Author : Billyn Abdul Category : Adventure Stories
dasuba sosai a gurin Inayah yake ji da saninsu.
Ahankali ya kalleta Bayan ya kalli umma yaganah da bakin Inayah yake Bata takaici wasu lokutan.
A natse cikin yace"
Inayah wannan wata Gaskia ce da Dole zamu hakura na dauka sbd nafiki Jin dacin rashin Zama Wanda ya haifeki Amma hakan Allah ya qaddara.
Wannan kukan kidaina Babu Wanda zai tafi dake koina,
Dr Abdul Kuma idan kin daina kuka kin nutsu zan Bari kije ki dubasa.
Gangaro Mata hawaye sukai tace"
Abbi maganar auren fa?
Da gaske an daura mun aure da......
Sake buge bakinta umma yaganah tayi cikin wani sabon takaicin tace"
Waiki bakinki baya shiru idan bakisan me Zaki fada bane?
Qarya zamu Miki baa shine mijinki ba?
Baice komaiba ya miqe ya fice Yana cewa"
Wannan kukan idan Baki dainaba ko gate bazaki sake fitaba bare zuwa duba Dr Abdul.
Yana fita anty Hafsat da Zata wuce tashigo dakin tana kallonsu,
umma ta zauna gefen Inayah cikin takaici tace"
Ke bakinki baya haila ko?
Kullum Ina kwabar bakin Amma kin kasa iya kamesa ko?
Da kike maganar dakinsan yanda Zaki hada Jini dashi da kin hada ayau
Saurin uban me kikeyi idan a gauraya Jini kikeso ai zaa zo gurin saikiyi bayani da kanki,
Kullum kwabarki nakeyi bakyaji
Yanzu dai mijinki ne idan zakiyi hankali kiyi Dan kuwa bakin Nan naki kaiki zaiyi yabaro tun baayi nisaba ki gane barno gabas take.
Murmushi Anty Hafsat tayi sbd ko baa fadaba tagano kan zancen ta kalli Inayah datai tsit idonta yake hawayen fadan ummsn cikin kulawa tace,
"Yi shiru Inayah
Amma ki koya fadan magana bako wace iriba agaban Abbi yanzu sbd yanzu mijinki ne wata maganar idan kinyi kina tadowa kanki aikine tunda wuri wuri Wanda bazaki iya daukaba.
Kinga shikansa yanzu bai Gama karban yanayin ba Dan haka ki ringa Kama bakinki kisan me zakina fada.
Karma ta Kama taci gaba ita Zata bada labari Ina zaune Ina kallo
Badai gaurayan Jini kikesoba
Zaa gauraya Inda rai kuwa.
Umma Dan Allah ayi Mata hakuri da kyakkyawar manufa ta fada sbd yanayin data samu kanta da Wanda ta dauka mahaifinta ne,
Ita kanta Batasan wata manufar abinda tafada tabadaba.
Duk da hakan Inayah nada buqatan sanin abubuwa da dama na sanin Kai tunda yanzu aure yahau kanta Dan haka Hafsat ke wannan aikin ya sama saiki bada himma gurin ganar da ita.
Da farin ciki anty Hafsat tace"
Umma ai wannan aikin Dole ma kuwa
Musamman angon na Inayah shakkarsa duka muke muma dake yanne Kuma iyaye
Amma ahakan zakisha kallon hudubar da zanwa mutuniyar tawa.
Allah yasa ta dauka idan ba zuwa zatai tana fada Masa abubuwan da kike koya mataba
Wlh databarki da kunyar duniya"
Umma yaganah ta fada tana dariyar abinda zai biyo baya kuwa idan hakan ta kasance.
Dariya anty Hafsat tayi tana cewa"
Dakuwa mun Bata da ita idan tamun wannan gangancin
Yanzu mijine bakomai Zata fada masaba sabanin adah dayake matsayin uba.
Ganin Zata shiririce yasata miqewa Tai musu Saida safe ta wuce sbd anzo daukanta.
Bayan fitar anty Hafsat umma ma miqewa Tay ta wuce dakinta
INAYAH tabi kofar dasuka fice da kallo tanajin sun datse Mata maganarta da Abbi batareda sun gamaba.
Miqawa tayi ta nufi toilet tashige sbd alwalar sallar magrib da ake Kira.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Shedar biya👇
07040727902
MTN card👇
09134848107[11/2, 10:00 AM] It's Queen Meenali👑: *_35_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
*_'YAR ZURU Maman ZEE ZEE Best kayan mata_*
Shin ko kunada labarin Yar Zuru mamar ZEE ZEE Mai maida tsohuwa yarinya wadda ta shahara wurin hada kaya kamar haka ❤️kamar su
Kaza
Zabo
Zakara
Ciccibi
Zuciya
Tsimin kankana d rake
Tsimin tabaje
Zumar dabino d kwakwa
Zumar gorun tula syrup
Garuka masu kama jiki kamar su ❤️
Bita zai zai
Dan wata bakwai
Madarar mata
Bata🤐🤐🤐
Ba kishiya ba Ko mugun mutan d mugun aljani sai sun barki
Matsin kinfi budurwa
Kalolin gumba dsauransu
Address maberar jariri bayan FGC sokoto
Phone 08068526455
Instagram Yar Zuru mamar ZEE ZEE kayan mata.
Karku Bari kuwuce Baku gwada kayan Maman zee zee best kayan Mata ba..
*_35_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Da daddare tun 7:30 sukaci abincin dare Amma banda Inayah dataqi fitowa shima Kuma abbin tambaya daya yayi umma tace Inayan ba yanzu tace zataciba
Baikuma maganaba yagama cin abincinsa ya fice yabar umma da Neesah a table suna sake jinjina taurin Kai irin na Inayah sbd son zuwa ganin Abdul Zata dagawa kowa hankali.
Cikin damuwa da takaici umma yaganah tace"
Babban damuwata akan Inayah
Ga abinda yakamata ta fuskanta wato Wanda aurensa ya rataya akanta Amma Sam ita ko yarda da zancen taqiyi bare bawa zancen mahimmanci hauka kawai ta dauka munayi tunda abokan wasantane mu,
Idan Ni ta rainani ai Alhaji babbah da Abbin nata bazasuyi Mata wasaba ko shirme irin nata datake tunani.
Neesah ajiyar zuciya ta sauke tana ajiye spoon din hannunta tareda Shiga tunani tana kwatanta irin rayuwar da Aminiyarta Zata zuba a cikin gidansu Kuma gidan aurenta da Wanda Koda qazantar mafarki Bata taba mafarkin aurensaba,
To Amma yanxu da hakan ta kasance tayaya zata karba auren harsu samu cika burikan dasuka dauka zasuyi da mazajensu idan dukkaninsu sukai aure.,
Babban qarin abin shiga tunanin shine abbin da kusan baiwani San mataba,
bama kusan ba
Baisaniba kwata kwata tunda bashine ya Haifa Inayah ba to tabbas kenan
"he's virgin" tafada a bayyane tana zare Ido cikin Murna Mai tsanani sbd burin Inayah kenan auren wanda Bai taba sanin kowace maceba sai akanta,,,
""ohh my God, Abbi is still a virgin????
Tafada da Dan farin ciki tana kokarin miqewa zuwa gurin qawarta suka hada Ido da umma yaganah dake sake Baki duka tana kallonta cikeda tsoro da mamakin yanda yaran Nan suka Gama lalacewa basuda masaniya akai.
Wata irin kunya ce takama Neesah tana ganin irin kallon da umma ke Mata tasan itama ta sake layi Dan daga ita har Inayah din bakin nasu wani lokacin ba burki bare ribas.
Dan fuskewa take kokarin Yi ta hanyar komawa ta zauna Dan qarasa cin abincin da Zata Bari sbd zumudi
Umma a kasalance da mamaki tace"
Aa karki koma ki zauna jeki Inda kikai niyar zuwa Dan yanzu Kam na Gama tabbatarda kunfi qarfina yaran Nan Musamman Inayah,.
Yanzu ko kunyar Allah bakwaji zakije kuyi maganar MAJEED Bai taba sanin ma....
Kasa qarasawa tayi tana girgiza Kai cikeda kunya da takaicin fada da bakinta.
Kallon yanda Neesah tayi tsamo tsamo tayi tace"
Jeki kuyi abinda zakuyi din,
Nagamo da ita tana maganar gauraya Jini kekuma gakinan yanzu kema kina Taki maganar banzar,
Allah ya shiryaku ya sakamu kunya irin ta 'yaya Mata Dan kuwa Naga sai mun dage da adduar kunyi nisa,
Ita ansamu tun batai tsamari ba an aurar Saura ke
Kema Kuma hankali na kwantawa zanfadawa Fatima suyi Miki aure.
Kaman munafukar Neesah tabar gurin a ranta tana cewa"
Allah yasa umma yaganah kinawa momy magana ko wata kada na qara Amin auren ai inaso.
Da mamaki umma tasake bin Neesah da kallo jin ta amsa adduarta ta qarshe da cewa"
Amin" a bayyane.
Neesah Kai tsaye dakin Neesah ta Isa tana murmushi da dauke gira daya ta qarasa kan gadon da Inayah din ke kwance tana waya da Abdulsamad wadda sai alokacin suka samu Jin juna tunda wannan abun yafaru.
Tunda ya Kira wayar ta dauka take rero Masa wani irin kuka ahankali tanajin kaman ta bude Masa zuciyarta yaga matsayin sonsa aciki.
Kukanta kawai yake saurara Yana zubda hawaye shima sbd bazai iya magana ba shima,
Daga zuciyarsa har kirjinsa da kansa zafi suke Masa,
Yakasa yarda ko karban Inayah amatsayin 'yar uwa,
Bazai iyaba,
Bazai iya daukaba,
Hakama zuciyarsa bazata iya daukaba bare kwakwalwarsa data gama yamutsewa akan son Inayah tuni.
Ganin halinda suke cikine yasa jikin Neesah sanyi ta kalli Inayah dake kuka sosai har hancinta Saida yayi jajir Bayan idanuwanta da fuskar gabaki daya.
Karbe wayar Neesah tayi tareda dorawa akan kunnenta cikin tausasa murya dakuma damuwa tace"
Dr wannan kaman kuna neman butulcewa qaddarar da Allah yake jarabtarku da itane,
Inayah matar wanice yanzu daga ita har Kai kunsan me ake nufi da hakan
Badan kana matsayin muharramintaba dasai nace wanna haramun ne kuke aikatawa mezaisa bazaku danganaba ku dauki hakan wani babban rabo daga ubangiji ku gode Masa da kuka kasancema Jini daya qarshen kauna,
Shi Abbi Yana baqin ciki da takaicin rashin zamtowarta jininsa kaikuma data zamo jininka kuna Neman batawa kowa da komai Dan wannan lalata komai zaku qarasa yi.
Kashe wayar tayi ta dungurar Mata gefe tareda kallonta cikin fara Dan siqewa da yawan kukanta akan soyayyar Dr Abdul tace"
Inayah can you stop all this stupidity,
Yanzu ke kunya bakyaji ki zabi wani kinata kuka akan wani duk kin kasa tsayawama ki duba babban abinda ya rataya akanki.
Tsoki tayi tareda juyawa tabar gurin ta fada toilet Dan yin wanka sbd ita duk sun fara Bata haushi.
Rayuwa saukine da ita,
Ansan ba abune Mai saukin karbaba wannan yanayin dayazo Amma Kuma ba abinda zaka daga hankalinka bane sbd abbin dai dayafi Mata komai da kowa yasake zamowa nata dukkaninsa ba maganar kukan rabuwa dashi Amma haukan soyayyar wani na Neman rufe Mata Ido waninma 'dan uwanta da aka tabbatar Mata da Babu aure tsakaninsu.
Inayah dake hawaye komawa tayi ta kwanta kawai batareda ta iya magana ba sbd bazata iya cire soyayyar Dr Abdul arantaba lokaci dayaba,
Tafi tausayinta sosai akan kanta na wannan yanayin dasuka samu kansu sbd sanin yanda yagama zurfafa da haukacewa a Sonta.
Aurenta Kuma da Abbi Bata Gama yarda dashi bane sbd tasan abbin ma bazai taba karban aurenba sbd Babu yanda zaayi suyi rayuwa ko zaman aure Dan tamkar haramunce garesu.
Ita maganar uwarta da akeyi Kuma batajin Zata taba iya daukanta a wani matsayin Bayan na mahaifiyar Abdulsamad kawai
Sbd aduk matsayinda Abbi zai dauketa hakan itama Zata dauketa Mai kyau ko sabaninsa sbd har abada Abbinta shine komai nata Kuma maganarsa zataci gaba Dabi har qarshen rayuwarta.
Koda Neesah tafito har lokacin Inayah din takasa daina hawaye sbd yanzu kukan rashin sanin kanta takeyi.
Shin marainiyace ita kokuwa 'yar gaba da fatihan dagaske¿
Yarasa tayaya uwarta Zata jefar da ita kokuma guduwa tabarta kokuma kaita gidan marayu tun jarinta,
Tayaya ta fada hannun Abbinta,
Wace irin tsana uwarta Tai Mata da Zata jefar da ita tana jaririya
ta dauki Abdul daya girmeta Amma ita ta jefar da ita.
Ganin kukan datakeyi yayi yawa Kuma akwai tsananin damuwar abin da quncinsa a bayyane da Inayahn yasa Neesah tahowa ta zauna gefen Inayah din tareda Dan rungumota batareda tace komaiba Dan kada ta katse Mata damuwar datakeson ragewa ta hanyar kukan da tunanin.
Sun jima a hakan kafin Inayah ta janye jikinta tareda zamewa ta kwanta kan gadon tana rufe idanuwanta.
Shiryawa Neesah tayi itama cikin kayan bacci masu gajeran wando tazo ta kwanta gefen Inayah sbd tana period bare tayi sallar ishai.
Tanajin yanda jikin Inayah yayi zafi sosai alaman yauma da zazzabin atareda ita Dan haka ta miqe tadauko Mata magani tabata Tasha suka kwanta tanajin jikinta duk yakuma sanyi.
Washe gari ma Bata fito breakfast shima Abbin Bai fitoba su kadai sukayi daga umma yaganah sai Neesah.
Bayan sun Gama umma yaganah da kanta takai breakfast din abbin palonsa ta jiye ta fito.
Neesah Kuma tayi Shirin na Inayah takai Mata daki itama.
Zazzabinta ya tsananta Dan haka hankalinsu ya tashi Amma dai duk da hakan umma Bata sanarwa Abbin ba sbd kada damuwar suyi yawa Dan haka suka samu suka Dan lallabata Neesah Tai Mata allura bayan awa biyu jikin nata ya Dan saki tasamu qwarinsa tasamu tayi wanka tayi sallar azahar.
Tana idarwa ta zare kayan sallar ta miqe ahankali ta zura slippers ta fito dakin sbd tasan Abbinta baisan batada lafiyaba tunda Bai nemetaba Dan haka Kai tsaye tana fitowa Bata nufi koinaba sai hanyar palonsa jikinta ba qwari tafiyarma ahankali takeyi.
Tsit taji gidan duk da dama basuda wani manyan motsi a gidan Amma tsit taji da alama kaman umma yaganah basa gidan.
A dining yake zaune yana Shan ruwan yakasa cin abincin dake jere gabansa
idanuwansa sun sauya sosai sbd yau wani irin daci ne da quncin zuciya tareda damuwar shekaru suke tasowa suna komawa sababbi fal Kaman yanda komai yafaru alokacin bayan...,
Baitaba sanin zai Kuma fuskantar maimaicin abinda yafaru dashiba alokacinda yake cikin radadi da zafin maraicinsa abayaba.
Rintse idanuwansa yayi cikeda daci Mai tsanani dayake sake cika maqoshinsa...
Qamshin Turaren Inayah duk da Bata wani sakaba da yawaba yasashi bude idanuwansa dasukai jajir Yana kokarin basarda yanayinsa sbd kada tagani ta daga hankali da tambayarsa abinda yake damunsa.
Jin takunta ya nufi wani direction din yasashi waiwayowa ahankali ya kalli hanyar.
Riga da wandone ajikinta na masu Fadi sosai Amma basuda nauyi ko kadan sai suke saka kirjinta da bra rawa qaramar hular kayan ce kawai akanta Bata Gama rufe baqin gashintaba da akaiwa gyaran aure Amma auren baiyiyuba.
Dauke kansa yayi daga kallon gurin tareda miqewa ya nufito ganin hanyar palon dazatakl kaita gurinsa ta nufa Kuma yasan su Alhaji babbah da dangin Hadiza da Hadizan suna ciki sbd maganganun da zaayi...
Shigarta hakan gurin zai iya bayyanarda raunin tarbiyarta ga Hadiza da danginta dake gurin harma da Dr Abdul Wanda zai Mata kallon da zai iya Zama laifi ga ubangiji.
Qaramin palon daya rabasu da palon Abbin ta Isa Zata shige taji anriqo hannunta ta baya.
Batada qarfin razana Amma duk da hakan a tsorace ta waiwayo sbd riqon bana mace bane hakama tasan basuda namiji a gidan dazai shigo har nan bayan Abbinta.
Tana juyowa acikin idon Abbin idonta yafara fadawa akaron farko dataji tsoro da fargaban kallon idon Abbin...
Da sauri ta maida kallonta kansa tana bayyanarda tsoronta da damuwarta tace"
Abbi..
Kasa magana tayi sbd idanuwanta dake kokarin cikowa da hawayen da batamasan na menene ba ita dai tasan Abbinta shagwabarta akansa ta qare Dan haka yanzuma tasan bazata iya dainawa sbd kallonsa kawai nasa taji duniyarta alhmdllh sbd samun tsayayyen uba kamansa sai Mai saa irinta.
Matsowa tayi tana sake riqe hannunsa cikin hawaye tace"
Abbi Dan Allah kayi hakuri idan fushi kakeyi sbd na nace Akan zuwa asibiti dubo heart...
Tun jiya Banda lafiya sosai abbi baka..
Saketa yayi tareda zare hannunta daga riqon datai Masa
Tabisa da kallo tana jin sabon kuka na zuwar Mata sbd ganin kaman fushi yake da ita sbd ta saba riqe hannun mahaifinta ko bayan ta girma Bata daina riqe hannunsa Amma yau din ya zare batareda ya kalletaba.
Juyawa yayi Yana komawa palon ya zauna Yana cewa"
Akwai baqi aciki koma ciki anjima zansa Dr farhat tazo ta dubaki.
Kuka ya fashi dashi tareda zuwa gabansa ta durqusa tana hawaye masu gudu tace"
Abbi Dan Allah kayi hkr idan nayi laifi,
Kamun hukuncin laifin ma
Amma Dan Allah kada kabari a rabani da Heart Abbi.....
#MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Shedar biya👇
07040727902
MTN card👇
09134848107
[11/2, 10:00 AM] It's Queen Meenali👑: *_36_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Ahankali ya waiwayo ya kalleta
Ganin irin kukan datakeyi yasashi Dan sauke ajiyar zuciya Yana nazarin halinda tashiga duk tabi ta sauya sbd kuka da damuwa da tashin hankali lokaci kankani.
Dr Abdulsamad ne ya sulale daga palon batareda sanin kowaba ya shigo ciki Yana Jin idan ba ganin Inayahn yayiba bazai fahimci dukkanin abinda akeson fadaba a zaman.
Umma yaganah data lura da fitarsa ta miqe ta biyo bayansa sbd fargabar abinda shedan zai iya sawa su aikata shida Inayahn idan sun hadu,
Itakuma yanzu Kam tunda aka daura auren INAYAH da MAJEED batajin tanada abinda yakai Mata wannan auren mahimmanci sbd dai basuda yanda zasuyi aure an daura Dan haka kowa hakuri zaiyi a runguma wannan qaddarar gabaki daya.
Shigowar Dr Abdul yasa Inayah dakatawa daga rokon datakeyiwa Abbi ta zubawa Dr Abdul din idanuwanta tanajin kaunarsa na sake karyar Mata da zuciya..
Meyesa ummansa Bata tashi bayyanaba sai alokacinda zasu mallaki junansu.
Dr Abdul ma kasa riqe hawayensa yayi dukda zamtowarsa namiji agabanta.
Qarasowa yayi ya durqusa gaban Abbin shima tareda sunkuyar da Kai Yana tsiyayar hawaye cikin yanayi na damuwa Mai tsanani da quncin dake cinsa cikin zuciya yace"
Sir Dan Allah kada ka rabani da Inayah idan ta haramta aguna matsayin Mata Dan Allah kabani ita matsayin 'yar uwa tunda hakan Bai haramtaba.
Kukan tausayin Dr Abdul din yakuma zuwarwa Inayah ta kalli abbin dayaqi ko kallonsu yayi shiru cikin nasa nazarin.
Idanuwansu sun rufe suna roqonsa
Inayah roqonsa takeyi akan ya warware auren da aka daura sbd har abada bazata iya karban Abbinta amatsayin mijiba.
Irin kukan datakeyi shine yake Sosa ransa ba girman kalaman datake fadaba,
Har cikin ranta take bayyanarda quncinta na auren,
Bazata iya karban wannan aurenba,
Ta zabi yaci gaba da Zama ubanta har qarshen rayuwarta...
Umma yaganah dataga irin kuka da Inayah keyi ya daga hankalinta sosai Musamman ganin shima MAJEED din yanda idanuwansa suka sauya sosai batareda ya juyo ya kalli su Inayahn ba.
Miqewa yayi tsaye ahankali ganin tana neman shaqewa sbd kuka numfashinta Yana hardewa alamar wani attack dinne Zata Kuma samu...
Idanuwansa ya juyo ya zuba Mata Yana kallon yanda numfashinta ke kokarin rabuwa da kirjinta duk akan aurensa daya rataya akanta,
Meyesa tun farko ya aminta da auren sbd tunanin shine mafitar da Zata Hana kowa karban Inayah daga hannunsa...
A zuciyarsa kusan yafi kowa Jin kunci da shiga matsananci hali akan wannan yanayin dahar yakai ga wannan auren Wanda shima yasan yin auren kawai akai bazai taba kallon 'yarsa amatsayin maceba bare matar da....kasa qarasa tunanin yayi sbd nauyin da dacin kalaman.
Da gudu umma taqaraso tana kokarin kamo Inayah
Inayahn ta miqe da sauri tana sake rarrafawa gaban Abbi tana roqonsa numfashinta ko fita daidai bayayi.
Cikin tashin hankali umma yaganah ta sake tarota tana miqar da ita tsaye tace"
INAYAH kinada hankali kuwa?
Kinsan me kike fada?
Wane auren kikeda qwarin gwuwar cewa araba?
Cikin kuka tace"
Umma yaganah wlh bazan iyaba,
Bazan iyaba,
Rayuwar auren da akeson ayi tsakanin ma'aurata bazan iya yinta da Abbi ba wlh,
Rayuwar auren dazanyi bazan taba yinta da Abbi ba,
Umma bazan iya kwanciya gado......
Suka umma yaganah takaiwa bakin tanajin baqin ciki da takaici harma da tashin hankali sbd yanayin MAJEED duk kannewarsa Yana bayyanarda bacin Rai da griman tasirin da maganganunta keyi a ransa.
Ajiyar zuciya Mai sanyi abbin ya sake Yana kallon yanda numfashinta ke kokawa da Isa yasake sauke numfashi Yana Dan dauke idonsa daga kallon kirjinta dake harbawa sosai sbd halinda take ciki.
Fuskarta ya kalla ahankali cikeda kulawa ya kalleta tareda riqo hannunta daga jikin Umma yaganah ya zaunar kan kujera tareda kallonta Yana nazarin kalamanta dasuke bayyanarda haqiqanin Gaskiar abinda yake ranta.
Cikin nutsuwa da sautin muryarsa Mai nutsuwa da kamewa yace"
Inayah!!!!!
Kasa dagowa tayi ta kallesa sai hawayenta dake gara gangarowa daga Idanuwanta dasukai mummunan kumbura.
Kukan dakikeyi Zaki jawa kanki ciwo akan wannan unnecessary Al'amarin,
Auren ne yasaki wannan halin right?
Gyada Kai tayi wasu zafafan hawaye na Kuma ganganro Mata.
Kai tsaye