WASAN KANIN MIJI BOOK COMPLETE BY TAKORI.pdf

Author :  Sumayya Abdulkadir Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   7 / 19

18K to 21K   out of 57K words

da zaman auren da
Mohammed din da har gobe zuciya ba ta hutawa da kaunar sa, zaman ZINA, tana sane, wane
hukunci Allah zai yi mata?
Ta fashe da kuka sosai tana yi a hankali kada wani ya jiyo ta, kuka mai cin rai da soya zuciya.
Ta yi tunanin bari kawai ta je ta nemi shawarar Abbas a dakin baki, domin kuwa shi babba ne da
ya fi ta kaifin hankali da kaifin tunani.
Sannan shi ne mutum na farko da idan ta bi shawarar shi take ganin alfanunta. Bata nadama a
cikin duk shawarwarin da yake bata.
Ta fada toilet ta wanke fuskarta da sabulu, ta sauya abayar da ke jikinta ta murda kofar ta fito.
A babban falo su Momi ne da su Najat sun yi shimfidar leda suna cin abincin dare, sai lokacin
ne ma ta tuna rabon ta da abinci tun na daren shekaranjiya.
Amma wannan ba shine a gabanta ba, fita ta yi harabar gidan ta doshi dakin baki. Ta yi sallama
har sau hudu ba’ a amsa ba, sai ta murda kyauren ta shiga.
Babu Abbas babu ko jakar kayan shi. A kidime ta dawo falon tana tambayar Isma’il ina Abbas?
Hannu ya tura cikin aljihu ya fiddo ambulan fara tas ya mika mata. Ya kara da cewa.
“Ai tun zuwan Mohammed, da na gaya mishi shine mijinki ya tafi. Ya ce 4 o’clock flight zai bi
zuwa London.
Dama burinsa shine ya rako ki ya kawo ki gida, sauran bayanan za ki ji a cikin wasikar”.
Cikin sanyin jiki da kasala ta mika hannu ta karvi ambulan din.
Sanah ta cika plate da shawarmah ta mika mata, hannunta har rawa yake saboda yunwa. Ga
wata kewa da ta lulluve zuciyarta, irin wadda ta dade bata ji ba a rayuwarta, tun bayan rashin
mahaifinta.
Abbas wani mutum ne mai muhimmanci da kima a gare ta da ba za ta tava mantawa da shi ba.
Hanya ce ta hada su, amma tana jin shi da wani muhimmin matsayi a zuciyarta da ba za ta iya
tantance wanne irin, matsayi ne ba.
Ga dai mahaifiya ga ‘yan uwanta, ga kanne da yayye musamman Isma’il wanda a yanzu yake
matsayin tamkar mahaifi a gare su, amma jin ta take kamar ita kadai ta rage a duk fadin
duniyar.
Haka nan take caccakar abincin ba don dadi ko dadin rai ba, illa don ta faranta wa ‘yan uwanta
da mahaifiyarsu da suka zubo mata ido don ganin sauyawar da jiki da fuskarta suka yi da jin
cewa bakon ta ya tafi.

Ba ma kamar Isma’il dake kare mata kallo cikin nazari. Gaba daya ta susuce ta zama kamar
wata firgitacciya.
Tun dawowar ta ya fahimci da abin da ke damun ta, tana kokarin voyewa. Ganin cewa juriyarta
ta kare kada ta fashe da kuka a gaban su, sai ta aje cokalin a hankali ta mike ta yi dakinta.
Isma’il da Momi Najla suka bi ta da idanu masu cike da damuwa.
Ba ta bude wasikar Abbas ba sai da ta yi sallar isha’i, ta kara da shafa’i da wutri. Ta daga
hannuwanta sama tana hawaye tana rokon Allah ya yafe mata, ya kawo masalaha cikin
rikitacciyar rayuwarta.
Sannan ne ta bude wasikar Abbas, ga abin da ke rubuce:

LAILAH!
Haduwar kan hanya ce ta zamo haduwar zuciya...aminci, kyautayi da abota ne suka hadu suka
yi gingimemen gini a zuciya..., wanda hakan ya janyo zuciyar ta ke so, amma baki ya gaza
furtawa.....
Sai dai kuma sau tari fuska kan gaza boye zahirin abin da ke zuciya…… domin zuciyar na
ragaita, a rashin sani na ashe bani da ‘yancin wannan al’amarin....
Don haka na wuce London, a duk lokacin da kika tuna ni Lailah..... ki sanya ni cikin kyawawan
addu’o’inki. Ina yi miki fatan ALHERI.....

Ta dade tana maimaita wasikar Abbas, amma ta kasa fahimtar ta, ta karanta ya fi sau hamsin
amma ba ta fahimci sakon da yake son isarwa gare ta ba.
Wane al’amari ne ba shi da ‘yancinsa? Zuciyarta ta halarto mata da amsoshi da dama, ciki
kuwa har da mai cewa.
“BA SHI DA ‘YANCIN AURENKI TUNDA KE MATAR AURE CE......!”
Sai ta kwantar da kanta a kan dardumarta, tana hawaye. Abbas shine irin mijin da take so, take
fata, take kuma addu’a, Allah Ya bata, miji wanda ya san hakkokinta, ya ke wanzar da lokacin
shi da hidimomin rayuwar shi wajen kulawa da mace. Yake ririta ta tare da tattalin ta. Sai ta
samu kanta da kewar Abbas, kewa mai yawa kuwa. Yayin da daya vangaren na zuciyarta ya ki kewar Mohammed Jama’are, wanda ke son su koma
su yi zaman zina, da son ranta ko babu.
Ta alkawartawa ranta da dai ta komawa auran Mohammed, gara ta karasa rayuwarta babu
aure, don ba ta ga so da kauna da aminci a cikin shi ba.
A wani vangaren kuma idan ta ki Mohammed shi Abbas a ina za ta nemo shi? Ya ga mijinta ya
dawo ya yi tafiyarsa ba tare da ya yi mata sallama ba, balle su fuskanci juna su shawarta mafita
ga rayuwarsu.
Ina za ta nemo shi? Kano da girma, ina za ta nemo shi ba ta san komi a kan garin da yake ba
balle mazauninsa....
Ta kifa kanta cikin tafukanta ta soma kuka mai cin rai, kuka irin wanda ta dade ba ta yi a
rayuwarta ba. Kukan sabo, soyayya da kewa, soyayya mai laushi da taushi, da ba ta tava tsintar
kanta a ciki ba.
Daga karshe barci ya sace ta cike da mafarkai barkatai marasa kan gado, duk a kan
Mohammed da Abbas.
Don haka da kyar ta samu ta yi sallar asuba a kurarren lokaci. Ta koma ta kwanta, ba ita ta tashi

ba sai karfe goma na safe da Momi ta kwankwasa mata kofa.
Ta yi mika ta yi salati sannan ta zo ta bude kofar.
Kallo daya Momi ta yi mata ta ga fuskarta a kumbure, idanunta sun yi luhu-luhu sun yi jawur. Ta
kama hannunta, har bakin gadonta sannan ta rungume ta. Ajiyar zuciya mai nauyi ta suvucewa
Lailah.
Hawayenta suka kwaranyo a bayan mahaifiyarta, ta yi kukan ta ma’ishi, Momi Najla ba ta
dakatar da ita ba.
Ta tabbatar akwai abin da ke damun diyarta wanda zurfin ciki irin nata ba zai bari ta bude baki
ta fada ba.
Ta kai hannu tana shafar bayanta tana lallashin ta. Ta ce.
“Idan baki gaya min abin da ke damun ki ba Lailah wa za ki gaya mawa? Ni mahaifiyarki ce, da
ta tsuguna ta haife ki, nice farko da ya kamata in san damuwar ki, in yi kokarin da zan iya in
warware miki ita.
Jiya na ga Mohammed ya fito cikin fushi, sannan tun da aka gaya miki tafiyar wanda kuka zo
tare kin kasa ko cin abinci. Kar dai ki ce dani aure kika yi a kan aure Lailah?”
Magana take cikin sanyi, da zuciya irin ta UWA, sannan ta kakkafe ta da idanu. Lailah na girgiza
kai tana cewa.
“Lala-lala Ummi......”
A hankali ta soma zayyana mata komai. Ta kare da cewa.
“Kwanaki uku kacal ya bani in bishi mu koma a bar maganar, ko in kai shi kotu in kwaci takardar
saki.
Duk yadda na so in nusar da shi rashin ingancin aurenmu ya ki sauraro na. Har yana zargina da
yiwa kaninshi sharri. Ummi ina cikin wani hali na kuncin zuciya da rashin yarda da kaina......
Me zan yi Ubangijina ya yafe mani ya kawo mani maslaha cikin rayuwa ta? WASAN KANIN MIJI
bai kare ni da komai ba sai jefa ni a halaka da wanzar dani cikin bakin ciki da nadama....”
Ta ci gaba da kuka a kan cinyoyin mahaifiyarta.
Momi ta rasa abin cewa, sai LA’ILAHA ILLALLAHU….. Allah ya kawo mu wani zamani
gurvatacce..... zina ta zama ba komai ba, daga wajen marasa auren da masu auren ma.

Ba ta tava jin irin wannan kwamacalar a cikin aure ba, sai dai al’amarin da ya riga ya faru ba
abin da za a iya yi a kai sai dai ayi kokarin gyarawa, don a guji gaba.
Ta dago fuskar Lailah daga cikin cinyoyinta ta ce.
“Kema kina da laifi Lailah, me ya sa a lokacin da ya bijiro miki da bukatarsa baki yi wani kokari
na kare kanki ba?
Me ya sa kika zavi yin nisa damu fiye da ki gaya mana a yiwa tufkar hanci? Ayi abin da ya dace
tun a lokacin?
Laifuffukan ki suna da yawa Lailah. Kin tafi zuwa wata duniya ba tare da yardar mijin da ke
auren ki ba, kin kulla alaka da wani da namiji da ba muharramin ki ba. Me zai hana soyayya ba
za ta gitta a tsakani ba? Da aurenki Lailah?”
Lailah dai ba baki sai kuka. Ta yarda ita ma da laifinta. Ta kama hannun Momin ta rike cikin
nata.
Cikin rishin kuka ta ce,
“Na yarda nima ina da laifi Momi.....sai dai na tuba, na dade ina tuba ga Ubangijina.....tuba irin

wanda Ubangiji ya yi alkawarin karbar sa.... wato tuban da aka tabbatar ba za a sake komawa
izuwa zunubin ba”.
Sai Momi ta rungume ta,
“To yanzu me kike so da rayuwarki? Kin shirya zama mutuniyar kirki ko za ki ci gaba da yin
alakar kusanci da mazan da ba muharramanki ba?”
Ta yi saurin katse Momi da cewa,
“Na shirya zama ‘yar kirki Momi a gaba dayan sauran rayuwata......”
Momi ta ce,
“Aurenki da Mohammed ya riga ya lalace, sai dai dukkaninku ku yi hakuri da shi.
Maganar zuwa kotu domin karvar takarda a hannun Mohd. ma ba ta taso ba. Domin kanki za ki
tozarta. Za mu nemi sulhu da shi, jibin zan ganku tare. Amma ki yi dauriya, dole Isma’il ya ji
zancen nan, don shine waliyyinki.....”
Lailah ta zaro ido,
“Zai tsane ni Momi, zai yi Allah wadai dani Momi”.
Ta ce,
“Shirmen banza kenan, an ce da ke hannunka na rubewa ka yanke ka yar ne? Baki yi tunanin
hakan ba a lokacin da kike hutawar haram da kanin mijinki? Tashi ki bani wuri tun nima din ban
tsane ki ba”.
Mikewa ta yi tana goge hawayen idanunta. Ta shiga ‘toilet’ ta sakar ma kanta ‘shower’ ko ta ji
sanyi a zuciyarta.

****
[12/17/2019, 18:28] Takori: An zauna a falon marigayi mahaifin su Lailah a ranar (26) ga watan
Maris na shekarar 2000.
A gefen Mohammed Jama’are kanin shi ne Sa’eed Jama’are, wanda tun da ya shigo falon
kanshi ke sunkuye bai dago ba.
Sai Isma’il Yayan Lailah, kusa da shi Lailah ce cikin abayat da Momi a gefenta. Sai Hajiyar su
Mohammad a gefe wadda fuskarta babu alamun rahma, kada ma su ce sulhun a mayar da
Lailah gidan danta za’a yi, don a cewar ta Lailah karuwanci ta tafi Turai ba wani karatu ba.
To sai kuma kallo ya koma sama, a inda ta ji sulhun da Balarabiya Najla ta nema, wato a
warware auren Lailah da dan nata sakamakon kazantar da auren da suka yi da WASAN KANIN
MIJI.
Ta dube su tsaf, a ranta ta ce ‘yan kundun uba.
Sannan ta mike ta bugi kirjinta ta dubi Momi ta ce, “Ni Baida’u ban haifi dan iska ba, ‘ya’yan nan
biyu su Allah ya bani ban taba ji an ce an gansu suna aikata wani aiki na assha ba.
Balle Sa’idu ya nemi matar Yayansa da yake mutuntawa fiye da ni, yake kaunarta da zuciya
daya.
Ta je can ta nemi abokin shaidancin can a inda ta je karuwanci....Takarda kuwa ko baku ce ba
dama za a ba ta, don tuni na aurawa dana mace ‘yar usli wadda na san asalinta. Don haka.......”
“A’a, Hajiya ki yi hakuri ki zauna ayi maganar nan a tsanake..........” Sa’eed wanda ke sunkuye
da kai ya fadi cikin sanyin murya....
Ya kara da cewa,
“Don Allah Hajiya ki zauna....”

Ta koma ta zauna tana hararar sa..... Shi kuwa Mohammed jifanshi ya yi da wani kallo mai tarin
ma’anoni da dama.
Amma Sa’eed ya maida kanshi kasa, ba tare da ya sake hada ido da kowannen su ba ya ce.
“Hajiya da Yaya ku gafarce ni, tabbas abin da Lailah ta fada cewa mun aikata gaske ne. Mun
tava kusantar juna amma sau daya ne cikin ribatar shaidan.
Zancen haihuwa ne ban san da shi ba, don ina jin tun a ranar da al’amarin ya faru ta bar gidan,
nima ban kara ganinta ba ko ji daga gare ta ba sai yau.
Don haka Yaya ka yi hakuri, ka kuma yi min duk hukuncin da ka so.......kasancewa ta wanda ya
yi maka cin amanar da baka tava zato ba, na raba ka da abin da kake so, ba don ka daina son
shi ba.
Yaya daga ni har Lailah ta wani vangaran bamu da laifi, ko me muka yi kai ka bamu damar mu
yi shi.....”
Kafin ya karasa Mohammed ya kai masa wani wawan mari, ya bishi ya shake da kyar Isma’il ya
kwace shi. Ya galabaita yana haki abin tausayi.
Hajiya ta ce,
“Rufe min baki tun ban tsine maka ba, kai kuma Mamman rubuta takardar sakin ka basu idan ka
haifu cikin iyayenka......rubuta musu yanzun nan ka bani, ko in daga maka nono wallahi…….”.
Ya sunkuyar da kai hawaye fal idonsa. Isma’il ya bashi biro da takarda.
Yana rubutun hawaye na jika takardar, ya rubuta saki daya jallin-jal, ya mikawa Isma’il, ba tare
da ya damu ya goge hawayen da ke zuba tarara daga idanunshi ba.
Cikin macewar jiki Lailah ta daga ido ta dube shi, anyi sa’a a lokacin shi ma ya dago sashen da
take. Sai ta ji hawaye sun tsinke mata na tausayin Mohammed, tsohowar soyayyar dake
zuciyarta ta motsa. Da gudu ta bar falon ta yi cikin gidansu ta fada bisa gadon Momi tana kuka,
mai fita daga karkashin zuciya.
****

Kwata-kwata rayuwar Lailah ta sauya, domin duk inda macen da ta san ciwon kanta take,
wannan kalmar ta ‘saki’ ba karamin tashin hankali bane a gare ta, ko da auren kiyayya ne kuwa,
balle auren da aka gina a kan turbar so da kauna.
Gaba daya ta susuce ta fita hayyacinta, tsakaninta da mahaifiyarta sai gaisuwa, don tun ranar
da su Mohammad suka daga gida Najeriya ba ta kara ganin hakorin Momi Najla ba.
Ta ce sai ranar da ta ganta a dakin aure, sun daina jera kafada, sannan ita dai ba ta tava ZINA
a tsayin rayuwar ‘yammatancin ta ba, balle da auren ta.
Isma’il ko kallon ta ba ya yi balle ta ga hakoransa. Duniyar ta yi mata kunci ta buwaye ta. A
wajen kannenta su Najat kawai take jin sanyi, wadanda basa rabo da dakinta suna yi mata hira,
suna wasanninsu.
Aka kwashe sati biyu a haka, rama da zugewa da take yi suka addabi zuciyar Momi Najla.
Ta soma tunanin Allah ya sa ba kanjamau ta je ta debo a kanin mijin nata ba. Don haka yau da
safe Momi ta sanya ta a gaba suka nufi asibiti.
Laila na jin sanda Momi ke ce da likitan ta kawo ta a yi mata gwajin kanjamau ne. Sai hankalinta
ya kara tashi.
Ko numfashi da kyar ta shake shi. Wai me kowa ya dauke ta ne? Karuwa ko me?

(Kadan kenan daga irin bakin cikin da ‘ZINA’ ke haifarwa, domin ita ce karshen tozarci a
rayuwa, musamman ga diya mace).
Ba ta shaki numfashi sosai ba sai da result ya iske su cewa Lailah lafiyarta kalau.
Lailah ta kasa jure mu’amalar doya da manjan da Momi da Isma’il ke mata, don haka ta soma
tunanin kirkirarwa kanta abin da zai amfane ta.
Da farko ta soma neman aikin koyarwa a jami’ar da ta yi, ba ta sha wahalar samun aikin ba,
musamman saboda ingancin masters dinta na Ingila.
Ta shigo gida rike da tulin takardu a hannunta da gani a masifar gajiye take. Sanah da Najat
suka garzayo suka rungume ta.
Ta russuna dai-dai tsahonsu ta rungume su ta sumbace su daya bayan daya, ta tambaye su ina
Momi? Suka nuna mata dakinta.
Ita da Isma’il ta samu suna magana da kasafce-kasafcen tulin kudi a gabansu. Ko dai na
business dinsu ne ko na mene ne ba za ta ce ba. Domin Isma’il babban dan kasuwa ne. Ya kan
je Dubai da America kawo kaya kasar Egypt, sam-sam ya ki aikin gwamnati, duk da kwalayensa
na karatu masu inganci. Nan da nan dukkaninsu suka yi fuska suka daina zancen da suke, suka bi ta da kallo kamar sun
ga wata bakuwa.
A savule kuma kamar ta yi kuka ta zauna a gabansu, ta aje takardunta a gefe. Kadan ya rage ta
fashe da kuka.
Wai Momin ta da Isma’il ke nuna mata yau ita bare ce a cikinsu, don kurum ta yi kuskure a
rayuwarta?
Ta kai bayan hannunta tana share hawaye ta kasa cewa komai. Zuciyar UWA ta soma russuna,
amma Isma’il sai ya hau fada.
“Lafiya za ki zo ki sa mutane a gaba kina yi musu kuka kamar su suka saki kije ki zama ‘yar iska
ki ci amanar aure?”
Sai ta idasa rushewa da kukanta, ta ce,
“Na tuba Momi, na tuba na bi Allah na biku. Isma’il wane ne ba ya kuskure a rayuwarsa?
Idan kun juya min baya ina za ni? Idan kun watsar dani wane ne zai tallafe ni? Dan uwana ka yi
min aikin gafara kamar yadda nake nema a wurin wanda na yi wa laifin amma ba kai ba”.
Ya yi tsaki ya soma tattara kudin yana zubawa a jaka, ya ce da Momi
“Idan za su tafi kaiwa sai a gaya mani in raka su”.
Momi ta ce, “Babu laifi”. Ya sa kai ya yi ficewar sa.
Lailah wadda ke durkushe har zuwa lokacin a gabansu ba ta daina shesshekar kuka ba, kukan
da ya tava zuciyar Momin, ko ta ki Allah.
Ta mika hannu ta kama tattausan tafin hannunta ta ce,
“Ya isa.......ya isa”. Tana goge mata idanu da gefen abayarta.
Da kyar ta tsaida kukan ta jawo ‘file’ din

7 / 19