WASAN KANIN MIJI BOOK COMPLETE BY TAKORI.pdf

Author :  Sumayya Abdulkadir Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   9 / 19

24K to 27K   out of 57K words

da ‘tissue’ ta ce,
“Insha Allahu Momi kamin in gama karatun nan na shekaru biyu zan kawo miki mijin aure na”.
Momi ta ce, “Da dai kin yi wa rayuwarki gata, amma ba wannan neman duniyar ba”.

Ranar litinin jirgin Egypt - Air ya sauke Lailah a birnin Jiddah, ta yi masauki a AL-JAMJOUM
zuwa washegari ta bi bus ta wuce cikin Makkah da niyar aikin Umarah.
Kwanan ta uku a Mecca cikin aikin Dawafi da neman gafarar Ubangiji a kan komai ma, tun safe
har dare ban da lalurar dan Adam ta ci da sha da shiga bayan gida ba abin da ke raba ta da
dakin Allah.
Daga nan ta wuce Madinah, ta kai ziyara shabbaki da duk inda ya kamata. Kwananta biyar ta
wuce Jami’ar Ummul-Kura.
Duk wasu cike-ciken takardu na ‘registration’ da ma an riga an gudanar da su ta computer, sai
dan abin da ba a rasa ba.
Ta zavi zama cikin ‘hostel’ din dalibai don ya fi mata kwanciyar hankali, ta soma karatunta cike
da himma da karfin zuciya.
Bayan tsayin watanni uku suna karatu suka samu hutun sallah break. Ta yi ‘booking’ jirgi sai
Egypt. Inda shigowarta harabar gidansu kenan ta soma cin karo da taron yara sa’o’in su Sanah
kowanne ya ci kwalliya kamar ranar ne sallah.
Sanah da Najat sun dora wuka kenan za su yanka ‘cake’ din ‘Birthday’ din su suka hango ta
tana ratso mutane. Suka yi wancakali da wukaken hannunsu suka sheka suka rungume ta.
“marhaba biki Ya Ablah” (Ablah suna ne da suke kiranta da shi sau tari, wanda ke nufin Yaya)”
Dole sai tare da ita aka yanka ‘cake’ din suka daddanna mata a baki aka yi tafi, sannan
kawayensu suka soma rero wakar ‘happy birthday’ cikin harshen Larabci, na cikar Sanah da

Najat shekaru goma-goma.
Don haka wunin ranar zungur hidimar da suka wuni yi kenan a gidan har magariba. Sujood na
asibiti an ba ta ‘bed-rest’ tana laulayin ciki mai wahalarwa.
Ba su samu kevewa da Momi ba sai lokacin barci. Suna hirarsu a hankali irin na da da mahaifi.
Lailah na ba ta labarin jami’ar Ummul-Kura da irin tsarinsu wanda ya bambanta da na Azhar.
Momi ta ce
“Af! Kinga kuwa na manta mutumin nan da ya rako ki Bahaushe ya zo bakya nan”.
Saura kadan Lailah ta fado daga gadonta, Momi ba ta yi aune ba sai ganinta ta yi durkushe a
gabanta, kirjinta kamar ya fashe saboda bugu.
Ta ce, “ABBAS?”
Momi ta ce, “Kwarai haka Isma’il ya gaya min sunansa”.
Ta ce, “Ya tafi?”
Momi ta ce, “Tun a ranar, domin daman a kan hanya yake zai wuce gida Najeriya daga London.
Ya ce ya zo ne ya gaishemu kawai, bai yi tunanin kun rabu da Mohd ba, ya dauka kina
Najeriya”.
Lailah dai gaba daya ta bushe a zaune ne don gigicewa, don ma tana kokarin saisaita kanta
kada Momi ta fahimci rikicewar ta.
To amma ai Momin ba karamar yarinya ba ce, ta fahimci akwai wani muhimmin al’amari
tsakanin Lailah da abokin tafiyarta, tun ranar da ta kasa cin abinci don an sanar da ita ya tafi, ba
tare da ya yi mata sallama ba.
Ta ce, “Hala saurayinki ne tun a Ingilar taku?”
Ta zaro ido kuru-kuru ta ce, “Wane irin saurayi Momi?”
Ta soma bai ma Momi labarin haduwarta da shi tun a filin jirgin saman Abuja ranar da za ta
tashi zuwa Birtaniya, da yadda ya taimaika mata da rayuwarsu a makaranta da gida.
Ta kara da cewa, “Ko da kuskure mutumin nan bai tava sauya kallon da yake min na kanwarshi
ba, ya taimake ni a kowanne fanni na rayuwata a can.
Ya kare min mutuncina domin da dama kallon mijina ake yi masa ko Yayana, don haka babu
wani mahaluki da ya tava dosa ta da zancen banza har na baro Ingila”.
Ta kare da cewa, “Momi shi ya yi min nasiha na dawo gida, shi ya hanani zub da ciki, Momi
Abbas yana da kirki sosai, kuma wallahi Momi shine irin mijin da nake mafarkin samu a
rayuwata”.
Momi ta yi murmushi ta ce, “Har kin sa ina son shi”.
Ta ce, “Kirkin shi ya wuce duk yadda kike zato Momi, ga tarin ilimi. Shi ma (Philosopher) ne, don
da ya kare karatu a take makarantar ta dauke shi cikin sababbin malaman ta”.
Ta ce, “Dan ina ne?”
Ta ce, “Kano-Nigeria”.
Ta ce, “Garin su mahaifin ku....”
Lailah ta ce, “Yauwa Momi, wai Babanmu ba shi da wasu ‘yan’uwa ne a can Najeriya?”
Ta ce, “Mahaifin ku maraya ne, amma akwai Baffanninsa guda biyu Kano a unguwar Kabara,
ban sani ba ko suna raye”.
Lailah ta ce, “Ya kamata mu neme su Momi, kinga dai yadda rashin dangin uba ya janyo min
gori da rashin kima a gun Hajiyar Mohammed”.
Ta ce, “Isma’il ya san inda suke, idan kun kara dawowa sai ku je, amma ni ba inda za ni”.

Lailah ta saki wannan hirar ta ce,
“Momi bai ce zai sake dawowa ba?”
“Wa kenan?”
Cike da jin nauyi ta ce,
“Abbas”.
Sai ta yi murmushi kawai ba ta ce mata komai ba.
Ko da Isma’il ya shigo daukar ma Sujood wasu kaya da za ta yi amfani dasu a asibiti bai ce da
ita komi ba game da zuwan Abbas.
Ta kasa daurewa ta ce, “Zan iya binka muje wajen Sujood?”
Ba tare da ya juyo ba ya ce, “Basu barin aje dubiya kar a damu mara lafiya”.
Ta ce cikin fargaba, “Ashe Abbas ya zo?”
Ya juyo yana kallon ta, shi kansa ya rasa dalilinsa na tsanarta, ya ce, “Eh, wani abune?”
Ta hadiye kukan da ya taho mata ta juya da gudu ta yi gidansu ba tare da ta ce da shi komi ba.
Ta kwanta rub da ciki a kan gado, tana kuka mara sauti, wanda ta toshe shi da bakin mayafin
abayarta kada Momi ta jiyo sautin kukanta.
Ba ta ji murda kofa da rufe ta ba sai zaman mutum a gefen ta. Kamshin turaren shi a gefenta ya
sanya ta dagowa da sauri, Isma’il ne.
Ya mika mata hankicif dinshi ya ce, “Share hawayen”. Cikin sassanyan Larabci.
Ta karva ta share amma ba ta dube shi ba. Ya yi shiru sannan ya ce, “Ki gafarce ni, haka nan na
samu kaina da daina ganin farin ki. Domin........”
Ta kai hannunta ta toshe masa baki don ba ta son jin abin da zai fada, zancen nan ne dai da ba
ta so a kara tuna mata.
Ya sauke hannunta daga bakinshi ya ce, “To ki yi hakuri”.
Ta ce, “Na yi”.
“Abbas ya zo baki nan, ya yi mamaki kwarai jin cewa all these while kina gida. Amma baki
neme shi ba, na gaya mishi ko waya baki rikewa. To amma zai dawo”.
Ba ta so ya ga ta fiya ci-da-zuci. Da ta tambaye shi yaushe zai dawo din?
Ya mike ya fita yana cewa, “Sujood ta damu tana so ta ganki. So ki daure ki yi ko sati ne ta
dawo ta ganki”.
Ta ce, “Allah sarki Sujood, Allah ya raba su lafiya”.
Ya amsa
“Ameen”.

Washegari ta tashi da nishadi, don haka ta je aka yi mata kunshi da gyaran gashi, akaifa da
wankin kafa. Ta wuce makaranta ta dawo.
Bakuwar mota ta gani a harabar gidansu, ta karasa ciki da sassarfa bayan ta rufe motar ta.
Mohammed ta fara yin tozali da shi, sannan Sa’eed da wasu kyawawan mata guda biyu da fara
da baka.
Tana tafe cikin falon har hardewa take yi, ya yin da Isma’il ke ta wadata ‘dining’ da abinci da
abin sha shi da Amatullahi mai aikin su.
Momi na gefe ita da A’isha suna ta hira, Momi na ta zuba shakakkiyar Hausarta kamar jakar
Kano.
Kallo daya Lailah ta yi wa Sa’eedu ta ga yadda ya rame ya lalace kamar ba shi ba, ta dauke kai

kamar ba ta ganshi ba.
Za ta wuce ciki Momi ta riko hannunta ta ce,
“Baki ga bakin naki bane?”
Dole ta zauna gefen Momin tana kallon su kawai da idanu. Sa’eed na kuka bayan shigar su
A’isha sassan baki, yake rokonta ta yafe masa, ta yafewa Mohd.
Don a dalilinta yanzu Mohd ya aje aiki, ya ce, tunda aikin ne ya raba shi da ita, yake kuma
barazanar raba shi da duk matar da ya aura to ya barshi, zai gwada wata sana’ar.
Kuma anyi masa aiki, yanzu haka A’isha na da ciki wata biyar. Wannan kuma Zanira matarshi
ce, ita ma ‘yar uwarsu ce. Shi kuma ba shi da lafiya suga ta kama shi sosai.
Shi yana kuka Lailah na yi. A da kam ta yi alkawarin ba za ta tava yafewa Sa’eed ba har
karewar numfashinta, amma a yau ta tuna wani karin magana da Hausawa ke cewa.
“....... Idan vera da sata.....to daddawa ma da wari”.
Sai ta ce, “Allah ya yafe mana bakidaya”.

Ta zage sosai ta karvi su A’isha, karva ta karshen mutuntawa. Shi dai Mohd sai ido yake binta
da shi ganin yadda ta kara komawa yarinya danya sharaf ba ‘yar shekaru talatin ba.
Soyayya gaskiya ce, kuma har abada ba ta gushewa. A haka yana ji yana gani ya baro Lailar
da a da mallakinsa ce.
Ba ta koma Saudiyya ba sai da Sujood ta fito daga ‘bed-rest’. Har da ita aka yi mata rakiya ta
tashi ranar Asabar.
Ta tarar da abokiyar zamanta a dakin (Dhuha) ta riga ta dawowa. Ta gyare masu dakin tsab.
Balarabiyar Afghanistan ce.
Suka ci gaba da karatu, wanda duk rabi bincike ne cikin manyan littattafai wato (research).

Tana tsaye gaban book-shelf na main library din Ummul-Kura, tana kokarin zaro wani littafi.
Dai-dai lokacin da agogon library din ya buga karfe goma sha daya na rana, ya yi dai-dai da
bugawar zuciyarta da faduwar gabanta. Dai-dai lokacin ta hango wani ‘giant’ yana tahowa cikin
fararen kaya, iska na kada shi, yana tafe yana waya, ba ta san lokacin da littafin ya suvuce, ya
fadi daga hannun ta ba.
Ba ta yi wani motsi ba har ya karaso . Ya russuna ya dauko mata littafin ya mika mata, sannan
ya kama hannunta suka fito daga library din. Ta zamo kamar mutum-mutumi, sai janta yake
tana binshi ba uhm-ba-umh-uhm.
A al’adarta tunda ta zo Ummul-Kurah, kullum sai ta kai ziyara shabbaki, kamar ya san hakan,
don kuwa da ya tare tasi shabbaki ya ce ya kai su.
Kasancewar masallacin maza daban da na mata, a nan harabar masallaci ya sata ta yi
addu’o’inta, shi ma ya yi. Suka fito ashe tuni ya yi masu ‘booking’ din mota wadda za ta kai su
har cikin Mecca.
A cikin mota Lailah ke bin shi da idanu, yadda ya damke hannunta kamar wata matarshi. Abbas
dinta.....abokin kan hanya!
Ya kara kyau na misali, ya kara murjewa. Ta yadda har ba ta gajiya da kallon kyakkyawar
fuskarsa.
Ta sunkuyar da kai cikin siririn sauti ta ce, “Amma ka san hannun nan da kake ta rikewa,
haramun ne ko?”

Ba ta kai ga rufe bakinta ba sai ya sa dukkan hannuwa ya rungume ta.

Lailah ta samu numfashinta yana sassarfa a cikin kirjin Abbas da kafadun shi. Ta yi ta kici-kicin
ta kwace amma ta kasa. Ta kuwa daga hannu ta kai mishi wani wawan mari ya goce, hucin
marin ya wuce ta gefen kunnuwansa. Ta fashe da kuka ta ce,
“Saboda na baka labarina shine ka dauke ni ‘yar iska ko?
To bari ka ji, ko na fi iblis iskanci ba zan yi a cikin garin da manzon mu ke kwance ba. Kai
malam tsaya da motar nan in sauka.....”
Ya yi dariya sosai, sannan ya sake ta. Ya nuna mata agogon RADO dake daure cikin
kwantacciyar sumar hannun shi.
“Karfe sha daya na rana wanda ya yi dai-dai da karfe biyar na yamma agogon mu na gida
Najeriya.
Baffanninki Malam Ado da Malam Ilyasu da waliyyinki Isma’il suka damka mani igiyar rayuwarki,
suka shaida na zama mijinki har zuwa karshen numfashinmu”.
Sai jikinta ya yi sanyi, ta rasa abin cewa, kuka za ta yi ko dariya? Bakin ciki za ta yi ko ko farin
ciki? Bata sani ba.
Ya sake runtse hannunshi cikin nata sosai ya soma ba ta labarin yadda al’amarin ya faru. Ta
tabbatar karfe sha daya na rana ta ji faduwar gaba da bugawar zuciya, ashe igiyoyin Abbas ne
suka hau kanta.
Ya ce,
“Na je Egypt watanni biyu da suka wuce in gai da Momi da Isma’il. Yake gaya mani cewa kina
nan Madina. Na tambaye shi Umrah kika je? Ya ce, a’a, karo karatu ne, don aiki kike yi. Ya ce
kun rabu da mijinki tun wancan karon. Ban yi kauron baki ba ko A BARI YA HUCE.... na ce da
Isma’il ya yi mani alfarma, ya aura min ke. Ban san ya suka yi da Momi ba, ta ce, in ba ta lokaci za ta yi nazari tana so ta ji daga bakin ki.
Sanda na sake komawa ta ce ta gama nazarinta in turo wakilaina wajen Baffanin ki a Kano su
za su sake daura miki aure.
Don haka Isma’il ya taho Najeriya muka hadu, muka je Kabara aka daura auren, sadakinki yana
hannun Isma’il
Ba yadda bai yi dani ba in bari za ki zo karshen watannan ban saurare shi ba, dole ya bani
adireshin inda zan same ki wato jami’ar Ummul-Kura.
Ban sha wuya ba aka binciko min lambar dakin ki. Na tura a kira ki sai abokiyar zaman ki ta ce
kina nan. To kin ji.
Nima ba dan iska bane. Da kuma dan iskan ne da ba yau zan fara ba......” Ya karasa da dariyar
da ta cunkushe masa ciki.
Ita dai Lailah binshi take da ido, mamaki ya hanata magana. Hakika tana cikin mutane masu
sa’ar samun duk abin da suke so a rayuwa. Da da hali da itama ta rungume shi ta yi kukan
godiya ga Allah a kan kirjinsa.
Sai yamma lis suka shigo cikin Mecca, ko abinci basu nema ba sai da suka fara yin (Dawafi)
suka yi sallar magariba da isha da nafiloli. Sannan suka je wani ‘restaurant’ suka ci abinci, daga
nan suka taho Ka’aba suka ci gaba da gabatar da ibadodinsu.
Sai asuba suka koma masauki, wanka kawai suka yi ya shige ciki ya kwanta yana biyan bashin
barcin da bai samu ya yi ba saboda godiya ga Allah da ya mallaka mishi abin da yake so, bai

kuma tava tsammanin samu ba, ya samu a bayan fidda rai.
Ita dai Lailah ko gezau, tana zaune dungurgur a kan kujera tana kallon talabijin din da ke ta aiki
ita kadai ba ta san me suke yi ba.
Kamar ka ce kyat.....! Ta arta a na kare. Don ita kwata-kwata yanzu kowanne namiji ma tsoron
shi take ji balle ya kai hannu ya tava ta.
Bai tashi ba sai karfe goma na safe, shi ma din kiran Isma’il ne ya tashe shi, suna gaisawa ya
mikawa Laila.
Bayan sun gaisa yake mata bayanin da Abbas ya yi mata, ta ce a sanyaye,
“Toh!”
Momi na karva sai ta valle da kukan kaunar da take mata. Tana so ma ta yi mata godiya amma
ta kasa.
Momi ta ce,
“To kukan na mene ne?
Ke fa da bakin ki kika gaya mani kina son Abbas?”
Ta share hawaye tana murmushi ba ta ce komai ba. Ta ce, “A’a, in kin daina son nashi ne ki
gaya mani sai in ba shi hakuri ya karvi sadakin shi, tun da dama bai zo hannun ki ba.”
Ta yi saurin cewa, “A’a Momi”.
Ta yi dariya ta ce, “To shi kenan, a sha amarci lafiya, ki kula da shan ‘fresh milk’ da cin dabino
da shan zam-zam tare da inibi”.
Kunya ta kama ta, don ta san sune abubuwan da take ba ta sanda za ta yi auren fari.
Abbas ya fito daga shi sai ‘short – nicker’ kanshi da tawul yana goge ruwan cikin sumar kanshi.
Kallo daya ta yi mishi ba ta kara ba ta kara takurewa a cikin kujera. Ya juya mata baya yana
dariya ya zuba farar jallabiya mai santsi, ya fesa turaren shi (one-man-show), ya fesa turaren
baki (mouth fresh), sannan ya iso gare ta.
Ya zauna a gefenta yana so ya ja ta jikinshi amma ya lura da yadda ta ke a tsorace da shi. Sai
ya yi murmushi ya mike zuwa hammam (bayan gida) ya hada mata ruwan dumi cikin kwami, ya
ce ta yi wanka ta ji dadin jikinta su fita su nemi abin karyawa.
Ba don ta so ba ta mike ta shiga wankan, amma fa ta kukkulle kofar bandakin da (jam-lock)
sannan ta fara wankan, shi kuma ya sauka kasa ya samo musu abin karin kumallo.

****
Kwanansu uku suna Umrah, amma ya kasa gane kan hutsuwar amaryar tashi. Ba ta umh ba ta
umh-umh, duk ta takura kanta. Maganar duniyar nan idan zai yi sai dai ta bishi da ‘eh’ ko ‘a’ah’.
Har yana mamaki kamar ba Lailan shi ba.
Ya kuma soma tunanin ko dai ba ta son auren ne. Ta hana mashi amarcin har zuwa ranar da za
su rabu, dama shi a kan hanya yake zai wuce London.
A daren ranar dai ya rantse yau sai ya gane abin da Lailah take nufi da shi, ba ta son shi ne ko
iya shege ne? Ita ba yarinya ba balle a yi mata uzrin kuruciya.
Tana zaune cikin kujerar falon hotel din da suka sauka, hannunta remote ne tana canza channel
ya kwankwasa kofar.
Ta tashi ta bude idanunshi cikin nata aka jefe shi da wani miskilin murmushi. Turata cikin dakin
ya yi da kafadunshi ya aje ledojin dake hannun shi. Sannan ya juya ya karvo na hannun yaron
hotel din da ke waje ya aje gefe ya rufe kofar.

Ba ta yi aune ba sai ji ta yi ya sunkuce ta ya yi sama da ita. Bai dire ta ko’ina ba sai cikin
kwamin wanka, duk da kayan da ke jikinta.
Ta

9 / 19