WASAN KANIN MIJI BOOK COMPLETE BY TAKORI.pdf

Author :  Sumayya Abdulkadir Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   1 / 19

1 to 3K   out of 57K words

 [12/17/2019, 17:50] Takori: WASAN KANIN MIJI
SHIMFIDA

1/MUHARRAM HIJIRIYYAH
HANYA MAI HADIN ZUMUNTAR DOLE!

Dare ne mai tsananin sanyi, cikin watan Nuwamba. Hazo ya lullube duhun daren ta yadda ya
fidda launi mai haske kamar hadadden hadari, wanda ya takura da yawa-yawan al’ummar birnin
tarayyah.
Za a iya kimanta lokacin da misalin karfe goma dai-dai na daren ranar Alhamis. Dai-dai lokacin
da LAILAH UMAR BALLAH, matashiya ‘yar kimanin shekaru (25) ta iso filin jirgin saman Abuja.
Laila tashe take da ‘yar madaidaiciyar ‘troller’ dinta ruwan toka a hankali, kamar mai tsoron
kada santsin tangaran din takawa (tile) ya tikar da ita. Rataye a kafadunta na dama, jakar mata ce baka mai girma samfurin (vincci) data hadiye
dukkan komatsanta masu muhimmanci.
Laila sanye take da doguwar abaya da mayafinta bakake wul! Kirar Oman, da takalmi rufaffe
maras tsayin dunduniya. Ta karasa ciki a hankali ta hau kan layi domin mika kayanta ga masu
binciken kwakkwafi na cikin gida (customs) kamin a auna su cikin jirgi. Tana daga cikin
(boarding passengers), masu tashi zuwa kasar England, a wannan daren mai tsananin sanyi,
mai kunshe da dimbin tarihi da kuma sabuwar rayuwa a gare ta.
Da ganin yadda Laila ke shige da ficenta, kai tsaye, babu tsoro, babu dari-dari, wajen mika
(passport) dinta mai dauke da Kambun Sarauniya (UK Visa) gami da katin shaida (ID Card), a
duk inda anka bukaci hakan kamar yadda ka’idar matafiya ta filin jirgin ta shimfida, ka san ba ta
da duhun kai; wato dai ba yau ne ta soma keta hazo ba. Sai dai kuma kallo daya za ka yi wa
kayatacciyar fuskar Lailah, ma’abociyar haske, zati da kamala, gami da kwarjini bayyananne
daga sarkin halitta, ka karanto matsananciyar damuwa, tsoro da firgici, har ma da tashin hankali
gami da matsananciyar nadama tattare cikin fararen kwayar idanunta.
Sai dai kuma ta kasance daya daga cikin irin mutanen nan da da wuya ka karanto damuwarsu a
fuska farat daya, kasancewarta ma’abociyar fuskar murmushi. Duk da haka a yau, babu
wannan murmushin, babu wannan annurin. Kamar yadda zuciyarta ke cunkushe da manyan
al’amura masu girgiza zuciyar diya mace, tare da jefata cikin rayuwar ha’ula’i, haka dan
kankanin bakinta ke tsuke tsam! Kamar ba ta tava murmushin ba a tsayin rayuwarta.
Ta daga kanta sama a hankali zuwa ga allon kwamfutar dake manne a saman kanta, mai dauke
da (travel-routine) na ranar gaba daya. (LONDERS-HEATHROW 12:am), kenan akwai sauran
mintuna talatin a gabanta, kafin su tashi.
Don haka ta bi layin sauran matafiya ‘yan uwanta a sansanin da aka ware domin tsimayen
lokacin tashin jirgi, ta samu kujera ta zauna. Ta bude jakarta ta dauko karamar gorar ruwan
(Faro) mara sanyi, ta murde ta kai bakinta tana kwankwada, cikin wani irin yanayi mara
fasaltuwa. Tsabar kishi ne ko ko gigicewa ce? Tun da ta kafa ruwan a bakinta ba ta iya ta sauke ba, sai da ta zuke robar gaba daya. Gardin
ruwan ya ratsa busashshen makoshinta da bakin cikin DA NAMIJI ya busar rayas! Ya saukar da
‘yar kankanuwar nutsuwa a zuci da gangar jikinta. Ta dire robar a kas, ta aje dogon numfashi,
kamin daga bisani ta sanya fuskarta cikin cinyoyinta ta fashe da kuka.

Wani irin kuka mai girgiza zuciya Laila ke yi, wanda ba ta tava yin shi a rayuwarta ba, kamar
yadda tunaninta bai tava bata wai watarana irin haka na zuwa da za ta yi shi ba. Balle a kan
MAZA, da ta raina ma wayau. Domin tana ganin ba ta daga cikin irin matan da ake cewa suna
dandanar bakin cikin DA NAMIJI. Tun da babu ta inda Ubangijinta ya rage ta; tana da kyau,
tana da gata, tana da gishirin rayuwa mai tsada (ilimi). Uwa uba nasabar mafi soyuwar jinsi,
wato Arab.
In haka ne to mene ne silar wannan balaguron gare ta? Zuwa inda ba Uwa, ba Uba, ba masoyi
balle dangi?

Har aka yi kiran (passengers) domin bincike na karshe wanda daga shi sai shigewa jirgi Lailah
ba ta ji ba. A gefenta yake zaune, tun shigowar ta, yana nazarin wata takarda mai dauke da
taswirar Birtaniya ciki da bai dinta.
Ya mike tsaye a yayin da kiran ya tsinkaye shi. Ya dauki jakarshi dake aje gefe mai dauke da
kwamfutar (laptop) tare da shafa aljihun bayan shudin wandon ‘jeans’ dake jikinsa domin
tabbatar da zaman tikitinsa da passport. Ya tabbatar suna nan. Don haka ya bi jerin-gwanon
matafiyan dake shiga jirgi bayan an bincike su. Sai dai har zuwa lokacin sautin shesshekar
kukan yarinyar mai taushi da raunana zuciya, ya kasa daina amo cikin kunnuwansa.
Ya yi taku a kalla biyar zuwa shida, amma ya kasa daurewa. Ya rage sassarfa, kana ya juyo. Ya
kai idanunshi ga sashen da ya barta. Har zuwa lokacin tana nan inda ya barta, har zuwa lokacin
kuma kukan take, kanta cikin cinyoyinta. Babu alamar tana da masaniyar cewa kowa ya tashi
daga wajen ya barta, kai babu alama ma ta tsinkayi kiran da aka yi musu.
Wankan tarwada, dogo mai tsararren tsayi, ma’abocin ingarman jiki. Cikakkiyar fuska mai
yalwar dara-daran idanu da wadatar dogon karan hanci zurr! Kai ka ce saita shi a kai a tsakanin
idanunsa.
Ma’abocin yalwar girar idanu kwantacce, gami da gargasa na gashi a kowanne gava mai
bukatar hakan a jikinsa. Dogo ne sosai mai nitsatstsen taku da wasu irin idanuwa masu sheki
da daukar hankali, kai ka ce ruwan zaiba ne aka diga masu (oily-eyes). Fatar jikinshi shine
bayyanannen sirrin kyawun da Allah yai mishi (fata ce irin mai taushin gani a ido). Sai ko wani
irin haske (cool) mai nuni da gogayya cikin zuzzurfan ilimin boko, wanda dole ne ga duk wani
bakin mutum mazaunin yankunan Birtaniya. Da gani babu tambaya, daga duba na farko, kaga
Ba-kanon usuli.
A sannu cikin nutsatstsen takun shi ya karasa gare ta, ya tsaya dai-dai saitin kanta, ya dau
kimanin mintina biyu a haka kamar mai nazarin, ya kamata yayi mata magana ne ko a’ah? Baya
daga cikin halayyar sa shiga haular da ba tashi ba, kamin daga bisani yayi kundumbala ya yi
mata sallama cikin murya mai taushi. “Kina daga cikin masu tashi kuwa?”

A hankali Lailah ta cira kai, kamar a dan razane. Ta kai duban ta ga sashen da sautin ya fito, ba
tare da duban fuskar mai maganar ba, idanuwan nan farare tas sun canja launi sunyi jawur
tamkar an gumbuda musu barkono.
Ta mai da dubanta zuwa hagunta da damanta, wayam, babu kowa. Ita kadai ta rage, ta yi
hanzarin mikewa ta rataya jakarta ba kuma tare da ta sake duban mai yi mata magana ba. Ta

ce, “Na gode”. Ta wuce babu ko waiwaye.

“Hakika Mallam Nasara kullum kara samun fasahar kirkire-kirkire yake…..”. Laila ta ce a
zuciyarta. “Wato jirgin ma yanzu sai dai kawai ka shige shi, ba tare da ka ganshi ba. Kafar shi
kafar hanyar da ka fito, sai dai kawai ka ganka cikin wani daki wai shi jirgi mai fuka-fukai. Inama
ace yadda yake da fasahar kirkire-kirkire, haka yake da fasahar rungumar kowanne jinsi da
zuciya daya, ba tareda wariyar launin fata ba?
A bayyane yake bature bai tava son baki. Ko ya so shin, akwai voyayyen dalili. Muhimmi shine
idan har ya san zai samu amfana daga gareshi.
An ce an bamu ‘yancin kai amma ba’a daina bautar damu ba. Turawan Ingila basa aiki, kwance
suke a gida, mu din dai har yau mu ke yi musu bauta. Suna kara bunkasa suna kara havaka
muna kara durkushewa. Masu fasahar mu sun tattare a gindinsu suna musu bauta. Suna kara
bunkasa su. Sun ki suzo su gina al’ummar su. Sun kasa ganewa har yau cewa shi dinnan
(nasara) makiyin su ne. Kansa kawai ya sani da al’ummar sa, su ‘bayi’ ya daukesu. A kullum
kara like masa muke muna kara dakusar da kan mu. Bamu da abin koyi sai shi da akidojinsa na
banza, alhalin halakar da kan mu kawai muke yi.

Ta juyar da idanunta ta wulwula cikin jirgin. Daga farkon shi har karshen shi bakaken fata kawai
take hange, musamman kabilar Yarbawa. Suna tururuwar tafiya bauta ma bature. Sun baro
iyaye da kakannin su cikin gonakin kauyuka suna noman Doya, Manja da Cocoa. Don samun
abin kaiwa baki, basa ko tuno su. Jar fatar usli dake cikin jirgin ‘yan kalilan ne, wadanda
yawanci aiki ne ya kawo su Najeriya. Lailah tayi tsaki tare da huci don karin bakin-ciki. To amma
me zata iya a kai? Sai ido sai du’a’i.
Tunaninta ya dawo ga tata rayuwar, da dalilin nata balaguron. Tana da yakinin cewa ba bautawa
Bature zata ba, kamar yadda mutanen mu suka raja’a a kai a UK. Neman ilmi zata. Domin ta yi
wa kanta hukuncin da addini ya tanadar a kanta, wanda ita kanta ba ta sani ba, a yanzun tana
nan a musuluncinta ne? Koko ta fita ne? Bata yarada da cikar imaninta ba….., bata yarda da kanta ba…..! Tana cikin rudani, tana neman
mafita,….. tana cikin nadama, tana cikin tsoron rashin cikar imaninta, tana cikin tsoron
mahaliccinta, tana cikin tsoron anya Ubangijinta zai yafe mata?
“Sa’eed!” Ta fada cikin rishin kuka. “Sa’idu!” Ta sake maimaitawa cikin karkarwar murya. A yayin
da ta zauna a mazauninta na kujera mai lamba (22), hannun dama, na cikin jirgin (British
Airways). Kafin wasu irin dumammun hawaye su kara wanke kyakkyawar fuskarta.
Ba kuma tare da ta yi wani kokari na sharewa ko voyewa ba ta ce a fili…..
“Allah ya isa tsakanina da kai Sa’eedu….Allah Ya isa!!!”
Ta sake mai da kai cikin cinyoyinta ta ci gaba da kuka.
Da a ce cikin al’ummar mu ne Lailah ke yin wannan sambatun, la-shakka da an tsaya kallon
zararriya-mahaukaciya, amma ga wadanda ba halayyarmu daya ba, ko kallon ta ba su yi ba,
kowa ta kansa yake, kowa kansa ya sani.
Babu wanda ya kula ya damu da halin da take ciki sai mutum guda, musulmi Bahaushe dan
uwanta, wanda har zuwa lokacin ke bibiyarta da ido, da zuciya.
“…..Budurwa har budurwa…., kyakkyawa har kyakkyawa, mai kyau matuka. Amma Allah sarki!
Watakila tana da ‘Psychological Problem”.

Ya raya cikin wasikar jakinsa.

Hakika duk inda musulmi yake, zuciyarshi ta sha baban da ta arne ko ya ya ne. Allah ya halicci
dan musulmi da zumunci ga dan uwansa musulmi, ko da basu hada jini ba, wato ko da haduwar
kan hanya ce. Musamman a inda suke sune ‘minority group’ wato a inda suke da karanci. To
hakan ce ta faru da ABBAS. Ya kasa dauke hankalinshi daga Lailah, ya kasa daina jin son
taimaka mata. Ko ba da komai ba; da son gusar mata da wannan dimbin damuwar da take ciki
ko ya ya ne, koda da fatar baki ne. He want to turn this sadness to joy…., he want to make
these tears- murmushi.

Jingine yake tuntuni a hanyar da ta raba first class seats da kujerun baya yana kallon ta, amma
tsayuwar shi bai hana masu wucewa hanyar wucewa ba.
Ya duba lambar mazauninshi jikin tikitin hannun shi, ya mayar aljihun bayan wandonshi. Ya
karaso inda take fuska cike da fara’a ya sake yi mata sallama a karo na biyu.
Kanta na fuskantar taga ne, tana kallon taurarin dake makale a sararin samaniyar subhana,
ma’abota haske gami da hasken fitilun lantarki kala-kala da ya mamaye duhun daren, tana iya
hangen gine-ginen gidaje, motoci da ma’aikatan birnin tarayya miri-miri kamar abebaden wasan
yara, kamar a tafin hannunta. Juyowa kawai ta yi fuska babu annuri, ba tare da nuna ya fuskanci halin da take ciki ba ya ce.
“Hello lady, can I’ve my seat here?”
Tare da nuna mata tikitinsa mai nuna cewa shine ‘occupant’ na kujerar da ke manne da tata,
wato mamallakin kujera ta (23).
Hannu kawai tasa ta dauke jakarta da ta dora a ‘seat’ din ta ajeta kasan kafafunta. Ta mai da kai
inda take fuskanta tun farko, wato tagar jirgin, ba tare da ta ce da shi ci kanka ba......
“Taron tsinannu! Taron mugaye, taron mayaudara, macuta, maha’inta, ‘yan tofin Allah tsine! Duk
kune........ MAZA!!!”
Ta ce cikin zuciyarta. Tare da kai tausasan yatsunta ta yarfe wasu matsiyatan hawaye da suka
kara shimfido mata.
“Iko sai Mai-Duka!”
Shi ma ya fadi cikin-cikinsa.
“Watakila bayan ‘Psycho-disorder’ Mamanta ko Babanta sun rasu, a wannan hutun da taje na
‘summer’. Allah sarki! Gaskiya ba karamin rashi bane rasuwar iyaye. Karewa ma, it’s the
greatest loss of all losses! Shi zai gaya ma kowa ya ya rayuwar dan Adam take wakana babu
iyaye? Ya ya dan Adam yake ji idan bashi da wanda zai zo ya rava, ya saki jiki da zuciya ya
gaya mishi damuwar shi? Ya ya yake ji idan ba shi da mai daukar nauyin lalurorin rayuwarsa,
har ya samu ya mike ya gina kansa?
Sai dai kuma Allah ya kawo mu wani zamani da (dutyn) Uwa ko Uba kawai shine su kawo ka
duniyar, amma ko kai kadai za ka iya rayuwa, idan har ka san me rayuwar ke nufi, da inda ta sa
gaba.
Sai ka fuskance ta a yadda ta zo, ka manta da komi, ka kasance mai binsu da addu’a.

Aka ba da shelar a daura ‘belt’ jirgi zai nausa. Kowa ya daura ban da Lailah. Sarkin sa-idon
nata ya kuma cewa a ransa.

“To ko dai ba ta ji ne?
Amma kuwa a ganinsa da hakan bai sa ta kuka ba!.
Sai me don Allah ya rage ka ta wani fannin?
Ai dole ba zai hada maka komi 100% ba. Dole idan ya baka wannan ya hana maka wancan don
ya jarrabi imaninka ya ga cewa, za ka gode da ni’imomin da yai maka ne ko a’ah?
Za ka butulce ta hanyar kuntatawa kanka? Idan ka gode sai ya karo maka da wata falalar daban
ta inda baka zata ba.
Don haka a ganina in nine ke ‘yammata ba zan yi kuka ba. A hakan zan daddage in jure in
fuskanci rayuwa. In shiga al’amuran duniya a dama dani domin babu maraya sai raggo. In
kasance mai godewa Ubangijina (Yawaita Hamdala) wannan ba shine karshen rayuwar ba!!
Kuma babu cutar da Allah ya saukar ‘yammata ba tare da ya saukar da ita tare da maganinta
ba, sai tsufa, sai mutuwa.
Sai in ci gaba da neman waraka. Sai dai hakan ba yana nufin zan dakatar da al’amuran ci
gaban rayuwata bane, a’ah, ci gaba zan yi, har zuwa sanda (Arrahmanu) Sarkin Rahma ya ga
damar yaye mini. Idan kuma ya fi son ganina a hakan? Ow.k! All it takes….!!!”.
Shi kadai yake ta sake-sakensa, har da su watsa hannuwa gami da yarfar dasu tamkar wani
zautacce sabon kamu.
Haka ita ma ba ta fasa kukanta ba, ba ta kuma da alamun dainawa. Sassanyan sautin kukan na
kara ratsa kunnuwansa, tare da yamutsa tunaninsa a kanta. Yana kara raunana raunanniyar
zuciyarsa, musamman kasancewarsa mutum mai matukar rauni a kan tausayin MACE.
Zuciyarshi ta gama lugwigwita, domin tun da yake bai tava jin irin wannan kukan ba, mai girgiza
zuciya, mai ratsa kashi da vargo. Tsigar jikinshi ya soma tashi, bai san sanda ya rintse ido ba ya
ce.
“Na hadaki da Allah kanwata ki daina wannan kukan!”
Da sauri ta cira kai ta dube shi da jajayen idanunta da suka rine kamar gauta. Yana son yin
shisshigi a kan al’amarinta......
“Haka kuke da farko,… nuna tausayi da kulawa, har sai mace ta yi kuskuren fadawa a tarkon
ku, sai ku cuce ta ku raba ta da farin cikinta……”
“Kuka na dinga yinshi kenan…. har karshen rayuwata!”.
Magana take a zucci, ba ta san har ta suvuto ta fatar baki ta shiga kunnensa ba. Murmushi ya yi
kamar bai ji abin da ta ce din ba.
Ya ce, “ ki daura ‘belt’ din ki”. Ba musu ta jawo ta makala a kugunta. Don kada ya sake damun
ta da magana, ta sake mai da kanta cikin cinyoyinta.
Ya dauki ‘earpiece’ da aka ajiye a kowacce kujera ya manna ma kunnen shi, tare da murdo
rediyon BBC harshen Hausa yana sauraro. Sai dai a zahiri ya yi hakan ne domin kare
kunnuwansa da raunanniyar zuciyarshi daga sautin kukanta, mai lugwigwita zuciyarsa da
kassara gavvan jikinsa. He donno why her cry weakens him…..(bai san meyasa kukanta yake
raunana zuciyar shi ba). Mai raguwar zuciya ba zai iya daurewa ba sai ya tayata, and he don
want 2 be among….. !(baya so hakan ta faru dashi). Jirgi ya mike sosai bayan ya gama
ruguginsa mai gigitarwa, ya soma keta hazo ya naushi kasar Birtaniya.

Sai da ya kama hanya sosai ya zare ‘earpiece’ din tare da daukar karamin bargon ‘British-Air’
ya warware ya rufe jikinsa, daga kafadu zuwa cinyoyi saboda wani irin sanyi da ya soma keta

vargon jikinsa. Wanda inda sabo to sun saba.
To haka da yawan al’ummar jirgin suka yi, aka yi light-up wasu suka soma barci. Wannan ma
duka ban da Lailah.
Ya mika hannu aljihun bayan kujerar da ke gabansa ya dauki mujallar (TNT) ya soma buda
shafukanta, ba don komi ba sai don kawar da hankalinshi daga kan wadda ba ta damu da shi
ba, bare al’amarin sa.
Ba ta damu da kowa ba, ba ta san me yake yi ba. She’s undoubtedly suffering a zuci, ruhi, fuska
da gangar jiki, da al’amarin da duk tunanin mai tunani ba zai tava bashi ba.
A fuska she looks innocent…. A kwayar idanunta tsoro ne karara….. A shimfide kan fuskarta
nadama ce tsantsa….. A karance kan siraran levvanta istigfari ne. Zuba suke tarara daga cikin
idanunta, hawaye ne.
Baya iya banbance rubutun da hotonan da ke cikin mujallar, baya ganin komi a kansu face
kyakkyawar fuskar Lailah, tare da sauraron zazzakan sautin kukanta.
‘Yammatan jirgi zuka-zuka, farare kal cikin vingil-vingil din (minis) da rufaffen takalmi, bakaken
‘suit’ da shudin ‘tie’.
“Looking so cool...........”
Ya fada ta hanyar motsi da tausasan levvansa. Sai dai kuma duk gyaran ku da kwalliyar ku you
are not as good looking as she is, (baku kaita kyan

1 / 19