Author : Boss Bature Category : Complete Novels
fuskokinsu, ga rashin kuzari, haka ƴa'ƴanma sun tsare su da tambayoyi kamar ƴan jarida, amsar da suke basu shine su jira Shiekh Imam ya ƙaraso.
Hakan ba ƙaramin jefa su a rudani ya yi ba, hankalin Faryat ya ƙi kwanciya tun da ta je ɗakin mommynta ta ga babu ita babu dadynta, duk wanda ta tambaya ina suka je sai ya ce mata ta jira shiekh Imam ya ƙaraso zata ji komai a bakinsa, abun ya 6ata mata rai, dama bata so zuwa ƙasar ba Zaki ne ya taso ƙeyar su ita da Ibad bisa umarnin mahaifinsa.
Around ƙarfe biyu agogon Nigeria ya buga, a daidai wannan lokacin Private jet din da ya ɗauko iyalan Hateem ya yi landing a airport from Dubai.
Tun kafin ƙarasowar su, already prime minister ya tura da motocin canadian polices da zasu ɗauko su tunkafin ma flight din nasu yayi landing, kafin ka ce me gaba daya jikokin Obinna da surukansa sun hallara a gidan sa ƙwansu da kwarkwatar su, tun daga kan iyayensu har izuwa jikokinsa kaf ɗinsu, kowa da kowa, suna ta tambayar ina baba Obie da Hajiya Saratu ganin babu gifcinsu, nan ma ce masu akai su jira Shikeh Imam ya zo zai basu amsar tambayar su, lamarin ya ɗaure musu kai har ta kaiga ransu ya fara 6aci ganin sun ki faɗa musu meke faruwa, sun barsu cikin zullumi da fargaba, gaba ɗaya suka ƙagara da zuwan Sheikh Imam Malik...💔
Gaba ɗaya duk wani motsinsu akan idanun Baba Obie, haka zalika hayaniyar da suke ta yi duk yana jinsu, daga dakinsa yana kallon komai dake faruwa a gidan saƙo da lungu ko sauro ya gifta sai ya ganshi ta cikin laptop dinsa, farin cikinsa ragagge ne, a da in ya ga ahalinsa sun taru daɗi yake ji amma a yanzu kunya da fargaba ya ke ji saboda yasan tonan asiri za a yi masa kuma da zarar sun ji abun da yake aikatawa zasu tsane shi su shiga halin baƙin ciki da danasanin kasancewar su wani bangare nasa.
Sir Mubarak ne ya kira shiekh Imam ya sanar da shi cewa kowa ya hallara na family dinsu suna son su bayyana masu komai, ya taimaka ya zo don ya yi masu nasiha gudun halin da zasu shiga, Sheikh Imam ya ce yanzu haka yana akan hanyar zuwa estate din nasu.
Before ya ƙaraso gaba ɗayan su suka hallara a main falo, iyayen suna a zazzaune saman Sofas yayin da ƴan mata da samarin family din suka zazzauna kan rug, babu mai walwala akan fuskarsa..
Bayan ya iso ya shigo da sallama a bakinsa, cikin girmamawa suka gaishe da shi in ka cire Faryat da ta ɗage kai sama tana hura hanci, kamar bata gansa ba, ko arzikin mayafi babu a jikin ta, wata ƴar iskar short gown ce a jikinta ta marasa ɗa'a wadanda suka gaji rashin mutunci, ta kifa facing cap a saman kanta ta saki gashin ta a gadon baya, ga wani ɗan iskan shade data mannawa idanunta daga ka ganta dai ka ga ƴar duniya, a tsiya ce ta ke tauna gum a bakinta, sautin har fita ya ke yi ƙas ƙas, ba don iyayensu basa a cikin nutsuwarsu ba da tuni Sir Mubarak ya korata ta ɗauko mayafi, su twins da suka saka ta tsakiyar su, sun raku6e ko kaɗan ba annuri akan fuskarsu sai zallar damuwar halin da suka baro mommynsu a asibiti.
A hankali Shikeh Imam yake ƙare musu kallon da ya sa duk suka sha jinin jikinsu ga waɗanda basu san meke faruwa ba.
Ɗaura idanunsa ya yi akan iyalin Hateem dake a zaune kan doguwar sofa, sheikha Mujeedat tana a gefen Hateem, ta ɗauki wankan royal abaya ta alfarma, as usual ta saka chain mask akan fuskarta, kyawawan idanun nan nata suna akan Hateem da ya sadda kansa ƙasa yama kasa ɗagowa saboda zullumin abun da zai biyo baya idan suka ji abun da ya tara su, yana jin tsoron ya rasa gimbiyarsa fiye da yadda yake jin tsoron tozarcin da zasu fuskanta a gurin al'umma, saboda yasan koda ta haƙura zata ci gaba da zama da shi da baƙin tabon family dinsu ba lallai Royal Family ɗinta su yarda a zubar musu da mutunci ba, dama kafin auranta saida ya fuskanci ƙalubale ya sha wahala kafin aka bashi ita duk da tarin dukiyarsu saboda tsada ne da su, basu cika auren bare wanda ba jinin su ba, kuma ba royal family ba. Ruƙe hannunsa ta yi a cikin nata gam ta harɗe yatsunsu hakan yasa shi jin wata irin nutsuwa na shigar shi..
Gimbiyar izza Nazli da Yazrin suna a zaune daga gaban Sofa din da iyayensu suke akai, gaba ɗayansu royal gown ne a jikinsu sun yi rolling, tun da ta sadda kanta ƙasa bata ƙara ɗagowa ba saboda tsabar izza.
Mai girma Sharafuddeen shima ya haɗa nasa matan guri guda, yana a tsakiyar su saman doguwar Sofa, su Hajiya Laura anyi zugudum ta zabga tagumi da alama ba kwanciyar hankali a tare da su, daga ita har kishiyar tata, Gimbiya Malika dama tuntuni suke zargin da akwai abunda ke faruwa a family din, tun kan abun da ya faru da hajiya Saratu, mijinta Pravin da Baba basu zo duba ta ba, kuma mijin nasu ya ƙi basu amsar tambayoyin su.
Idan muka koma bangaren Iyalin His excellency Abdul Razak, Hajiya Muhibbat dake a zaune gefensa ta daura ƙafarfa ɗaya kan ɗaya, kowa ya shiga damuwa amma ita da alama ko a jikin ta, hasalima wayarta take daddanawa tana yi tana taunar gum a bakinta, gashi ta zuba uban ado kamar amarya..
Turai tafi kowa rashin sakewa, ta damu baiwar Allah, gabanta sai faɗuwa ya ke yi, tun da Sir Mubarak ya faɗa mata maganar meeting din da zasu yi, ran ta ya bata akan Hajjaty da Pravin ne amma da ta ga an kira kowa na family din sai ta ruɗe saboda ta fahimci ba abun da take hasashe bane, wannan yafi karfin laifin da su Hajjaty suka aikata.
Sir Mubarak dake a gefen ta kwata kwata hankalinsa baya akan kowa ya lula duniyar tunanin makomar rayuwar family ɗin su.
Ƴa'yansa suna a zaune gaban Sofas din da suke akai, Zaki da ya lumshe idanunsa kwata kwata bai so ya zo Nigeria ba, saboda baya son ma kusanta kanshi da abun da ya yi silar barin shi, sai gashi mahaifinsa ya dawo da shi. Ibad dake zaune gefensa na hagu abun ka ga mai kuruciya a kai, game yake bugawa a Ipad dinsa.
Daga ɗayan bangaren Dr. Jazz ne ya langwa6e kansa jikin sofa, bawan Allah har rama ya yi cikin ƴan kwanakin nan saboda damuwar rashin ganin baba Obie baya picking calls dinsa, kullum wayarsa a kashe, ba kamar yadda suka saba ada ba, a rana sau uku yake kiransa kuma baya missing picking call nasa, dama tun lokacin da baba Mubarak ya faɗa masa baba ya yi tafiya bai yarda ba sai da ya zargi wani abu daban, ga kuma abun da ya faru da hajiya Saratu, yau da aka tara su ya shiga ruɗu sosai, gabansa sai faɗuwa yake yi.
A bangaren Deen kuwa, shima yana zaune kan sofa tare da uwargidansa Jamila, batasan matsayar ta ba, kanta ya ƙulle, ta rasa gane meke shirin faruwa? Amma tana jin babu lafiya a family din..
Chief Owais yana a zaune dirshan kamar mai neman gafara, ba zaka ta6a gane halin da yake a ciki ba, gefe da gefensa Ziyad ne da Captain Yaseer sun saka shi a tsakiyar su, Dr Nadeem yana a gefen Captain, damuwa ce ƙarara akan fuskokin su, da ya ke su sun san komai.
Filin dake a tsakiyar Sofas din wasu jikokinne zaune saman Carpet, Dr.Nawaz sai Yusra ƙanwar Yaseer tare da Hindu ƙanwar Owais, da kuma Zulaihat ƙanwar Ziyad, sun jera layi kowannan su ya yi zaman cin tuwo, babu wanda gabansa baya faɗuwa, tun ma kafin su ji me za a faɗa musu.
Haka zalika Hajiya Madina tana a zaune gefen Senate Lateef, hannunta ruƙe cikin nashi sai tausar shi take yi ganin yadda ya yi sukuku kamar ba laka a jikin shi..💔
Sai da Shikeh Imam ya kammala kallace su tsaf kafin ya samu guri ya zauna kan Sofa din da ke fuskantar su, duk suka bi shi da ido gaba ɗaya sun ƙagara da son jin me zai ce..
"Ana ta ja mana rai, ni banga amfanin ɗauko mana malami ba, sai ka ce dai masu iskokai balle ace za'a mana rukiya.."
faryart ce take gunaguni bata kai ga ƙarasawa ba, Zayn ya make bakinta da tafin hannunsa ya buga mata warning, harara ta watsa mashi da yake ba kunya ce ta ishe ta ba..
"Nifa na rasa ganewa, kaina ya kulle, meke faruwa ne? Meke damun kowa ne? Nifa bana son tashin hankali, kowa ka tambaya sai ya ce a jira sheikh a jira sheikh ga sheikh din ya zo amma ya yi shiru yana ta kallon mu kamar ya samu tashar bollywood..."
Rai a ɗan bace Dr.Nawaz ya yi maganar shima da yake ba kunya ta ishe shi ba, tsagera ne..
"Karka kuskura ka ƙara magana!" A ɗan tsawace Nadeem ya faɗa, kallonsa ya yi tare da yamutsa fuskarsa batare da ya furta kalma ba.
"Mijin mace ɗaya, yau ahalin namu ba lafiya, kamar masu zaman makoki, ni bansan meyasa ka matsamin akan in zo ba, ina tsaka da hidimar biki kasa na baro dangina, nayi nayi ka faɗamin meke damunka ka ƙiya, ga sheikh din ya ƙaraso ya wani tsare mutane da idanunsa kamar wasu masu laifi, wlh zan tafi ne idan na gaji da zama, kuma dai kasan bana zaman jin wa'azi ehe..." Her excellency Muhibbat ce ta fada tana kallon Abdul razak hada murguɗa ƙaramin bakin ta, tana karkaɗa ƙafarta..
Da yake yasan halin kayansa bai biye mata ba..
"Nifa Allah na gani, malaman sunnar nan ba burgeni suke yi ba, wlh da nasan tara mu za'a yi don a yi mana wa'azi ba abun da zai sa in wanko ƙafa in biyo mommy mu zo nan.." Cike da takaici Yusra ta yi maganar tana jifar Imam da harara a fakaice.
In a cool voice Hindu ta ce, "Pls, Yusra, mu ƙara haƙuri, bai kamata kina fadin maganganun nan ba.." cuno baki ta yi ita ala dole an takura mata..
Gyaran muryar da sheikh Imam ya yi musu ne ya ja hankulansu ga dubansa, gaba daya suka tattara nutsuwarsu da hankalinsu a kansa, a hankali ya zauna kan Sofa din dake fuskantar kowannan su.
"Innalhamdu lillahee, nahmaduhu wa nasta'eenuhu wa nastaghfiruhu, wa na'oodhu billaahi min shuroori anfusinaa wa min sayyiaati a'maalinaa. Wa man yahdillahu fala mudillilahu, wa man yudlil falaa haadiya lah "Alhumdulillah. Indeed, all praise is due to Allah....'
ya ɗan dakata yana dubansu kafin ya ce, "Sallu Alal nabiyyul Kareem, Sallallahu Alaihi Wasallam..."
atare suka haɗa baki gurin karasa ambaton Sallallahu Alaihi Wasallam
kafin suka fara yin salatin annabi, Faryat dai ta ƙi tsayar da hankalinta guri guda, bayan sun kammala ya soma magana cikin harshen turanci saboda yana son kowan nan su ya ji me ya ke faɗa,
"Nasan gaba ɗayan ku kun ƙagara ku ji dalilin da yasa aka umarce ku da ku baro komai da kuke yi ku zo nan, wataƙil an takura maku amma abu ne na gaggawa wanda da bukatar ku haɗu domin mu nemawa kanmu mafita a tare game da musibar da ta kunna kai a family din nan.. "
Cike da tsantsar ruɗani suke jefawa junansu kallon kallon ga waɗanda basu san meya faru ba.
Numfasawa sheikh Imam ya yi kafin ya daura da cewa, "Kafin mu fara sanar da ku, ina so in fara tunasar da ku da nasiha, saboda gudun halin da zaku shiga..."
Maganganun sheikh Imam sun rikita lissafin kwakwalan su, sai zare idanunsu suke yi cike da fargaba.
Tun da ya fara yi masu nasihar suka yi shiru suna sauraran shi, ko tari babu wanda ya yi a cikin su, da alama nasihar ta ratsa zukatansu, jikinsu ya yi sanyi lakwas saboda tsoron Allah da ya ƙara shigar su, duk da akwai tarin fargaba da zullumin abun da zai biyo bayan nasihar tashi don sun san dole akwai maƙasudin yin ta.
"Jazakallahu Khairan Malam, mungode da nasiha, Allah ne kadai zai iya biyan ka.." Hajiya Madina ce ta yi maganar cikin sanyin murya,
"Sai dai gaba daya hankalin mu ba a kwance ya ke ba, mun damu da ganin halin da mazajen mu suke a ciki, sannan babu Baba, Saratu ma bamu san ina take ba, munyi munyi su faɗa mana gaskiyar abun da ke faruwa sun ƙi sanar da mu, sun ce mu jira ka ƙaraso za mu ji komai a bakinka, don Allah malam ka faɗa mana, koma menene in wani ya rasu ne in kuma wani abun ne a fada mana, we're all muslim mun yi imani da kaddara mai kyau da mara kyau,.."
Ta karasa maganar fuskarta a yamutse, gaba daya sauran suka tsoma bakinsu akan a fada musu meke faruwa.
Shiru Sheikh Imam ya yi, shi kanshi yana jin fargaban sanar da su, saboda ya lura akwai masu ƙarancin tawakkali a cikin su.
"Bismillah Owais, ka fada masu komai dake faruwa..." Ya faɗa idanunsa akan Chief Owais da ya raku6e kansa jikin Sofa, gaba daya suka mayar da dubansu gare shi.
Tunani ya ke yi taya zai fara sanar da su? ya zasu dauki abun? Me zai biyo baya?
Ba kaitsaye ya fara sanar da su ba, saboda harshen sa yayi rauni, ba zai iya ɗaga muryarsa ya yi magana mai tsayi ba.
A hanakali ya zaro wayarsa daga cikin trouser pocket dinsa, ya mike cike da rashin kuzari a jikinshi ya ɗaura wayar saman c-table din dake a gaban Imam Malik, bayan ya kunna masu video din dake ɗauke da duk wani bayani game da gidan Kurkukun ƙaddara da miyagun ayyukan da ake aikatawa a cikin sa..."
Ya ƙure musu volume yadda kowa zai ji dakyau, zama yayi dirshan gaban table ɗin tare da sadda kan shi ƙasa..
Da ya ke cikin harshen turanci ya yi audio din kowannansu yana sauraro kuma yana fahimtar me ake cewa, tun suna jin abun kamar shirin wasan kwaikwayo har suka fara ruɗewa da jin irin azabtarwar da ake yiwa matasan yaran da basu ji ba basu gani ba. Lokaci ɗaya suka ruɗe, suka fara tambayar Owais wai dagaske ne abun da suke sauraro yana faruwa ko dai ƙagaggen labari ne na almara? Gaba daya sun kasa yarda da gaske ne saboda aganinsu ba zai ta6a yiwuwa a rayuwar zahiri ba, don ko a tarihi basu ta6a jin makamancin labarin kurkukun ƙaddara ba, sai dai abun da ya ɗaure musu kai chief Owais ne ya ke yin magana a cikin audio din, sun gane voice dinsa ne.
Hajiya Laura ta ce yaushe Owais ya zama ɗan jarida mai karanta hausa novel? Abun da daure kai.."
Her excellency Muhibbat ta ce, "Ni na rasa ganewa, mu da muka zo don mu ji meke faruwa da mazajen mu why za'a kama bamu labarin ƙanzon kurege..."
Lokacin da audio din ya yi nisa hankalin wasu daga cikin su ya tashi matuƙa, ƴan matasan cikinsu har sun fara zubda ƙwalla saboda yadda labarin ya ta6a zuciyar su har suna fadin wannan rashin imanin ya yi yawa, yaran nan ana zabtar da su wlh, saboda baƙin zalunci na wasu mutanan da babu Allah a ransu, kowa dai yana ta tofa albarkacin bakinsa, wadanda suka fi tausayi a cikin su irin su Jazz da Hindu da Zulaihat da Turai tuni sun fashe da kuka saboda tausayin yaran da ya kama su tsigar jikinsu har tashi take yi, musamman da aka zo kan labarin Unaizah da Majnoon wa'iyazubilla! Kuka sosai suke yi abun ya ta6a zuciyar su, hatta Gimbiya Mujeedat saida ta matse ƙwallarta, itama Hajiya malika zuciyarta ta yi rauni ta dinga fadin Owais ku yi mana bayani mana, wani darasi ne ake so mu ɗauka acikin labarin nan? Meyasa kuka kunna mana shi? Ko dan mu ƙara imani ne um?"
Cikin sanyin murya Owais ya ce mommy ki yi hakuri ki ƙarasa sauraran shi, ta ce toh Owais Allah yasa mu ji Alkhairi, duk rashin tausayin su twins saida jikinsu ya yi sanyi lakwas dama zuciyarsu a raunace take duk sunyi sukuku da su a ransu suna ayyana in da gaske labarin kurkukun kaddara ke faruwa ya wadanda abun ya faru da su zasu ji?
Dr. Nawaz da Faryart da Yusra ko gizau basu yi ba, tabbas labarin ya ta6a zuciyoyinsu sai dai ba kamar sauran ba, saboda su a tunaninsu bazai ta6a zama gaskiya ba, ƙagaggen labari ne kawai, jin abun suke yi wani iri.
Ibad sarkin tsoro ga tausayi da ya addabe shi, tuni ya aje game din da yake bugawa, jikinsa sai kerma ya ke yi kamar mazari hakan yasa Sir Mubarak ya rungumo shi a jikin shi.
A hankali Zaki ya zaro hanky daga aljihu ya soma share ƙwallar dake gangaro masa saman kuncin sa, zuciyarsa ta karaya.
Shiekh Imam dake kallon fuskokinsu a hankali yake karantar yanayin su, tun anan ya fahimci masu rauni da marasa raunin cikin su..
Hatta Yazrin so take ta fashe da kuka ta kasa sai dai ta sadda kanta ƙasa, gimbiyar izza kuwa tun da ta fara sauraron Audio din bata motsa ba, dama ita haka take da wuya mutun ya iya karantar abun da ke a ranta ta yanayin fuskarta, saboda tsabar izza, Amma fa da alama ta razana da jin labarin kurkukun kaddara, duba da yadda yatsu ta suke ta kerma, cheeks dinta sun yi jawur saboda kaɗuwar da ta yi, haka zalika Hajiya Jamila tausayi yasa ta kasa jurewa, sai faman sharce ƙwalla take yi da yatsun ta.
Cikin rauni na murya Jazz ya ce, "Tun da uwata ta haife ni a duniyar nan ban ta6a jin labari mai ban al'ajabi ba irin wannan! rashin imanin ya yi yawa, wasu mutane ba tsoron Allah, zalunci da mugunta kadai suka sa a gaba, na rasa gane me yasa idon wasu mutane ke rufewa akan neman duniyar da zamu mutu mu barta, basu tuna cewa suma fa halittar su aka yi kuma zasu mutu su koma ga Allah ne, amma dai yaran nan sun bani tausayi wlh, an azabtar da rayuwar su..."
Bai ƙare maganar ba, cikin karyayyar murya Ziyad ya ce, "Wlh tun