Author : Billyn Abdul Category : Adventure Stories
tana cewa"
Heart yunwa fa nakeji sosai yau banwani ci abinci ba
Zaa ramar maka Ni da yunwar biki.
Cikin kulawa sa so Mai tsanani ya karyar da murya yana cewa"
Ni zasu illata gskia bazan dauka ba,
Kyakkyawar amaryar tawa ce zaa Bari da yunwa
Gskia bazan yardaba
Laifin anty Hafsat ne data hanamu haduwa yanda muka saba kewanki is driving me crazy
Gobe da safe zanzo na ganki kafin su Umma su iso sbd itama tana zuwa Zata qarawa anty Hafsat qwarin gwuwar hanamu ganin juna sai ranar Daurin auren.
Murmushi tasake Mai kyau tana cewa"
Dan Allah kazo goben da wuri Nima nayi kewanka fa sosai.
Zama tayi a dining daidai lokacinda Abbi ke isowa dining room din a kasalance ta ajiye wayar sbd bataso Gama waya da Heart dinta ba Amma Kuma girman Abbinta na daban ne akan komai.
Kallon abbin tayi Yana sanye da Fararen hoodie graffiti print sweatset.
Sanyin qamshinsa ne yake neman danne na Lafiyayyan abincin dake jere kan dining din yayi fresh Kamar ba baban amaryar ba Batasan lokacinda ta sake qaramar dariyaba tana cewa"
Abbi barka da fitowa.
Da Dan silent murmushi ya kalleta yana amsawa da cewa"
Barka Amaryan Dr Abdulsamad.
Dariya tasake tana kallonsa tace"
Abbi Naga kamanma ka matsu natafi nabar gida,
Kullum saikace mun amaryar,
Nidai kunya nakeji Gaskia.
Wani qayataccen murmushi ya sake daidai lokacinda Neesah da umma yaganah suka iso dining din cin abinci yace"
Inayah kinsan kunya dama?
Inace you don't know the name kunya,
Kin manta a gabana kike zuwa kina kukan soyayya da Kiran sunan zayyan ne sunan koma fahat ne I can't recall
And now kinata tsalle da murnan zakiyi aure shine kike fadamun kunya
Rashin kunya plus lie ko??
Dariya umma da Neesah sukai umma na saka musu Baki da cewa"
Inayah kam ai indai anan cikin gidane Babu Wanda take kunya saidai mutane waje take kunya.
Kai umma yaganah please karki sake batan suna gurin Abbi Kinga zaifi kowa kewata fa idan natafi ko Abbi?
Abincin data Gama zuba Masa yafara ci yana Dan gyada Mata Kai ahankali.
Bayan sun Gama cin abincin bin Abbinta tayi palonsa suka cigaba da maganganunsu na tsakanin uba da 'ya sai kusan after 9 tafito ta nufi daki ta kwanta bayan tasake goge fuskarta da face cleanser.
Washe gari shine zaai Mata lalle Kuma tasan heart dinta yace zaizo Dan haka da wuri ta tashi tayi wanka ta shirya cikin Riga da skirt na maroon super exclusive wax da qaramin Marron veil ta fito a sace sbd yaca Mata ya iso Yana palon Abbi.
Tana shiga palon Abbin Yana zaune tareda Abbi suna magana cikin nutsuwa.
Bude kofar tareda sallamarta a sirance tasaka su waiwayowa kallon kofar atare take zuciyar Abdul yakusa bugawa.
Ya salam ya furta a fili batareda yasan ya furta hakan agaban Abbin ba.
Qamshintane ya doshi hanyar mamaye palon gabaki daya sbd wasu irin qamshine kala kala na designer turarukanta masu tsada da turarukan khumrahs da akai Mata masu tsananin sanyin qamshi da shiga zuciya.
Kallo daya Abbi yayi Mata yaga yanda daga ita har Abdul din suke kallon juna yaji mamakin gaske yana kamasa ta yanda Inayah duk ta lalace har haka baida sani.
Ahankali ya dauke Kai daga kallonsu tareda gyara murya yana Kiran sunan Inayah din a natse.
Cikin nutsuwa da girmamawa tace"
Yes,
Good morning Abbi.
Qarasowa tayi tareda dauke kallonta daga kan heart din tana Zama kusada Abbinta tasake gaidasa.
Amsawa yayi tareda Dan kallonta yace"
Hafsat tasan kinzo Nan?
Murmushi tayi tana girgiza Kai da cewa"
Abbi Bata saniba banaso ta sani please.
Da mamaki ya Dan kalleta sbd yasan hakan bai kamataba Musamman yanzu irin yanda yaga suna maitar kallon juna bayason ko kadan shedan ya Shiga zukatansu Koda rungumace suyi kafin aurensu tunda daga yau ne sai gobe jibi zaa daura auren Dan haka ya Dan kame fuska a kame yace"
Ok ku gaisa ki koma ciki zanyi magana dashi.
Bata fuska take Neman yi ta marairaicewa abbin Amma ganin ba wannan damar yasata kallon Abdul daya Gama mutuwar zaune gurin satar kallonta ta gaishesa a gutsure.
Amsawa yayi batareda ya kalleta sosaiba tunda Abbi na gurin
Badan sun soba su duka haka ta juya Takoma Inda ta fito.
Shima Bai wani gane sauran zantukansa da Abbin ba sama sama ya gane yayi Masa sallama ya wuce.
Jiki mace akai Mata zanen kunshin sbd rashin ganawa dakyau da heart dinta.
Sai kusan yamma daya kirata yasamu yasaka zuciyarta da ranta ya sake suka Dan zanta a wayar kafin ta aje tashiga wanka sbd anmata dilkan yamma again.
Washe gari Koda ta tashi da murnar sauran kwana daya ta tashi hakama da damuwar rabuwa da Abbinta Dan haka ta ringa samun sauyin yanayi aranar,
Tayi farin ciki tashiga damuwa ahaka dai yamma tayi duk saitaji tashiga damuwar tunda gobene Zata bar gidan gashi har yamma tayi Babu abinda ya rage a wunin yawuce sai kawai ta fashe musu da kuka.
Bata taba tunanin halinda Zata shigana ranarda Zata rabu da mahaifinta sai yau Musamman idan ta tuna da Heart dinta Dan Adamawa ne can zasu tafi da ita bazata sake Zama gurin Abbinta ba
Tsorone Mai girma ke Neman cika zuciyarta sbd duk Inda Zata tafi jinta safe cikin nutsuwa da kwanciyar hankali agurin mahaifinta.
Tun su anty Hafsat na Mata dariya hardai suka fuskanci da gaske takeyi hankalinta ya tashi matuqa a tsorace take.
Umma yaganah ma jikinta duk yayi sanyi Musamman itama datai wata irin sabo da shaquwa da Inayah din tun jarinta.
Heart dinta hankalinsa ya tashi da kukan nata sbd kowa yayi yayi taqiyin shiru shiyasa anty Hafsat tafada Masa kozai iya zuwa ya lallashi Inayah din
Itama umma yaganah takira Abbi tafada Masa Inayah fa tana nan tana zabga kukan bazata iya zuwa Inda Batasan kowaba ta rabu da mahaifinta.
Cewa yayi idan yagama magana da baqinsa dasuka iso Lagos domin daurin auren goben zai iso gidan.
Dr Abdulsamad Yana tareda mahaifiyarsa da qannan babansa biyu Mata sai 'yayan yayyun mahaifiyar tasa biyu suma Koda anty Hafsat me Masa wannan bayanin.
Kallon umman yayi yace"
Umma Bari naje gidan Inayah ce tanata kuka wai bazata iya zuwa garinda batasan kowaba.
Murmushi umman tayi cikeda mamakin shirme irin na Inayah
Gata ta girma dai Amma gata yasa yarinyar kasa nuna ta girma.
Wayarta dake gefenta ta dauka tana cewa"
Kaga bara natashi muje tare sbd dama yakamata da muka iso munje gidan an gaisa kafin goben ranar biki muje gidan,
Kaga dama abinda yasa nazo da kaina kenan sbd Inayah din tasake tasan muna kaunarta sosai
Nice zan karbeta da hannuna Inshallah cikin Amana bazamu Bari tayi kukan baro gidaba.
Gaba yayi Yana cewa"
Okay umma saikin fito to.
Bayan fitarsa tsadadden mayafinta dake ajiye ta dauka tareda LV handbag dinta ta nufi kofa tana cewa"
Nafisat zo muje Naga kece a shirye da alama su Asmau akwai sauran gajiya atare dasu kaman wainda sukai tafiyar mota bayan jirgi kuka biyo.
Ficewa suke kokarin Yi yayar mahaifin Dr Abdul dake sallah tana idarwa cikin Dan daga murya tace"
HADIZAH.
cak umman ta tsaya tareda waiwayo tace"
Na'am.
###MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Shedar biya👇
07040727902
MTN card👇
09134848107[10/26, 8:44 PM] Sweet sis: *_26_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Ku jirani a motar Bara na sauya Kaya muje Nima zan gaisa da iyayen na Inayah tunda dai kaman yanda kikace din yakamata muje a gaisa basai gobe bayan daurin aurenba muje.
Ok Tom muna jiranki a motar.
Juyawa tayi ta fice daga babban dakin ta ratsa palon zuwa babban palon gidan na mijinta Wanda Sam basa Zama anan tunda aikinsa na soja ya maidasa Abuja ita saita koma Adamawa sbd uwar gidantace a Abuja ita Kuma a Lagos to ana Masa transfer zuwa Abuja tabar Lagos Takoma babban gidansa dake adamawa.
Tana Isa motar Haj balaraba na isowa Dan haka sai kawai suka shiga suka wuce zuwa gidansu Inayah din.
Tafiyar mintuna sukayi suka iso lafiyayyar anguwar ta masu abun duniya.
Kai tsaye security ya budewa Abdulsamad din gate Yana daga murya da cewa"
Welcome Sir.
Yauwa thank you Bosco.
Parking yayi tareda kashe motar suka firfito su umman na sake yaba arzikinsu Inayah din Dan kuwa gidan irin tsarin ginin turai ne komai ma kusan yanda Inayah takeso akayisa.
Kai tsaye hanyar kofar palon cikin gida ya nufa dasu
Sbd su din Bai kamata yabi ta hanyar palon Abbi dasuba.
Suna Isa kofa Safnah na fitowa da waya a hannunta tanayi ganinsu yasata katse wayar Dan nuna girmamawa gasu umman Abdul din dasuke manyan Mata sosai.
Cikin sakewar fuska da girmamawa tafara musu sannu da zuwa tana gaidasu.
Juyawa tayi tai musu jagora zuwa can qurya palonda kowa yake Anata fama da Inayah din.
Tsokar Abdulsamad tayi da cewa"
Yanzu sbd heart din taka ka tado su umma da magribar fari Dan azo a rarrasheta.
Dariya yayi yana cewa"
Safnah harda ku kuka sake rudar mun da ita gskia
Amma haka kawai baby bazata fara kukan Nan ba.
Shi a palo ya zauna Yana amsa waya sukuma su umma palon ciki tayi dasu.
Su umma yaganah dasu Mimi na ganinsu cikeda farin ciki da mutuntawa suka tarbesu suna musu sannu da zuwa a waye.
Mahaifiyar Abdulsamad hadiza babbar mace ce Mai tattare da Kamala da mutunci sosai Kuma a bayyane ta nuna kaunarta da kulawarta ga Inayah.
Drinks da snacks zubbi da Salimat suketa aikin kawo musu Anata sake musu sannu da zuwa.
Cikin Jin Dadi da farin cikin yanda aka karbesu hannu bibbiyu da mutuntawa suketa amsawa suna sake yaba gatan da Inayah take dashi Dan duk Wanda is kalla yanayinsa a gidan zaka tabbatarda yanda yake kaunarta tunda kusan duk albarkacinta kowa keci acikinsu adai cikin gidan da rayuwar AA MAJEED.
Da 'yar Raha umma yaganah tace"
Kuna fama da gajiyar tafiya Rigimar Inayah ta fiddoku,
Shima Abdul din dabai daukokuba ai yabari Kun huta shegantaka ne kawai irin na Inayah Zata fara kukan barin gida tun yanzu
Ai tabari har zuwa goben idan andaura aure.
Yar dariya Haj balaraba tayi tana cewa"
Ai Dole zatayi kuka tun yanzu sbd auren nesa na gida Daman sai kaji kaman shikenan katafi.
Umma Hadiza kuwa Inayah data fito daga bedroom sanye cikin Riga da skirt na soft embroidery Swiss Mai kyau da tsada navy blue ta zuba Mata Ido gabaki daya tana kallonta.
Duk hotunan Inayah da vidcall dasuke ganinta idan Abdulsamad na gida basu bayyanar Mata da kamannin Inayah ba kaman yanzu datake ganinta a gabanta.
Da farko zuciyarta harbawa tayi da kyawun fuska Dana jikin Inayah hartana Jin Anya Abdulsamad bazai bartaba akan matarsa Inayah bayan auren
To Amma Kuma zuciyarta tarigada ta kamu da kaunar Inayah tun kafin auren sbd son da Abdulsamad ke Mata to yanzuma data ganta saitaji kaunarta Mai nutsuwa da tsafta takuma shigarta.
A natse Inayah ta qaraso Inda suke fuskarta duk yayi ja sbd har lokacin hawaye takeyi sosai Musamman ganinsu umma Hadiza sai taji kaman sunzo tafiya da itane gabaki daya zatabar gida.
Cikin farin ciki da kulawa tareda murmushi a fuska umma Hadiza ta kamo hannunta ta zaunar da ita a gefenta tana cewa"
Zo ki zauna 'yata Inayah kinji,
Ki daina kuka sbd inshallah bazamu taba Bari kiyi kewansu umma da Abbinki ba sosai Dan zamuyita tattalinki muma kaman yanda suke Inshallah.
Ba kunya Inayah ta dago ta kalli umma Hadiza alamar da gaske kike fada.
Da sauri umma da Anty Hafsat suka dungure Mata kan suna cewa"
Inayah wai bazakiyi hankaliba ko??
Su umma Hadiza da haj balaraba kuwa dariya suka sake atare harma dasu Neesah
Haj balaraba na cewa"
Eh Inayah Inshallah bazakiyi kukan shigowa zuriar muba da yardar Allah,
Barema wannan ja'irin Abdulsamad duk Wanda ya damar Masa Mata Inayah ai nasan zaburewa zaiyi da rashin arziki kala kala
Shima Kinga muna kaunarsa sosai Dan haka bazamu Bari matarsa ta Shiga damuwar dashima zai shigaba.
Washe Baki su umma yaganah suka hau Yi suna Jin dadin sirikan da Inayah tasamu masu kaunarta.
Murya a sanyaye Inayah ta bude Baki cikin girmamawa ta gaidasu tana Dan sake goge hawayenta.
Inayah daina kukan kinji Inshallah Baki rabu da gida ba duk lokacinda kikaso gida zakizo ki gansu
Kuma kin manta Anan Abdulsamad din yake aiki ne?
Bawani dadewa zakuyi a Adamawanba zaku dawo Lagos mune ma zamu ringa zuwa dubaku basaikunyi wahalar zuwanba.
Ahankali Inayah ta saki Dan siririn murmushi tana kallon su Anty Hafsat dake Mata dariya.
Da Raha Haj balaraba tasake cewa"
Inayah akwai sauran kuruciya kam,
Gaki 'yar fari shiyasa aketa shagwaba ko?
Nikam ma menene Ma'anar sunan Inayah Dan naji sunan shima na Yan shagwaba.
Dariya sukai saidai anty Hafsat ce tace"
Ma'anar sunan Inayah shine kyauta daga Allah,
Kaman ace kyautar datazo wadda bayan Allah Babu Mai iya baka ita.
Dukkaninsu murmushi sukai ana cigaba da Dan sake maganganu cikin Raha da mutuntawa har lokacin sallah yafara wucewa Dole suka tashi Dan gabatar da sallah.
A dakin umma yaganah aka Kai su umma Hadizan suyi sallah sai alokacin Inayah tasamu ta Isa Palo gurin Heart dinta.
Yana ganinta ya taso a natse tareda miqa hannunsa ahankali ya kamo nata hannun suka Isa kujera suka zauna Yana kallon fuskarta datai ja cikin damuwa da kulawa sosai yace"
Baby sosai kikai kuka haka?
Oh my God,why baby?
Wasu hawayen takuma gangaro Masa tana sake narkar Masa da fuska tace"
Heart Dan Allah karmu dade Adamawa da yawa mudawo Lagos da wuri.
Numfashi ya sauke Yana goge mata hawayenta da tissue din dake palon cikin kulawa kaman ya janyota ya rungumo yace"
Baby ki daina hawaye da damuwa please,
Idan Dan zakibar gidane na miki alqawarin bazamu dauki lokaciba zamu dawo okay?
Gyada Masa Kai tayi tana tsayar da hawayenta.
Lallabata yayi takoma ciki Dan yin sallah shima ya fice zuwa qaramin masallacin dake gefen gidan yayo sallah Yana dawowa yace su umma su fito ya maidasu gida akwai baqinsa dasuka iso daga Adamawa yau Dan daurin aure zai samesu a hotels din dasuka sassauka su gaisa friends dinsane sosai.
Yana harabar gidan jikin motarsa Yana jiransu saiga motar Abbi tashigo yadawo shima.
Su umma Hadizan ne suka fito tareda su Anty Hafsat da Mimi dasuka rakosu harma da Inayah dake maqale gefen Haj balaraba tana sake rarrashinta cikin kauna da kulawa.
Cikin maroon luxury motar Bentley bentayga yadawo gidan Dan haka suna ganin motar duk suka tsaya Dan gaidashi dakuma su umma Hadizan ma su gaisa tunda yariga yadawo.
Cikin wani Sky blue tsadaddiyar soft Italian cashmere a jikinsa ya fito
Fuskarsa fresh a kamile.
Kyakkyawar fuskarsa ya juyo da ita ya kalli Inda suke gabaki dayansu sun tsaya suna jiran fitowarsa daga motar a girmame.
Hasken fatarsa da dogon hancin zuwa haiba da kwarjini Mai yawa da Allah yayi Masa yasa dukkaninsu Babu Mai iya Masa kallon quru quru saidai a gaisa kana Dan sauke Kai a mutunce.
Inayah ce tabar gefen Haj balaraba ta nufesa tana kallonsa cikin kulawa tace"
Abbi barka da dawowa.
Wani nutsatsen murmushi ya sakar Mata Yana amsawa Kai tsaye da kallon fuskarta datai ja sbd kuka a natse cikin lafazinsa masu nutsuwa yace"
Duk kukan da kikaita yine wannan?
Bata fuska tayi zatai magana anty have ta Dan qaraso kadan tana Masa sannu da zuwa cikin girmamawa tace"
Sirikan Inayah dinne wato mahaifiyar Abdulsamad sukazo tareda yayar mahaifinsa zasu tafi ko zaku gaisa.
Ok ba damuwa"
Ya furta tareda qarasa tahowa cikin nutsuwa Inayah din na gefensa kaman Zata maqale Masa.
Tunda suka doso su kowa ya sake Dan kame kansa suna rage kallonsu akansa sbd kam badai cika Ido da zallar haiba ba.
Umma Hadiza datai Masa kallo daya taga fuskar kaman wadda ta sani Dan haka ita bata dauke idonta akansaba taci gaba da bude idanuwanta dakyau akansa.
Dan juyawa kanta yayi kadan sbd toshewar Dan qwaqwalwanta ke Neman Yi gabaki daya da kamannin nasa.
Baya wani kallon Mata Musamman su din dayaga ba laifi dattijai ne Dan haka a mutunce ya gaisa dasu ya kalli Abdulsamad dake nuna umma Hadiza yace"
Sir wannan itace mahaifiyar tawa.
Dan sake fuska Abbin yayi kadan tareda kallon umma Hadizan a natse yace"
Barka da zuwa Haj,
Ya hanya?
Allah ya hutarda gajiya......
Tsit yayi bayan yasamu yakai qarshen gaisuwar a Dan rarrabe.
Kallon fuskarta yakeyi dakyau cikin Dan basarwa sbd danne duk wani Abu dayake yunquro Masa cikin Rai.
Mummunan bugawa Mai qarfi zuciyarsa tayi wadda bayajin yataba samun wannan bugawar.
Sam Bai nuna halinda yashigaba saima juyawa da yayi ya wuce ciki Yana musu a sauka lafiya.
Mutuwar tsayece da daukewar hankali na daqiqu agurin ya Kama Hadiza Saida Haj balaraba ta Dan girgizata tana ambatar sunanta.
Kasa motsi tayi sai kawai sukaga tana neman zubewa sbd duhun dayake Neman rufe idonta da qyar ta iya bude Baki murya a hargitse ta furta"
BP Dina ya hau sosai please ku kaini gida Nasha magani bana gani sosai.
Hankali tashe Haj balaraba da Abdulsamad din suka kamata ta shiga mota dukkanin jikinta na rawa a rude sukabar gidan.
Da tausayin umma Hadizan su Inayah suka koma cikin gida Bata tsaya komaiba ta nufi sashen mahaifinta.
Zaune yake numfashinsa na Dan fita da sauri
Qananun zufa na tsatsafo Masa a goshi da alama Yana Jan numfashi ne dake Neman qwace Masa da qyar.
Da gudu tayo kansa tana Kiran sunansa hankali tashe da firgici Dan Bata taba ganinsa hakaba.
Bai dago ya kalletaba ya karba tissue din datake goge Masa zufa
Ya Dan kame kansa Yana kokarin basarwa a hankali yace"
Ya Isa haka, I'm okay kije
Kawai.
No Abbi bakada lfy
Kana gumi fa.
Ahankali ya furta"
I think my BP dropped.
Wat?" Tafada da sauri tana kallon yanayinsa.
Juyawa tayi da sauri tana cewa"
Bara naduba.
BP monitoring machine harma dasu sphygmomanometer ta dauko da sauri tadawo cikin damuwa sosai.
A tsaye ta taddasa kaman ba Wanda tabari Yana Dan hada gumi ba da jajayen Ido.
Da mamaki ta tsaya da Kaya a hannunta tana kallonsa cikin mamaki da kulawa tace"
Abbi?
Magana zatai ya Dan waiwayo ya kalleta a Dan kame yace"
Kibarshi kawai ya wuce
Zanyi baqi yanzu ki koma ciki.
Kallonsa tayi a marairaice da fuska Zata Kira sunansa da 'dan daga murya yace"
Nace kije Inayah.
Hawayen tashin hankali da tsoro taji suna Shirin gangaro Mata sbd yaune karon farko da Abbi yayi Mata tsawa tunda dai ta girma tasan kanta.
##MAMUH#
#AYSHATOUH MRS AA MAJEED
#LOVE/ROMANCE/MARRIAGE
_ZAFAFA BIYAR_
*_INAYAH_*
_MamuhGee_
*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_
*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_
*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_
_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*
ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070
Shedar biya👇
07040727902
MTN card👇
09134848107
[10/26, 8:44 PM] Sweet sis: *_27_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Kasa riqe hawayenta tayi suka gangaro Mata ta juya a sanyaye tana Satan kallonsa Zata fice ya sauke wani boyayyan numfashi tareda ajiyar zuciya Mai tafe da hucin zafin da Kai da kirjinsa suka dauka a natse Yana sake kame kansa da basar da yanayin dayake ciki ya bude Baki yakira sunanta a natse.
Da sauri ta juyo ta dawo Dan dama bason tafiyar takeyiba ta kallesa tana share hawayenta tace"
Na'am Abbi.
Sake sauke ajiyar zuciya yayi wannan karon kansa na qara daukan zafi Mai tsanani kawai dannewa yakeyi Yana basarwa kada hankalin 'yarsa