biyu da kusan rabi na dare Ramatu na cikin garin wudil tana bulayi tayi nan tayi can ta rasa inda zata sa kanta da wani mutum suka had'u da sauri tace "dan Allah kasan wani Musbahu"? Kai ya girgiza "ban sanshi ba zaki iya karawa gaba" yana fadin haka yai gaba da harara Ramatu tabi shi tana cewa "ji min mitsiyaci kada Allah yasa ka sani shashasha kawai mai ba'kin hali" cigaba tayi da tafiya sai tambaya take kowa yace bai san shiba takaici ne ya kama Ramatu ga gajiya ga yunwa harda bacci take ji ganin ta rasa mafita ga jama'a sun fara raguwa a layi sai ihun karnuka yasa ta samu wani bakin shago ta zauna tana zafga hamma ta kalli gabas ta kalli yamma.

Tsaki taja tana cewa "wannan wacce irin ba'kar jaraba ce ace idan mutum yazo gari baida kowa shikenan ya zama bola ba Wanda zai kula ka balle yaji matsalar ka ya taimake ka bari na tsaya na kwana anan din kar nayi gaba na had'u da kare gari na wayewa zan cigaba da cikiya................................

Ihu taji an kurma da karfi ana cewa "ihuuu jama'a ku fito 'barawo ku bishi gashi can yayi ta nan ku dauko abin duka haba da sauri Ramatu ta mi'ke tsaye tana gyara daurin zani tace "tofa yau nake ganin bankad'a iri iri wanne irin barawo kuma........ji tayi ana gashi can ku harbeshi kada fa ku bari ya tsere kallon gurin tayi aiko ta hango barawo yana cin gudu ana binsa ganin ya nufo wajen inda take yasa da sauri tayi gaba a guje taje shan kwana a bisa tsautsayi ji kake gammm!!!! Tayi karo da mutum tuni tayi baya rim ta fad'i cikin azama mutumin ya d'aga kokarar dake hannunsa ya buga

14 / 67