Kurkukun Kaddara Final StepComplete Hausa Novel

Author :  Boss Bature Category :  Complete Novels

Chapter   61 / 107

180K to 183K   out of 319.4K words

yi aka kaita kurkukun ƙaddara."

Tambayar ta Sajeed ya yi wacece Khala? Nan take ta labarta masa irin taimakon da ta yi mata, duk da baisan wacece ita ba ya ji ta kwanta masa a rai, kuma yana son ya ganta saboda taimakon da ta yi ma yar uwarsa. Kwantar mata da hankali ya yi ya ce zai tambayi Chief game da ita don su ji in tana a raye.


Bayan fitar Chief Owais daga ɗakin bai nufi ko'ina ba sai ɗakin da aka kwantar da amininsa, shigar sa dakin ya yi daidai da fitowar Omar daga toilet, yana tafiya daƙyar daƙyar, jikinsa sanye da kayan mara lafiya, kwata kwata bai lura da mutun a ɗakinsa ba, gadon sa ya nufa yana niyyar haurawa don ya kwanta unexpected muryar Owais ta katse shi, "Alhamdulillah, Ya Allah na gode maka da ka farfaɗomin da aminina! Na gode Ya Allah..." Cike da farin ciki Big Guy ya waiwayo tare da kallonsa.

Bazai iya jira ya ƙaraso ba, da sauri ya nufesa suka rungume juna, irin sosai ɗin nan.



"Na yi kewarka Omar, kullum da tunaninka nake kwana, ina ta zullumin kada na rasa aminina, bansan ina zan samu madadinka ba." Cikin shesshekar murya ya furta kamar zai fashe da kuka.


Daɗi da farin ciki suka lullu6e Omar, in a cool voice ya ce, "Nima na yi kewarka bugun zuciyana, na so a ce kaine mutun na farko da idanuna suka fara yin tozali da shi a lokacin da na farfado amma sai na ga akasin hakan, baka ji yadda na ji ba, bansan meya faru ba tun bayan dana fita hayyacina a gidan kurkukun kaddara, amma da docs suka faɗa mini kana nan da ranka da lafiyarka sai na ji farin ciki ya cika ni, saboda ni damuwana akanka ne, ina son ka aminina." Ya faɗa yana ƙara hugging dinsa, daga gani sun yi kewar juna sosai, farin ciki duk ya cika su.

"Omar, ina fata babu inda ke yi maka ciwo a yanzu? Ka ci abinci? Ka yi wanka?" Dariya ya yi, "Ka kwantar da hankalinka, doctor ya tabbatar min da na samu lafiya, raunin da na ji a brain ɗina ya warke.." Leƙa kansa Chief ya yi ya dudduba daidai inda aka yi masa ɗinki, ya ji daɗin ganin yadda gurin ya warke sosai.


"Allah ya ƙara maka lafiya da tsawancin kwana aminina.." Da fara'arsa ya amsa masa da, "Ameen, kaima haka mutumina."


"Am sorry Omar, na yi maka laifi, kwana biyu ban leƙo na duba ka ba, bani da kwanciyar hankali, abubuwa da dama sun faru masu daɗi da marasa daɗi..."


Damuwa ce ta bayyana akan fuskar Big Guy, "Don Allah ka faɗa min meya faru? Me ake ciki? Dame dame ya faru bayan doguwar sumar da na yi? Ina Danish? Ina Salsabeel da Taj? Ina U.s armies? Ya labarin kurkukun kaddara da Elders da su na farka a raina? Har yanzu baku gano su wanene ba?"


Kamar ɗan jarida ya tsare shi da tambayoyi.

Girgiza kai Chief ya yi cike da takaici ya ce, "Omar, zan fada maka amma ba yanzu ba, na fi so lafiyarka ta inganta, bana so kaji abun da zai ɗaga maka hankali..."


Bai kare maganar ba, Omar ya ce, "Kada ka damu da lafiyata na ji sauƙi, kawai ka fada min! In ba haka ba hankalina ba zai ta6a kwanciya ba wallahi.." Matsa mashi ya yi akan ya fada mashi saboda ya kagara da ya ji me ya faru..

Ba don ya so ba, cikin karyayyar murya ya fara zayyana masa abubuwan da suka faru,
wa'iyazubullah! Lokaci ɗaya idanun Big Guy suka rikiɗa suka koma jajir, zufa ta fara tsattsafo masa saman fuskarsa, tsantsar tashin hankali da ruɗani ne akan fuskarsa, al'ajabi ya kama sa, damuwa da baƙin ciki suka mamaye zuciyarsa duk a lokaci ɗaya..

Cikin shesshekar murya ya furta, "Owais, jin komai nake kamar ba a gaske ba, kamar a mafarki ya faru, ina ma ace ban farfaɗo daga coma din nan ba, in mutu kawai!" Ya faɗa hawaye masu ɗumi suna sauka kan kuncinsa..

Wani irin kunci da baƙin ciki ne suka tarar masa a cikin zuciyarshi, idanunsa sun kaɗa jajir..

"Ban yi mamakin jin mahaifina ne Jan Wuya ba, zato zunubi ko da ya kasance gaskiya, amma wallahi, rantsuwar ɗan musulmi tun da labarin kurkukun kaddara ya riske mu na ji a raina mahaifina yana ɗaya daga cikin azzaluman da suke da sa hannu a cikin sa, na yi shiru ne saboda bani da hujjar da zan tabbatar da zargina akan shi shiyasa ban ta6a faɗa maka ba. Amma zuciyata ta karaya da jin cewa baba Obie shine Shugaban kurkukun ƙaddara! Hankalina ya tashi Owais, ban ta6a jin tsanar rayuwar duniya irin na yau ba. Owais meke damun su ne? Wani irin neman duniya ne wannan? Da zalunci da mugunta? Me suke nema ne wai? Wani irin tushewar basira ne haka? Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un!.."


"Baba Obie bai kyauta ma rayuwarsa ba bai kuma kyauta maku ba, wallahi nafi jin zafin halin da kuka shiga akan wanda ni na shiga, saboda baba Ya zalunce ku, Ya dade Yana ha'intarku da fuska biyu, Owais, wai dan Allah da gaske ne? Ba mafarki ba? Wannan wata irin baƙar kaddara ce Allah ya jarabce mu da ita?"

Ɗaura kansa ya yi akan kafadar Chief Owais ya fashe da kuka tamkar ana zare ransa.

Cikin sanyin murya Owais ya ce,"Shiyasa ban so ka matsa min akan in fada maka ba Omar! Saboda nasan ba zaka ji dadi ba.."


"Allah Ya isa tsakanina da shi, Allah ya wulaƙanta rayuwarsa tun a gidan duniya, Allah ya haɗa shi da dukkan musiba da fitintunun duniya, Allah ya saukar masa da cututtukan da zasu hana sa kwanciyar hankali, ko na minti ɗaya ban son ya ƙara jin dadin duniya. Lalacewar sa kawai nake son na gani, ban ta6a tsanar wani mutun kamar yadda na tsani mahaifina ba, shaiɗanin mutun azzalumi, fasiƙi mai kafurar zuciya, mutumin da tun da ƙuruciyata yake nema na, ni wai! Ɗansa na cikinsa! Shine Ya 6ata min rayuwata ya jefa ni a harkar safarar miyagun ƙwayoyinsa, ya hana rayuwata sukuni, ya ƙi bari mahaifiyata ta bani tarbiya, ya raba ni da danginsa, ya dinga sarrafa ni son ranshi. Owais ina da ciwon baƙin cikin da ya ƙunsa min, wallahi Owais ba don Allah ya ƙaddara zuwan ka cikin rayuwata ba, da yanzu nima ina ɗaya daga cikin giant din kurkukun kaddara, Allah ne ya tsare ni, wataƙil addu'ar mahaifiyata ce ke bibiyar rayuwa na, shiyasa bai yi nasara akaina ba..." Kasa ƙarasa maganar ya yi wani kalulun baƙin ciki mai tattare da radadi ya sarƙe muryarsa, ya kuma fashewa da kuka yana tari.

Cikin sigar lallashi Owais ya daura tafukansa a saman bayansa a hankali yake dan bubbuga sa yana lallashinsa.

"Omar, ka yi hakuri, ka yi hakuri, kuka bashi bane mafita ba, muma mun shiga mawuyacin hali, wanda na yi imanin dukkanmu in aka bincika lafiyarmu babu wanda za a samu batare da ciwon zuciya ko hawan jini ba, saboda depression din da ya kama mu, amma ba yadda muka iya, dole muka yi hakuri saboda bamu isa mu sauya abin da Allah ya kaddara faruwarsa a cikin rayuwar mu ba, bawa bai isa ya gujewa kaddararsa ba, iya cuta dai an cuce mu, an yi mana bakin ta6o, amma ba komai akwai Allah, su ke tunanin sun zalunce mu, wallahi bamu suka zalunta ba, kan su suka zalunta, sun kashe rayuwarsu da kansu, sun yi asarar duniyarsu da lahirarsu!"


"Na fi jin tausayin ku Owais, ni bana jina a matsayin kowa, na rayu batare da dangina ba, bakowa ya sanni ba ko a family ɗinmu, ku kuwa duniya ce ta san ku, ina jiye mana halin da zamu shiga idan asiri ya fallasu mutane suka sani, bana so ahalinmu su muzanta a idon duniya, bana son laifin da bamu muka aikata ba ya shafe mu, mutane bakowa keda fahimta ba, wasu dama jiran mu suke yi, mun tara maƙiya da mahassada nasan da zarar sun ji abun da ke faruwa zasu yi farin cikin samun hanyar da zasu baƙanta mana rai don su ga raunin mu. Owais ya zamu yi? Meye mafita Owais um?"



"Omar mafita ɗaya ce! Shine mu yi hakuri mu rungumi kaddara! Mu dogara ga Allah, mu miƙa lamuranmu gare shi, mu aje batun mutane gefe ɗaya, addu'a ita ce takobin da zamu kare kanmu daga dukkan me nemanmu da sharri."


Gaba ɗaya komai da suke tattaunawa a cikin kunnan Salsabeel yana gani kuma yana sauraron su, tun da suka fara magana.


Bawan Allah ashe ya ji labarin zuwan Chief a bakin docs din dake kula da su, shiyasa ya yanke shawarar zuwa ya gan shi ya ji shiru bai leƙo shi ba.


Unfortunately ya iske shi a dakin Omar suna tattaunawa, kunnuwansa sun jiyo masa abun da ya karya masa zuciyarsa, yana daga tsaye bakin kofar ɗakin, hannunsa ɗaya ya ɗan karkace da ɗauri a jikin shi, fuskarsa ta jiƙe sharkaf da hawayenshi, so yake ya yi kuka sosai amma ya kasa, saboda bai son su san ya ji bai san ya zasu ɗauki abun ba, duk da shi bai zo da niyyar ya yi masu la6e ba.


Ba zai iya jurewa ba, ya gaza yarda Danish babu shi a doron duniya, yaron da ya kwallafa rai akan son ganin ya haɗu da iyayensa ya kuma samu farin ciki mai ɗorewa a rayuwarsa, ga kuma tausayin Owais da Omar da ya kamasa, da farko ya yi farin cikin jin sun gano su wanene elders saboda shi kanshi ya ci burin ya gansu da ainihin suffarsu, amma da ya ji akwai kakan Owais da mahaifin Omar sai ya ji zuciyarsa ta karaya, jikinsa ya yi sanyi lakwas, damuwa da tashin hankali suka baƙunci zuciyarsa. Wlh ya ji ɗacin jin cewa dasa hannunsu a ciki sune ma giggan kurkukun, bayin Allah gwanin ban tausayi yake kallon su..


Jikin sa a sanyaye ya juya zai bar dakin, har ya kusa fucewa muryar Omar ta katse shi, "Salsabeel! Kai ma ka ji komai ko?" Baisan ya ganshi ba, lokacin da zai ɗago da kansa daga kan kafadar chief Owais ya hango shi.

A hankali ya juyo ya fuskance su, "Ku yi hakuri, ba labe nake yi maku ba, na ji zuwan Chief shi na zo nema, sai kuma na taras da shi a dakin ka.."


"Kana nufin baka ji komai da muke tattaunawa ba?" Umar ne ya tambaya fuskarsa a marairaice,


"Ku yi hakuri, amma na ji komai da kuka tattauna, haƙiƙa zuciyata ta karaya, tsigar jikina ta tashi, na ji abun da ya ɗaga hankalina, ya kuma jefa ni a hali na damuwa, wallahi ban ta6a zaton za a samu Elders a family din da ya daga cikin ku ba, saboda kyawawan halayanku, amma idan na tuna faɗar Allah wannan bakomai bane..." Ya faɗa yana tafiya a hankali yake tunkarar su. "Na tausaya ma rayuwar ku, da ahalinku, bansan tayaya zan misalta maku ba, amma na razana sosai..."


Daga gaban gadon ya tsaya tare da goya hannayensa akan ƙirjinsa..

"Sai yanzu na gane dalilin da ya sa lokacin da Danish ya rikiɗa ya zama maciji bai nufi ko'ina ba sai gidan kakanka.."

A ruɗe suka dube shi.

"Kiranye ne ya yi mashi saboda yana son ya mayar da shi gidan kurkukun ƙaddara, ni nasan ba za a rasa gurin da ya ke6ance a cikin ɗakinsa ba, wanda da zarar Danish ya faɗa ciki zai mayar da shi kurkukun ƙaddara ta ƙarfi ta tsiya..."

Cike da takaici suka girgaza kawunansu.

ɗakin yayi tsit na ɗan lokaci kowa da abun da yake saƙawa a zuciyarsa.

Akwai tarin tambayoyin da suka cika zukatansu wadanda suke so su yi ma Owais sai dai damuwa ta hana su furta 💔


A daren ranar suka baro asibitin su dukan su, tare da twins bayan da docs suka tabbatar da lafiyarsu ta inganta ba abun da za su bukata..

Ba sai na bayyana maku irin farin cikin da su Unaisah suka yi ba na ganin Sajeed da twin sister din shi, duk a daren ranar Owais ya dawo da sauran yaran gidansa. Murna a gurinsu kamar waɗanda akaiwa albishir da gidan Aljanna...



Luxury-incense By Sapnah Borno.
Ta kawo muku turarukan wutan su Na maiduguri dana chad, turarukanta masu masifar dadi da kama waje harma da daukar hankali, indai kikayi kabbasa da turaren ta har wajen da kika zauna indai kika tashi sai kin bar kamshin ki, sannan Tana saida mayukan gashi irin nasu na shuwa Arab masu tasirin gaske, wajen gyaran Amare kuwa babu magana dan tazo muku da Chadian and Sudanese dilka Wanda zaki gyara jikinki da kanki, oga ya kasa ganeki, haka zalika akwai wata humrar ta mai suna hana bacci da kuma sirrin shuwa Abun ba magana, yar uwata ki jarraba turaren yar mutan borno nasan zata zame miki best turaren wuta plug. Tanada turarukan da zaki turara gida, toilet, bedsheets, curtains, kabbasa and hair incense ku jarraba kada ku bari ayi babu ku.
Wardrobe balls
Kabbasa spray
Chadian khumra
Hawee
Halud
Gabgab
Sandal sukkariya
Kajinguru
Dilka soap
Ready to use dilka
Karkar oil
Turaren tsuguno
Habil
Dorut
Dorot after period
Brown khumra
Dufr khumra
Body milk
Sudanese kuleccam
Chadian dufr kuleccam
Musk khumrah.

Maganin matan mu sunada inganci Wanda muke kawo su daga sudan, sannan munada maganin karin girman nono, Wanda basuda effects, ga masu bukatar maganin Matsi ko maganin mata Masu aiki garanti munada su, sannan muna zuwa gyaran jikin amarya a duk garin da take

Our Chadian aphrodisiacs are.
Beejay fire
Sata jagab honey
Wetness and sweetness combo
Daka
Great A sabaya
Breast engagement powder
Ciccibi
Gumbar madara
Gumbar dabino
Bita Zaizai

08093772168


*Welcome, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan number din 08103884440*~_____💞______💗_____💘_____🌹______💋_____💫_____🫀___~



Luxury-incense By Sapnah Borno.
Ta kawo muku turarukan wutan su Na maiduguri dana chad, turarukanta masu masifar dadi da kama waje harma da daukar hankali, indai kikayi kabbasa da turaren ta har wajen da kika zauna indai kika tashi sai kin bar kamshin ki, sannan Tana saida mayukan gashi irin nasu na shuwa Arab masu tasirin gaske, wajen gyaran Amare kuwa babu magana dan tazo muku da Chadian and Sudanese dilka Wanda zaki gyara jikinki da kanki, oga ya kasa ganeki, haka zalika akwai wata humrar ta mai suna hana bacci da kuma sirrin shuwa Abun ba magana, yar uwata ki jarraba turaren yar mutan borno nasan zata zame miki best turaren wuta plug. Tanada turarukan da zaki turara gida, toilet, bedsheets, curtains, kabbasa and hair incense ku jarraba kada ku bari ayi babu ku.
Wardrobe balls
Kabbasa spray
Chadian khumra
Hawee
Halud
Gabgab
Sandal sukkariya
Kajinguru
Dilka soap
Ready to use dilka
Karkar oil
Turaren tsuguno
Habil
Dorut
Dorot after period
Brown khumra
Dufr khumra
Body milk
Sudanese kuleccam
Chadian dufr kuleccam
Musk khumrah.

Maganin matan mu sunada inganci Wanda muke kawo su daga sudan, sannan munada maganin karin girman nono, Wanda basuda effects, ga masu bukatar maganin Matsi ko maganin mata Masu aiki garanti munada su, sannan muna zuwa gyaran jikin amarya a duk garin da take

Our Chadian aphrodisiacs are.
Beejay fire
Sata jagab honey
Wetness and sweetness combo
Daka
Great A sabaya
Breast engagement powder
Ciccibi
Gumbar madara
Gumbar dabino
Bita Zaizai

08093772168.





Idan muka koma bangaren jikokin Baba Obie mazauna ƙasar waje, da matayen ƴa'ƴansa da basu samu halartar family meeting ba, saboda uzururrukan da suka ruƙe su, kwata kwata basu da masaniya game da abun da ke faruwa da ahalinsu na Nigeria saboda ba a sanar da su ba, sai dai kowan nan su ya damu da rashin samun iyayen nasu a waya, sun saba akai akai suna kiran su su ji lafiyarsu, ko su yi fira a family groups din su amma wannan karon komai ya sauya ba kamar yadda suka saba ba, ko sun kira basa samun su, hakan yasa suka fara tunanin su dawo gida don su duba meke faruwa da ahalin nasu.




Mazauna ƙasar wajen ne suka tattauna maganar a wani video call da suka yi tsakaninsu kuma suka yanke shawarar zuwa, batare da iyayensu sun sani ba, haka matayensu ma sun yi deciding biyo sahun mazajen su da suka ji shiru basu dawo ba kuma sun daina picking calls ɗin su.



~_____________________________💔✍️~




Sheikh Iman ne ya shawarce su da su kira sauran ahlin nasu su fada masu komai, tun kafin duniya ta ji, gudun halin da zasu shiga idan suka tsinci labarin a waje.



Batare da 6ata lokaci ba suka ɗauki shawarar shi kowannansu ya kira matar shi da ya'yan shi ya umarce su da su bar komai da suke yi su zo gida zuwa gobe, sa'ilin da suke kiran su a waya yanayin muryoyinsu sun ɗaga masu hankali, hakan yasa wasu daga cikin su suka gaza hakura sai gobe su taho. A yammacin ranar flight din su gimbiya Her Excellency Jamila ya yi landing from Kaduna to Abuja, tare da Autanta Dr. Nawaz ta zo shima ba mazaunin ƙasar bane a Uk yake aikin likitancinsa, an ci sa a da safe ya dawo Nigeria sai kuma ga kiran da ya riske su na gaggawa hakan yasa bai yi ƙasa a gwiwa ba ya biyo mommynsa suka taho....



Washe garin ranar kiran sallar asubahin farko, business jet din da ya ɗauko su Zaki Mubarak Obinna ya yi landing a airport, tun jiya jirginsu ya taso su uku ne suka zo tare da Faryat da Ibad, bayan Zaki ya kira daddynsu ya sanar da shi sun ƙaraso, ba tare da 6ata lokaci ba ya tura da motocin escorts suka ɗauko su.



Basu jima da ƙarasowa ba, sai ga kiran hajiya Her Excellency ya shigo wayar Deen bayan ya daga ta sanar da shi gasu a airport sun karaso, bai tsaya bata lokaci ba ya tura da motocin securities suka tafi dauko su, su biyu ne suka zo tare da last born ɗinta Dr. Yusrah.



Wuraren goma sha biyu na safe, mai girma Sharafudeen tare da Iyalansa suka ƙaraso Estate din.



Ba a fi ƴan mintuna da zuwansu ba, sai ga iyalan Senate Lateef sun shigo gidan baban suma..



A hankali ahalin suka fara taruwa a gidan Baba Obie, duk wanda ya zo da walwalarsa da zarar ya ga halin da ƴan gidan suke a ciki sai kaga yanayin fuskarsu ya sauya zuwa tsantsar damuwa da ruɗani, iyayensu mata suka dinga tambayar mazajensu meya faru da su? Meyasa suka rame? Meke faruwa ne babu walwala kan

61 / 107