Author : Billyn Abdul Category : Adventure Stories
da Neesah sukai Masa sannu da isowa
Da qaramin sauti ya amsa Yana dan kallon Inayar kafin ya kalli anty Hafsat sbd umma yaganah na waya yace"
Doctors din sungama dubata ne?
Neesah ya nisan yanayin nata?
Firgici ne kawai data shiga ya daketa sosai Amma Inshallah lafiyanta kalau yanzu anmata allura ne sbd tayi baccinda kanta zai Dan warware ya rage Mata tashin hankalin.
Gyada Kai yayi ahankali tareda sake kallon Inayah datai wani iri cikin lokaci qanqani.
Dan gajeran numfashi ya sauke tareda juyawa yafita zuwa ganin likita Dan bayason ta kwana a asibitin gida zasu koma tunda suna tareda qwararrun likitoci a gidan.
Fitarsa da mintuna biyar sai gasu Mimi sun iso asibitin a gigice sbd tashin hankali biyu,
Na farko Jin auren MAJEED da Inayah dakuma Jin uwarsu daya ubansu daya itada Dr Abdul ga qarin halinda Inayar tashiga.
Jigum jigum sukai a dakin wasunsu na sake Dan jajanta wannan alamari da masu godewa Allah da baa Riga an daura aurenta da Dr Abdul dinba dan da abin yafi lalacewa.
Umma dai bayan taga Inayah ta tashi babu abinda take fata Dan ita kanta yanzu tanajin dacin da Inayah Zata Shiga,.
A sanin dataiwa Inayah kuka da baqin cikin dazata Shiga na zaman Abbi ba mahaifintaba zaifi Mata ciwo da radadi fiyeda auren Dan kuwa tafi buqatan ace alaqar jini suka hada Bata auratayyaba.
Har yamma lis suna asibitin Inayah Bata farkaba sai magriba.
Tana farkawa takasa kallon kowa a dakin sbd yanda duk sukai jigum jigum yabata tabbacin abinda yafaru kafin zuwanta asibitin Gaskia ne haqiqanin Gaskia Kuma Dan haka Batasan ta Ina Zata fara bayyanarda babban abinda takeji tokare da zuciyarta da maqoshinta.
Cikin kulawa da sanyin jikin yanayin da Inayah din ta nuna umma yaganah da Anty Hafsat suka fara kokarin magana saiga shigowar Abbi Wanda Yana shigowa qamshinsa ya gauraya dakin suka tsit suna jiran abinda zai faru Kuma ga Inayah din ga Abbi a amatsayin ma'aurata.
Yanayinsu yasashi basarwa tareda Dan kamewa ya kalli Inayah data dago ta zuba Masa Ido tana Neman fashewa da kuka yace"
Kina farkawa Kuma Zaki fara wani kuka agurin.
Neesah dake gefenta ya Dan kalla yace"
Ku shirya gida zaa koma da ita yanzu.
To" Neesah tace tana kallon Inayah din dake kokarin fashewa da kuka Amma takasa sbd abun datakeji ya girma qwaqwalwarta.
Juyawa yayi ya fice suka biyo bayansa.
Anty Hafsat motar CM zatabi itada Mimi da Safnah
Su Kuma su Inayah din motar Abbi zasubi Dan haka suka nufa motar Kai tsaye umma yaganah na riqe da hannun Inayah dake kokarin zubewa sbd tangadin datake na Bata cikin cikakkiyar nutsuwarta.
Kaman yanda suka Saba fitarsu da Abbin idan takama Inayah ce a gaba Dan haka yau dinma itace agaba sai umma da Neesah a baya.
Bayan sanyin Ac na motar da qamshinsa daya cika motar Yana zagayawa Babu Mai ko motsi acikinsu kaman ba kowa a motar kowa da tunanin daya shiga Banda Inayah da har lokacin qwaqwalwarta Bata fara aiki daidai ba dif take Bata ji Bata gane komai yanzu.
Suna Isa gida Dole Neesah ce ta kamota suka nufi ciki tana kokarin kaita bedroom dinta ta qwace Takoma Palo tana kokarin bin bayan Abbi cikin dimauta tana cewa"
Abbi ne kawai zaifadamun Gaskia na yarda da abinda duk ake fada,
Abbina ne kawai zan yarda da maganarsa.
Da sauri umma yaganah ta riqota tana cewa"
Ki nutsu Mana Inayah,
Me zakije kice Masa yanzu?
Bakiji anfada Miki yanzu mijinki bane,
Qarya zamu taru mu Miki ne?
Alhaji babbah zai Miki qaryane?
MAJEED din dakikeson saiya fada Miki komai Yana cikin damuwa sosai bakya gani?
Zaki sake daga Masa hankali da kukan Nan nakine idan kikace rikicewa zakiyi.
Rikitaccen Kuka ta fashe dashi Mai tsananin qunci tana cewa"
Ni bazan yardaba wlh abbin ne mahaifina,
Banason kowa a mahaifi sai Abbi,
Har umman Abdul din banaso amatsayin uwa Ni Abbi ne kawai uwa Kuma ubana...
Da sauri umma ta rufe Mata Baki jikinta na rawa sbd jikinta daya fara sanyi itama da irin kukan da Inayah din fasawa Wanda tunda take Bata taba yin irinsaba sai yau.
Rirriqeta sukai ta zube qasa tana sake tsananta kukanta zuciyarta na Mata wani irin zafi da radadi...
Idan ba abbine mahaifinta ba ai ita asaran duniya da baqin cikin duniya tana cikin cikinsa da wannan mummunan labarin da gwara ayita fasa aurenta har abada akan wannan labari...
Bazata taba yarda da maganar kowaba sai taji daga Abbinta cewa gaske bashine ya haifetaba.
Dukkanin sautin kukan datake yanajinsu Amma Bai iya zuwa Inda suke dinba Dan kusan yafita baqin ciki da wannan bankadar,
Dan yaso ya tsaya a ubanta na har abada saidai qaddara Bata bar hakan ba Dan kuwa Koda warware auren Nan akayi har abada ita zaa Kira da matarsa ta farko wadda tafara daukan igiyoyin aurensa haka itama har abada shi zaa Kira da mijinta na farko daya fara riqe martabar aurenta.
Kuka Inayah da tashin hankali sosai tashiga lokaci daya Wanda ya gigita umma yaganah da Neesah harma dasu zubbi da Salimat sun Shiga tashin hankali da damuwa sosai ganin halinda Inayah din ke ciki
Ta bangare daya shi kansa Mai gidan babu Wanda yakuma ganinsa har washe gari,
Abincin gidan ranar haka aka daukesa aka fitarwa Bosco ya rarrabawa securities din anguwar abokanansa sbd Babu Mai nutsuwar cin wani abinci.
Da zazzabi Mai zafi Inayah ta kwana Dan kaman yarinya qarama Takoma musu daqyar baccin wahala ya daukeda jikinta da mugun zazzabi.
MAMUH#
#LOVE/ROMANCE
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Shedar biya👇
07040727902
MTN card👇
09134848107*_33_*
*_Arewabook@Mamuhgee_*
Da zazzabin ta tashi da safe Dan haka sallah kawai ta iya Yi Takoma ta kwanta sbd tsananin ciwon Kai Dana kirji,
Ana Gama breakfast umma yaganah ta sallami baqinta aka kaisu aka sanya mota tareda Dan abin arziki gidan yasake daukan tsit.
Su zubbi tuni suka shirya komai a dining na breakfast kaman yanda suka Saba.
Umma dai a dakinta tayi breakfast din Neesah ma bata fito dining ba Dan a daki Tasha tea Danma sunyi sunyi Inayah ko tea din Tasha taqi.
Har lokacin bata daina tsiyayar hawayeba,
Takasa yarda da wannan qaddarar lokaci daya wai ace Abbinta shine mijinta,
Tayaya Zata fara fuskantar wannan maganar,
Har abada bazata taba iya karban Abbi amatsayin mijintaba sbd haramun nema agunta kallon Abbi a matsayin Miji ba uba ba.
Daga Neesah har umma sunyi rarrashi da nasihun harsun gaji Amma Babu sassauci a lamarin,
Gabaki daya fuskarta ta sauya sbd kuka.
Anty Hafsat ma tazo tayi nata rarrashin Amma Dole haka zasu hakura sbd dama bazai yiyu ka karbi irin wannan ba lokaci daya.
Gabaki daya wunin basuga Abbi ba sbd yafita tun safe gurin sallamar baqinsu na nesa dazasu wuce Kuma akwai wainda zaiyi meeting dasu kafin su wuce din.
Da farko mantawa yayi da auren daya rataya akansa jiyan sai daga baya bayanma ya daga waya zai Kira Inayah.
Dan rinte Ido yayi tareda maida wayar ya ajiye Yana fitarda Dan numfashi Mai zafi.
Miqewa yayi ya nufi toilet ya sakarwa kansa ruwan Yana gogawa fatarsa sabulun mountain water soap na Creed.
Sai bayan wasu Yan mintuna yafito daureda blue towel a qugu yafara shiryawa.
Cikin dark blue kaftans yafito da blue hular kube Bai wani shiga can palonsu ya fice daga gidan sbd jiransa da ake.
Sai Bayan azahar Inayah ta iya tashi da daqyar takai kanta toilet tayi wanka.
Sallah tayi tazauna tareda janyo wayarta tana sake saka kiran Heart dinta Wanda yanzu Kuma hankalinta ya karkatane akan taji yanda yake sbd tasan Yana cikin matsanancin halin shima.
Wayarsa har lokacin bata Shiga Dan haka tasake daga hankalinta da wata qarin damuwar.
Dole anty Hafsat da Neesah da umma yaganah sukai Shirin tafiya dubosa asibiti Dan dama suma duk sun damu dason sanin halinda yake ciki din tun iya basuda labarin komai akansa da mahaifiyarsa Kuma mahaifiyar Inayah.
Abbi umma yaganah takira ta sanar Masa zasu tafi dubo Abdul din Bai hanasuba yace suje.
Har Zata kashe Kai tsaye a nutse cikin kamewa yace"
Kar kuje da Inayah ta zauna gida.
Ok shikenan.
Inayah taji lokacinda Abbi yace kada aje da ita Dan haka hankalinta yaqara tashi da sauri tadauki wayarta tareda saka kiransa.
Ringing wayar tafara
Lokacin Yana tareda dasu CM da wasu school mates Dinsu da duk sunzo daurin auren sbd kowa nata kokarin hulda dasu shida CM yanzu sbd ganin sun Zama abokan manya sbd kudi.
Dan waiwayawa yayi gefensa da wayar ke ajiye ya kalli wayar a natse yaga Inayah ce me Kiran yakuma San Sarai roqonsa zatai akan binsu shikuma bazai taba barin ta hadu da Hadiza ba ayanzu Dan haka ya dauki wayar a kame yace"
Yes,Inayah.
A marairaice da alamar kuka tace"
Abbi Dan Allah zan bisu inason dubo Heart Nima,
Abbi Dan Allah kada ka hanani....
Bakida lfy Babu Inda Zaki kina wannan kukan
Kisha magani ki kwanta.
Kashe wayar yayi tareda ajiyewa Yana maida hankalinsa kan maganar dasukeyi.
Hawaye tafara tana kallon wayar
Su umma na ganin haka suka fice suna cemata saisun dawo.
Zaunawa tayi bakin gadon dakinta Tana cigaba da tsiyayar hawaye sbd tana tsananin buqatan son ganin Heart Dan taga yanayinda yake ciki.
Wurgi tayi da wayarta kan gado tana cusa fuskarta cikin tafukan hannuwanta zuciyarta na radadi.
Hannu takeson dorawa akai ta ringa zumduma ihu da birgima ko zataji sassaucin tsananin qunci da damuwar dake ranta.
Tayaya Zata iya cire soyayyar heart daga ranta bayan yayiwa zuciyarta kyakkyawar Shiga?
Tayaya zasu iya rabuwa da juna sbd kalmar uwa daya uba daya da ake dangantasu da ita?
Batada uban daya wuce abbi Kuma batajin Zata daina daukansa ahakan kokuma daina kallonsa ahakan.
Abbinta fa ake maimaita Mata kalmar mini agurinta.
Kasa riqe kukan tayi ta kwanta agurin tafara rero kuka tana sake Jin zuciyarta kaman zata kama da wuta.
***Su umma yaganah kuwa koda suka Isa asibitin da Dr Abdul yake hankalin Yan uwansa da mahaifiyarsa atashe yake sosai fiyeda tunani Dan kuwa Dr Abdul dai jiki ya rikice.
A jiyan da aka kawosa asibiti daqyar aka samu ya farfado ya kalli mahaifiyarsa da hankalinta ya rarrabu cikin tashin hankali masu girma sbd labarin auren MAJEED da INAYAH ya gigitata sosai,
Zancen ya daketa har Batasan lokacinda itama ta zube qasaba jininta na Neman hawa.
Tabbas AA MAJEED ya nuna Mata shi namijin duniya ne,
Ya Sha gabanta ta hanyar aure Inayah sbd baida niyar bata 'yarta,
Tabbas Babu shari'a yanzu Kam da Zata karbar Mata Inayah daga hannunsa Amma Kuma idan har Inayah Bata son wannan auren Koda abinda ta mallaka zai qare duniya kowa ya juya Mata baya saita tsaya Sharia ta raba auren anbata 'yarta.
Su Haj balaraba dasu Alhaji buhari saidai su Alhaji kabiru sukai musu bayanin cikin daya bayyana jikin Hadiza bayan shekaru Wanda yayi sanadin dasuka koreta daga gida
Saidai yanda komai yafaru Bayan barinta gidan shine Basu saniba saisunji daga gareta dashi AA MAJEED din Dan yanzu sune kadai zasu qarasa warwarewa kowa wannan qullin da tunanin dasuka shiga.
Haj balaraba kuka ta ringa rerawa tana yiwa salisu addua suna qara godewa Allah da baa daura wannan aureba da basusan iya Ina tashin hankalin zai kaisuba.
Hajiyarsu suka kira suka Dan sanar da ita komai a taqaice to dayake tasan da maganar cikin da haihuwar bayan barin Hadiza gida daga bakin jama'a Amma tayi shiru ta lafe sbd tunanin ko cikin banzane Hadizan tasamo daga Lagos sbd kada a dangantasu da cikin Tai shiru taqi Kuma barin 'yayanta ko daya yasani dan kada suce zasu karba tunda ba tabbas hakama Hadiza ta sameta takanas da jaririyar Amma shedan yaqi Bari ta amsa.
Tsufa ya kamata sosai yanzu Amma itama haka ta ringa kukan danasani da farin cikin da aka samu Ayshatouh take zancen yafara fita a dangi saidai halinda Abdul ke ciki yafi daga hankalinsu akan murnar bayyanar wadda basuma San da itaba a zuriar.
Dr Abdul mummunan shock din daya shiga ya daki zuciyarsa zuwa qwaqwalwarsa sosai Dan haka ya jima Bai farfado ba Kuma ya a farfadowa ummansa yafara zubawa indanuwansa dasukai mummunan ja yana kallonta cikin karaya da mutuwar dukkanin jiki yace"
Umma since Inayah 'yarki ce itama kece kika haife shiyasa bazan auretaba Abbi ya aureta
Ni nakasa gane komai
So kawai naji daga bakinki idan kece mahaifiyar Inayah tayaya AA MAJEED zai Zama ubanta?
Umma Dan Allah kicemun ba kece kika haifetaba,
Kicemun bakida alaqar komai da ita sai wadda zamu qulla yanzu ta auratayya,
Umma Dan allah kice bakece uwar Inayah ba bakida alaqan komai da ita...umma bazan iya rayuwa Babu Inayah ba kinsani akanta zan iya rasa hankalina da nutsuwata,
INAYAH ce farin cikina,rayuwata da nutsuwata.....umma kice wani abun Dan Allah Amma ki janye maganar kece mahaifiyar INAYAH.
Kakkarwa jikinsa keyi idanuwansa na sake fitowa da tashin hankali.
Saikowa yayi gadon Yana Neman faduwa sbd jiri sukai saurin riqesa umman cikin kuka ta riqosa tana kallon yanda yake kokarin haukace musu tace"
Abdul hakuri zakayi da wannan kaddarar ka runguma sbd bazan iya goge alaqar jinin dake tsakaninka da Ayshatouh Inayah ba,
Kai Dan uwantane na Jini,
Nice na haifeta kaman yanda na haifeka,
Uwar daya ubanku daya Babu Mai iya goge wannan sbd rubutacciyar kaddara ce,
Abdulsamad ma dauki danganar rasa Inayah sbd har abada Babu aure tsakaninku
bazaka taba aurentaba Koda ku biyu zaku rage a duniya.
Dan Allah Abdul ka karbi wannan kaddarar da hannu babbiyu sbd zuciyata bazata iya daukan wannan tashin hankalin dakake saka kanka acikiba Dan Allah Abdul.
##MAMUH#
##KUYI HAKURI AMIN UZURI NASAN CHAPTER DIN IS TOO SHORT.🙏
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Shedar biya👇
07040727902
MTN card👇
09134848107*_34_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Umma Hadiza hankalinta yagama rabuwa daban daban,
Tana buqatan fuskantar MAJEED akan abinda yayi na auren Inayah badan komaiba sai Dan nuna Mata iko akan Ayshatouh..
Ta Bangare Daya tasan Inayah ma na can cikin matsanancin halin itama,
Babbar damuwar Kuma ganin Abdulsamad na Neman zauce musu sbd yaqi sauraren kowa bayan zantukan tashin hankali da qin yarda da uwarsa daya da Inayah kaman yanda itama Inayah batama yarda da tanada wata uwarba Dan ko acikin tarin damuwarta umma Hadizan Bata shigob ita tashin hankalinta Abbi daya zamana ba mahaifinta ba ko auren daurawa kawai akayi batajinsa ajikinta kwata kwata.
Zuwansu umma yaganah yasa hankalinsu Haj balaraba tashi sbd mummunan halinda Abdul yakuma shiga Dan kuka ya ringa yiwa su umman da Anty Hafsat Yana maimaita sunan Inayah cikin karyewar zuciya.
Umma yaganah dayake tanada saurin kuka take itama tafara hawayen tausayin Abdul tana cewa"
Abdulsamad sai hakuri
Jarabawar ubangiji ce duk zaa cinye idan anyi hakuri da tawakkali
Inayah tariga ta Zama ta waninka dole dangana zaa dauka abarwa Allah...
Kalaman umma yaganah suka qara Karya zuciyarsa yaci gaba da zubda hawaye Yana sunkuyar dakai zuciyarsa na Masa wani irin ciwo.
Anty Hafsat ma jikinta mugun sanyi yayi da tausayin Abdulsamad Mai tsanani Dan kuwa Basu dauka abin yayi tsanani hakanba.,
Abdulsamad din dasuka sani Dan gayu da kwalisa shine ya garare cikin kwana daya sbd masifar ciwon rashin Inayah.
Neesah kuwa itama jitayi tausayinsa da Inayah harma Dana Abbi yasa hawaye ciko idonta sbd kowannensu yana cikin matsanancin halin da Babu mafita sai dauka da dungumar abinda ya samesa.
Irin naci da daga hankalinda Abdulsamad yayi nason zuwa ganin Inayah yasa umma yaganah miqewa su tafi sbd ko hauka bazata sakata tafiyada abdul dinba ko basa damar zuwa ganin Inayah ayanzu sbd bayan haqqin mariqi da MAJEED yake dashi akan Inayah yanzu shine Mai gabaki dayanta Dan haka bazatai wannan wuce gurinba ko gangancin zuwa dashi Dan haka suka miqe suka fito jiki a sanyaye Koda,
Inayah ma Babu Wanda yayi musu maganarta sbd kowannensu baimasan me zaiceba akanta Dan haka sukai shiru kafin suga sun fara samun daidaituwar Abdul tukuna ayi zaman wannan maganar dake buqatan iyaye da manya aciki sbd tsanar da MAJEED yayiwa Hadiza Saida manya a zancen zai yiyu.
Abbin ne yarigasu isowa gida Kuma yasan Babu kowa a gidan sai Inayah Dan haka daya dawo direct ta palonsu ya biyo tareda nufar bedroom dinta.
Yana isowa zubbi na fitowa daga dakin daukeda tray din abinci da Inayah din bataci ba.
Zubbi na ganinsa tayi saurin Dan yi gefe Tana cewa"
Welcome Sir.
Tray din hannunta ya kalla ganin Babu abinda aka taba daga abincin.
Dan rintse Ido yayi ya bude tareda cewa a natse,
"Kiyi warming abincin ki dawo Mata dashi.
Ok Sir" tafada tareda barin gurin.
Dayake kofar abude take Koda suke maganar Dan haka Inayah taji Qamshin turensa tasan abbi na kusa sai gashi taji muryarsa a hankali.
Da sallama Mara sauti sosai yashigo dakin Yana kallon yanda take zaune kan gado daga fuskarta har idanuwanta sunyi mugun kumbura gabaki dayama kusan kamanninta sun sauya sbd kuka da tsananin tashin hankali.
Sofa dake dakin ya nufa ya zauna ahankali tareda Dan takaita kallonsa akanta sbd ganin fuskarta ahakan damunsa zaiyi sbd baitaba barinta tun yarintaba tashiga damuwa irin haka.
Yana zaunawa ta miqe tsaye ta nufosa.
Wani kallo yayiwa qafafuwanta dasukai haske sosai ga sai zanen maroon lallen da akai Mata na aure yafito da Babu safa ko bedroom feetwear a qafafun tana kallon ta dakata tareda komawa baya ta dauki feetwear dake gefen gadon masu taushi na bargo ta saka kafin ta nufosa Dan yawo ba feetwear ko safa wani abune da abbinta koyar da ita tun qanqanuwarta
Duk tsafta da kyan gidansu basa da yanda tsarin gidansu yake na komai fes Bata tafiya ba takarmin ko safa a qafarta sbd wasu qananun qwayoyin cuta ta qafa suke saurin shigar mutum.
Gefensa ta qaraso jiki a sanyaye ta zauna tana kokarin yimasa wani kukan Dan dama tun jiya takeson ganinsa tayi Masa kukan dake cinta Amma taqi barin kowa ya gansa ya shigewarsa.
Fara hawaye tayi tana kallonsa tace"
Abbi Dan Allah kada kacemun bakaine mahaifinaba,
Ni Kai nasani Kuma Kai zanci gaba da sani a wannan matsayin
Bazan taba karban kowaba amatsayin uwa ko uba
Dan Allah Abbi kabarni da matsayina na 'yarka ta Jini nafison.
Umma yaganah ce ta bude kofar dakin tashigo Kai tsaye sbd dawowarsu kenan.
INAYAH Bata tsaya da abinda take fadaba tacigaba da cewa"
Abbi Dan Allah kada karka bari a sauya mini wani sunan bayan Wanda ka sanyamin,
Ni banason kowa amatsayin jinina sai Kai,
Abbi Ni Kai kadai ne jinina,
Danasan yanda zanyi na hada Jinina da naka ya gauraya daya da naka Abbi wlh danayi ayau dinnan.......
Umma yaganah dake kokarin juyawa tabasu guri Batasan lokacinda ta tsaya cak ba tareda dawowa da wuri tana buge bakin Inayah din cikin kunyar zancenta.
Shi kansa MAJEED din Dan muskutawa yayi tareda fuskewa sbd Inayah dai idan zatai zance ba ruwanta yanko abarta kawai takeyi.
Lokuta da dama Dan umma yaganah na kwabarta ne Amma zantukan datake yankowa gaban Abbin mamaki suke basa matuqa Dan shi wasu abubuwan na halayen Mata dabai taba saniba sbd Bai mu'amalantu