Inaaya Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Billyn Abdul Category :  Adventure Stories

Chapter   28 / 43

81K to 84K   out of 128.5K words

matsayi agunsa,

Duk yanda yake tsananin kaunarki idan kina nuna Jin zafi ko kishin kusancinsa da Haj umma Zaki iya jawa kanki matsala,

Ki cire tunanin komai ki maida hankali kan aurensa dake kanki Dan yanzu duk wani shashanci ki ajiyesa ki fara sanin aurene akanki.

Kuma ki koyi hadiye Abu Dan Allah Inayah sbd banson afara samun damuwa tunda wuri tsakaninki da mahaifiyarsa tunda dai ba zaunawa zatai har abada ananba dole wataran Zata tafi,
Nima zuwa gaba kuna fara taramun 'yan jikoki Zan barku ayita kaimun renonsu..koba haka ba?

Ko har shirin auren da kukai keda Neesah ya wargaje sbd Abbi ne mijin ba'a aura masu rawar Kai ba..

Da 'yar tsokana ta qarasa zancen tana shafa kan Inayah sbd ta sake Dan tasan Zata iya kwana da damuwa aranta.

Murmushi kawai Inayah tayi tana safe lafewa tace"

Umma yaganah ai Abbi ma kila ya manta da cewa nifa yanzu matarsace..

Nidai umma yaganah kiyi Masa tuni nifa yanzu ba 'yarsaceba kawai Ni matarsace Dan Allah ya......

Buge bakin umma yaganah tayi tana cewa"

Zaki fara ko?
Ba nace ki ringa Kama bakinkiba idan bakisan me Zaki fadaba.

Umma yaganah fa kinaga ko Dan kallon mace bayamun saina 'yar baby Inayah wadda ta.......

Bazakiyi shirunba kenan?

Shiru tayi tana hadiye sauran zancen Dan ita idan matsayin Mata zaisa kulawan Abbinta yadawo Mata Zata zabi hakan da sauri.

Zubbi ce tayi knocking kofar dakin tashigo tareda Dr farhat wadda taketa zuba qamshi Mai Dadi da adonta na doguwar Kuwait Abaya red fes da ita kaman ba dareneba.

Abbi ne yakirata ta taho duba Inayah,

Qarasowa tayi fuskarta daukeda murmushi da kulawa tana gaida umma yaganah kafin ta zauna gefen Inayah tana cewa"

Oh my baby meke damunki?

Abbinki yakira hankalina ya tashi na dauka sosai ne jikin naki,

Meye matsalar?

Tashi zaune Inayah tayi daga kwancen ta zauna tana cewa"

Ciwon Kai ne kawai due to stress na aiki I think,
So Inaga dana samu nayi isashen bacci I will be ok by morning.

Duk da hakan Bari nai checking pulse naki,
Duka wannnan Zaki Saba ahankali ok?
Ki ringa samun bacci da hutu sosai.

Tea da cake Mai laushi akasa zubbi ta kawo Mata Tasha suna Dan fira sama sama kafin sukai sallama Dr farhat ta fito.

Umma yaganah ce takaita har dakin Haj umma ta gaidata.

Da mamaki sosai Dr farhat ke sake gaida Haj umma dakyau tana mamakin ba umma yaganah ceba Ashe ta Haifa AA MAJEED.

Haj umma itama sosai ta saki fuska suka gaisa da Dr farhat din Dan yanda Dr farhat ta ringa gaidata cikin Jin kunya da girmamawa sosai yasa taga mutuncin Dr farhat din sosai.

Bayan tafiyar Dr umma yaganah itama wucewa tayi dakinta ta kwanta.

Har Inayah tayi bacci cikin sanyi tana Jin damuwar rashin ganin Abbi.

Da safe haka taqi fita aiki da wuri Saida tayi breakfast da kowa.

A dining tana zuwa da Abbi tafara hada Ido Yana zaune cikin Navy blue Ralph Lauren suit dasukai masifar yimasa kyau tareda fidda hasken lafiyayyar fatarsa dake cikin hutu.

Gabaki daya Qamshinsa ya hadu Dana English breakfast din dake jere a dining ya sauya gurin.

Cikin nutsuwa da kulawa da sanyin murya tace"

Good morning Abbi.

Idanuwanta ya kalla kafin ya dauke idonsa akai anatse Yana cewa"

Morning,
Yaya jikinki?

Complain zatayi umma yaganah ta katseta da cewa"

Yaya jikin Inayah?

Naji sauki umma,
Haj umma Ina kwana?
Umma yaganah good morning.

Zaunawa tayi tana kokarin fara cin abinci Haj umma tace"

Yaya kan?
Yayi sauki ko?

Eh naji sauki alhmdllh.

Fara cin toasted bread tayi tana daukan tea tafarasha.

Itace tafara gamawa ta miqe ta Zata fice Abbinta yace tajira zai ajeta asibitin.
##MAMUH#




_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107*_49_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Bai dauki wasu mintinaba ya Gama shima ya goge bakinsa da tissue tareda miqewa yabar dining din
A natse cikin sautin Mara qarfi yace"

Saina dawo umma.

Umma yaganah ya dan kalla itama yace"

Saina dawo.

Kusan atare sukai Masa adduar adawo lfy.

Zaune Inayah take tana chatting sama sama da Neesah dake son Jin labari daga gareta tana ganin ya nufota tafara kokarin saka wayar cikin aljihun skinny jeans din dake jikinta da farar doguwar Riga Mara nauyi wadda gefenta yake yanke daga qasa har gurin qugunta.

Cinyoyinta da wandon ya lafewa ya Dan kalla Yana dauke kai kafin ya dakata daga shiga motar ya juyo cikin fada yace"

Kije kisa native wear.

Kallonsa tayi da sauri tana kallon kayan jikinta....

Me Kuma kayanta yayi?

Sake dagowa tayi ta kallesa taga harya shige motar Yana zaune
Batace komaiba ta juya Takoma cikin gida ta sauya kayanta zuwa Riga da skirt na atampa dark green da qaramin medium chantley veil ta fito riqeda qaramar Chanel handbag.

Gaban motar ta bude tashiga suka wuce.

Suna fara tafiya ahankali ta juyo ta kallesa tareda marairaice fuska ta dafa dayan hannunsa dake gefen datake cikin wata sanyayyar muryar shagwabar data Saba yimasa tace"

Abbi idan nayi lefi Dan Allah kayi hakuri bazan sakeba.

Dan juyowa yayi ahankali ya kalleta da idanuwansa dake sake Jin hawayen shagwaba,
Tace please Abbi Dan Allah bazan sakeba.

Hannunta ta qarasa dorawa kan hannunsa
Ya Dan sake kallonta

Tana ganin ya kalleta ta gangaro da hawayen data Tara a Ido tana qara marairaice Masa.

Rintse idanuwa yayi ya bude ahankali Yana dauke kai daga kallonta....

Besan yaushe Inayah ta iya wainnan abubuwanba na saurin kuka yanzu Musamman idan tanason Abu daga garesa sbd tasan kukanta shine abu na karshe dazai so a duniya.

Ahankali ya sauke boyayyan numfashi cikin kulawa da sanyin lafazinsa yace"

Meyasa kike Wasa da abinci?
Kina aikin lfy kice bakisan ciwo da dama suna shigaba ta hanyar yunwa?

Karna kumajin zaaci abinci kinbada different story daga yau.
Okay?

Gyada Masa Kai tayi tana sake riqe hannunsa cikin nata.

Zare hannun zaiyi tasake riqewa tana cewa"

Nacefa bazan sakeba Abbi,
Ahaka zamu qarasa ai ni matarkace yanzu Ab....

Wani mummunan burki yaja dasu akan hanya Saura kiris motar bayansu ta dakesu.

Kallonsa takeyi da mamaki batareda ta damu da abinda tafadaba cikin kulawa tace"

Are you okay Abbi?

Juyowa kadan yayi Yana zuba Mata manyan fararen idanuwansa dasuka sata Jin gabanta faduwa a Karo na farko sbd Abbin nata Bai taba zuba Mata idoba sosai Yana kallonta.

Koyaushe kallonsa akanta taqaitaccene duk da tsananin kaunar da son dayake Mata amatsayin ubanta.

Sunkuyar da kanta tayi ahankali Jin kallon yayi Mata nauyi da karfi ahankali tace"

Sorry Abbi.

Hannunsa dake cikin nata ya janye ahankali batareda yace komaiba ya ja motar suka wuce.

Shiru bakinta yayi sbd tasan ta zaro zancen da umma ke cewa idan batada abin fada ta ringa yin shiru Dan haka tayi shiru Amma Kuma ai Dagaske shi mijintane kodai Abbinta baya Sonta kenan da auren???

Innalillahi wainnan ilaihrrjiun" ta furta a fili tareda dagowa ta kallesa tana Jin kaman hankalinta zai tashi da wannan tunanin.

Har suka Isa asibitin Babu Wanda yasake magana
Yana parking motar Dr Abdul na shigowa harabar asibitin.

Fitowa Inayah tayi tana kallon motar Dr Abdul din kafin tadawo da kallonta kan Abbinta.

Bai lurada Hadiza ba dake cikin motar ya sauke glass din motarsa Yana amsa gaisuwar Dr Abdul daya iso cikin girmamawa kaman da can Yana gaidasa.

Ba tsammani sai ganin hadiza yayi tana qarasowa gurinsa.

Inayah ya juya ya kalla itama shi take kallo batareda ta kalli Inda Hadiza ke tahowaba.

Hadiza na isowa cikin Jin kunya da nauyinsa Mai tsanani ta Dan kallesa a sanyaye tace"

Ina kwana Abbin Inayah.

Daga ita data fada har su duka dake gurin tsit sukai cikin jujjuya zancen.

Batareda ya kalletaba cikin nutsuwa ya amsa a taqaice da cewa"

Muntashi lfy¿

A natse Inayah ta gaidata tareda kallon Abbin tace"

Abbi to waye zaizo daukana idan natashi tunda banzo da motaba?

Tada motarsa yayi ya dago ya kalleta cikin kulawarsa da kaunarsa yace"

Dr Abdul nasan zai Zama busy
May be mamansa idan Bata komai Zata iya maidaki gida,

Amma karki biya koina daga asibiti gida direct Zaki koma.

Jan motar yayi yabarsu tsaye Inayah nabin motarsa da kallo
Umma Hadiza kuwa wanin zallar farin ciki da mamakin MAJEED ne yacikata kenan majeed din ya yarda takai Inayah gida sbd kawai ta zanta da 'yarta....

Tasan bazai iya yafe Mata ko kulata lokaci dayaba Amma ko ahakan ta gode da karamcin.

Inayah rasa abin cewa tayi ta kalli umma Hadiza da farin cikinta Bai boyuba tace"

Zan dauki drop kokuma na Kira Charles idan natashi sbd Zaki wahala zuwa daukana Kuma ki kaini har gida.

No Ayshatouh please kibari nazo na daukeki da kaina
Muna buqatan sanin juna
Damace Abbinki yabani please.

Dan murmushin yaqe tayi tana cewa"

Ok Zan tashi 2 yau Inshallah.

Zanzo kafin 2 Inshallah.

Juyawa tayi ta wuce dama Dr Abdul Bai tsayaba ya wucewarsa.

Bayansu umma Hadizan tabi da kallo tana jin farin ciki Mai tsanani ganin yayanta dukasu biyun likitoci ne.

Duk da Inayah Bata Gama Zama qwararriyaba Amma zuwa gaba itama tasan Zata Zama abin alfahari gurin marasa lfy dasu iyayenta.


Data tuna mahaifiyarta zatazo daukanta saitaji wani iri Amma Kuma ita kanta tanason sanin umman Abdul din.

Qarfe daya da arbain kuwa saiga Hadiza ta iso asibitin Dan haka Inayah ta tattara ta fito suka wuce gida.

A hanya umma Hadizan keta Jan Inayah din da fira da tambayoyi akan rayuwarta Wanda komai ta tambaya sunan abbine amsar,

Anan tasake saddaqarwa MAJEED sbd yariga yayi ginuwar da Babu abinda zai girgizasa Aran Inayah,

Shine ciki da Bai din rayuwarta Dan kuwa da ace wani mijin ta aura bashiba zaiyi wuya mijinta baiyi kishinsaba duk da Yana matsayin ubanta sbd kaunar tayi karfi.

Kaman daga sama ta jeho Mata tambayar

"Ya maganar aurenki da Abbin naki?...

Shiru Inayah tayi cikin rausayar dakai tace"

Bansaniba,
Amma dai Ni aguna tanan bazan taba rabuwa da Abbi ba ko bayason auren nidai inaso yanzu....

Kallon mamaki Hadiza tayiwa Inayar tana tauna zancen,

Lallai majeed yagama shagwaba Inayah ta yanda Babu ruwanta duk maganar datazo Mata fada takeyi.

Tayaya zakiso auren idan shi baisoba ai Babu au......

Karki min Baki a auren please,
Ni inaso Kuma tunda inaso Abbi ma zaiso.

Murmushi Hadiza tayi aranta tana cewa"

Hmm wanna abbin naki Mai taurin Rai bazai taba kallonki mace ba bare matarda zai iya kwanciyar aure da ita.

Suna Isa gida a gate ta ajiyeta batareda tashiga gidanba ta juya ta komawarta.

Inayah na shigowa gida a Palo ta tadda Dr farhat tazo sunata fira da Haj umma
Umma yaganah Kuma tana kitchen yau da ita ake aikin abincin sbd kwana biyu bataiwa MAJEED abinci da kantaba.

Da mamaki Inayah ke kallon yanda har suka Saba a wuni daya daga zuwan Dr farhat din.

Gaisawa sukai tana tambayar Dr farhat dalilin zuwanta tace Haj umma tasake zuwa gaidawa da Rana sbd jiya darene Basu gaisa da kyauba.

Dakinta ta wuce tayi tube tayi wanka da sallah ta fito sanyeda doguwar chiffon gown Mara nauyi kanta daure da silk scarf.

Tunda ta fito itama kitchen ta nufa gurin umma yaganah acan Tasha cornflakes sbd bata iya cin birabisco ba shi sukai da Rana.

Da ita aka qarasa aikin tasaka hannu duk da bawani aikin ta iyaba bayan wanke plates da cups sai dafa tea shima Dan Abbinta Nasha sosai yasa ta iya Dole.

Daki Takoma ta sauya kayanta sbd batason kamshin girkin dasukeyi.

Har dare Dr farhat na gidan da ita sukai dinner tareda Abbi dashima ya danyi mamakin sabonta da ummansa daga zuwa.

Gurin cin abincinma haka dai umma yaganah da Inayah suka Zama Yan kallo har aka gama kowa ya tashi.

Da Dr farhat Zata tafi har mota ta rakata ta wuce sai yabon Haj umma takeyi itadai Inayah batace Mata komaiba akan aurenta da Kuma Dr farhat din Bata saniba hakama Haj umma Bata Sanar mataba.

Kasa bacci tayi Saida ta fadawa Neesah zuwan Dr farhat sukaita maganar kafin ta kwanta.

Washe gari Abbi Bai tashi da wuriba Dan haka ta wuce
Kuma acan ta tadda umma Hadiza Saida suka gaisa kafin ta wuce.

Yauma tana dawowa Dr farhat na gidan yau Kuma wai BP din Haj umma dinne yahau tazo dubowa.

Haka takuma wuni dasu sai dare ta wuce.

Ahankali ahankali Dr farhat ta maida gidan nasu gurin zuwa fiyeda yanda take zuwa adah,

Tayi sabo da Haj umma sosai ba laifi Dan kuwa Haj umma najin dadin yanda take zuwa duba BP dinta akai akai Wanda Kuma a Yan kwanakin tagano irin son da Dr farhat kewa MAJEED sbd hatta kulawar datakewa Inayah Mai girmace duk sbd MAJEED
Shikuma baimasan tanayiba.

Ta bangare Daya Inayah kwata kwata yanzu Bata wani gane kan Abbinta sbd dukkanin kulawansa Takoma kan Haj umma sbd kwana biyun batajin dadin BP dinta sai hawa yake Yana sauka.

Tun suna mamaki itada umma yaganah harsun koma Yan kallo Danma umma yaganah tana kokari sosai gurin dannarta da hanata magana,.

Duk tabi Takoma sukuku batada walwala koyaushe a sanyaye take Dan yanzu koyaushe idan dai Abbi na gida to Yana tareda Haj umma wadda yanzune tasan tana tareda kaunar danta tunda ya maida hankali sosai akanta.

Ganin hakan yasa Inayah ke dadewa gurin aiki sosai sbd gidan ba Dadi tunda Abbinta baida lokaci sosai.

Hadiza kuwa ganin tana samun ganin Inayah a asibiti yasa kusan duk bayan kwana daya saitaje gurin Inayah asibitin su jima suna magana
Da hakan tafara sabuwa da 'yarta tunda dama Inayah bamai hayaniya ko riqe Abu bace
Ba jimawa tayi sabo da mutum sbd sanyin halinta.

Ahankali umma Hadiza ta fahimci abinda ke damun inayah na kishin Abbinta da kowa karya fita kusanci dashi
Hakama Sam wannan auren nasu tasan idan akabi ta MAJEED kila ahaka zasu qare amatsayin uba da 'ya.

Cikin dubara ta bawa Inayah shawaran ta fadawa antynta Hafsat abinda yake faruwa.

Dayake anty Hafsat tayi tafiya jiya tadawo aikuwa da farin ciki ta karbi shawarar.

Tana dawowa gida wanka kawai tayi tayi sallar la'asar tayi zamanta adaki zubbi takawo Mata noodles data saka ta dafa Mata da sausage.

Wayarta ta fidda ta Nemo numbern anty Hafsat ta saka Mata Kira.
##MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107[11/8, 9:55 AM] Sweet sis: *_50_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Ringing biyu wayar tayi anty Hafsat ta dauka tana cewa"

Dr Inayah majeed Yar gatan Abbinta Kuma amaryar Abbinta.."" ta qarasa zancen da Yar dariya.

Sanyi jikin Inayah yayi tana Jin dadin kirarin Amma Kuma duk wannan yanason kauduwa.

A sanyaye tace"

Anty Hafsat Yaya gida?
Ina my sweet Siyama?

Lfy kalau Inayah,
Ya kike?
Yasu umma yaganah da hajiya?
Ya abbin naki Kuma?

Bata tsaya amsa gaisuwar yasu umma ba tace"

Anty Hafsat Abbina ya canja sosai zuwan Haj umma
Kuma umma yaganah ta Hana nayi magana
Ni gaba daya Abbina yafara Zama kaman na nawaba.

Umman Dr Abdul tace na sauya bangaren Mata
Ni banganeba Anty Hafsat kizo gidan kigan yanda muke yanzu duk ba Dadi,

Ga Haj umma komai nayi saitace shiriritata da shirme kawai na iya.

Yanzu itace Mai kulawa da Abbi fa,
Umma yaganah ma yanzu Takoma Yar kallo abinci kawai take Masa.

Nidai anty Hafsat wlh bazan iyaba
Ina kallo Abbina ya Dena ji Dani kaman da
Bayan umman Abdul tace kamata yayi matsayina ya ninku tunda matsayina biyu agurinsa.

Numfashi anty Hafsat ta sauke tana jinjina zantukan Dan duk da kusan a shagwabe da damuwa Inayah ke fadan zancen idan ta fahimta Haj umma batai na'am ba haryanzu da Inayah a rayuwar AA MAJEED barema ta dauki auren da mahimmanci.

Wani numfashi takuma sakewa tana ajiye ruwan data kawowa CM ta juya ta fice daga palonsu zuwa dakinta Dan bazataso yaji zancen nasuba.

Tana Shiga daki ta zauna bakin gado tana cewa"

To kodai kina Mata abinda baimata bane Inayah?

A sanyaye tace"

Wlh anty Hafsat bana Mata komai
Kuma Ni bandamu data kaunaceniba
Nidai Abbina nakeson ya koma yanda yake kada ya rage ji dani.

Inayah duk wannan abin na tabbata Koda qwayar zarra kaunarki da matsayinki a zuciyar Abbinki Bata raguba
Bama Zata taba raguwaba qaruwa zatayi sbd har Koda yaushe kece kaman strength dinsa.

Kawai dai inaga aurenku ne Bata aminta dashiba sbd ganin kaman bazaki iya kalawa da AA MAJEED dinba kinyi qanqanta....

Aikuwa wlh Ni inason auren yanzu bazaa rabani da Abbi ba,
Ko shima Ni Zan fada Masa inason aurena bazan rabu dashiba.

Da mamaki anty Hafsat tace"

Yanzu Kuma kinason auren kenan?
To kinason auren yanzu harzaki tsaya kina kallo auren na Neman fara rawan tun baigama tsayuwa ba,

Wannan rashin amintar da Haj umma tayi kome zai iya faruwa
Dan kuwa ko auren be rabuba MAJEED Kam zai iya samun matar dazata kular Mata dashi....

Wani mummunan faduwa gaban Inayah yayi ta tashi zaune ahankali dakyau tana cewa"

Sai tasashi yayi wani auren anty Hafsat?
Shima abbin sai yayi wani auren?

Wani mugun sanyi taji Yana shiga qafafunta tayi shiru tana jiran amsar anty Hafsat wadda taji rashin kamatan yin zancen da Inayah Dan haka ta Dan gyara murya cikin nutsuwa da kulawa da rarrashi tace"

Idan kika tsaya shirme nake fada Miki hakan kila zai iya faruwa,
Dan haka yanzu ki nutsu kema ki ringa kulawa da Abbin kaman matarsa sbd wannan right dinki ne dake Zaki bawa kanki.

Kasa cewa komai tayi sbd jikinta daya Gama mutuwa da wani irin tsoro dan kuwa tana fama da zuciyarta akan Haj umma idan Abbi ya auro wata Batasan ya Zata iya dauka.

Ganin ta Dena gane abinda take fada yasa Anty Hafsat yimata sallama da cewan Zata shigo gobe Inshallah.

Aje wayar tayi hannuwanta na Dan rawar data kasa gane Kota menene.

Kasa qarasa cin abincinta tayi ta miqe tareda daukan tray din ta fita zuwa kitchen.

Tana ajiye kayan data kawo kitchen kasa juyawa tayi ta tsaya agurin tana shiga tunani
Ita gabaki daya kanta ma ya toshe takasa gane komai,

Ita Abbinta kawai takeso ita kadai.

Juyawa tayi ta fito tana kokarin Isa hanyar bedroom dinta taji Qamshin Boadicea ta dakata sbd tasan Abbinta ne yadawo.

Juyowa tayi tadawo palon daidai Yana shigowa sanyeda kaftan
Navy blue best kalar dayafi amfani da ita.

Ganinsa yasa idanuwanta cikowa da hawaye tanajin wani irin nauyi a zuciyarta da abinda anty Hafsat ta fada dazu.

Kallonta ya qaraso yanayi zuciyarsa na tabuwa da kallonda take Masa idanuwanta da Hawaye Wanda yasan na kewansa ne.

Ahankali ya bude Baki zaiyi magana ta fada jikinsa ta qanqamesa tana sako hawayenta.

Shiru yayi Yana kokarin daidaita kansa sbd ba zatan datai Masa.

Qamshin Turarenta na black opium ya shiga hancinsa da kyau
Take yaji kansa ya Sara ya bude idanuwansa akanta tareda daga hannuwansa zai zareta daga jikinsa Amma ta ture hannunsa tana sake shigewa jikinsa hawayenta na sake gudu zuciyarta na bugawa da zancen anty Hafsat har lokacin.

Maqoshinsa yaji Yana Neman bushewa sbd yanayin yayi Masa nauyi Musamman Haj umma ko umma yaganah wani zai iya samunsu ahakan.

Numfashi ya sauke ahankali tareda Dan nutsuwa cikin kulawa yace"

Me kikeyi Inayah?
Lafiya?
Akwai abinda ke damunkine?
Taso naji matsalar...

Girgiza Kai tayi tana qin sakinsa tace"

Abbi Dan Allah karka rabu Dani Ni inason auren....

Wani irin duka zancenta yayiwa zuciyarsa har baisan lokacinda ya rintse Ido ahankali ba tareda budewa zuciyarsa na Neman yin sanyi

28 / 43