Author : Jamsy Category : Complete Novels
mu yi wani abu mana shi mahaukacin masoyi ki nuna masa kin amince da soyayyar shi, domin ta haka ne kawai zamu iya gano wane ne."
Da sauri ta kalle shi jin abin da ya ce sai ta ci gaba da tuƙi ba ta ce komai ba.
"Akan me zan fara soyayya da wanda ban sani ba ko aljani ne, musaki ne duka ba ni da matsaniyar hakan?"
"Ni ma ai ba wai son gaskiya nake nufin ki yi masa ba. So nake ya yarda kina sonsa har ya bayyana kansa." Ya ce mata yana kallonta.
"A'a, wannan ba mafita bace." Ta ce tare da kallonsa sai ta mai da hankalinta kan tuƙi ta ci gaba da cewa,
"Hakan ba mafita bane ina tsoron kar na ƙara amincewa, abu ya kwaɓe ka zo ka barni a ciki irin wancan. Kuma Ummu yau ta yi mini kashedi mai ƙarfi kan ko waye kar na kuskura na amince masa. Don haka mu bar maganar in ya gaji da haukarsa zai daina. Da zarar na kammala karatuna na yi aure ai dole ya haƙura ya zo ya karɓi kayansa ko?" Ta ƙarashe maganar tana tambayarsa.
"Over my dead body! Ke tawa ce kuma an halicce ki saboda ni." Ya faɗa a ransa ganin kallon da ta tsaresa ya ba ta amsa da cewa,
"Mu gwada hakan wataƙila ma dace. Kuma na yi miki alƙawarin a duk lokacin da lamarin ya kwaɓe zan karɓi hukuncin duka."
"Promised?" Ta tabbaye shi.
Ɗaga mata kansa ya yi wanda ya sa ta ce,
"To shikenan zan gwada. I will do as you said." Ta ce daidai lokacin da ta ƙaraso ta yi paking tare da kashe motar tana kallon shi.
"Yauwa ƙanwata. Ma za ki shiga aji bari na koma gida."
"A motar haya? Na san fa ba ka son hawa. Kawai ka je da motata sai ka sanya direba ya kawo mini amma a waje za ka ije karka shiga ciki da ita saboda Ummu."
"Mai zai kai ni bayan na san ƙaryar da na shara mata." Ya ce yana dariya.
Tsayawa ta yi har ya tada motar ya fara tafiya, sai ta ɗaga masa hannu tana kallonsa cikin tsananin ƙauna. Tana son yayan nata don ya damu da lamarinta. Rungume laptop ɗinta ta yi ta shige departmen ɗinsu.
A lokacin da ya dawo, Ummu ba ta ce masa komai ba har ya ci abinci ya fita. Don ma ƙin fitowa ta yi ko da ya tambayeta tana bacci.
Bayan Hilah ta gama lectured ta tuƙa motarta ta dawo gida.
Ta shigo da sallama tana kallon su Umnaah dake zaune suna kallo.
Gefen su ta zauna bayan sun yi mata sannu da zuwa.
"Ke Azerh ba kin ce Malamin kunya gaya miki in har ba ki kai masa haddarki ba zai zane ki, shi ne kika tsaya kallo?"
"Ƙyale shi Anty Hilah, ya cika takura haka jiya na ƙi ƙallah don na yi haddar, amma da na kai masa cewa ya yi ba ta zauna ba. Duka ne ya saba mini, don maimaici ne in ban kalla ba ya wuce."
"Lailai haka kika ce? Ai ko kya ta shan duka kamar jaka." Amnaah ta ce.
"Allah ya shiryeki, wasa kike yi wa haddar shi ya sa, randa kika yi ninya ai tana zama." Ta ce tare da miƙewa za ta shige ɗakinta daidai lokacin Ummu ta fara saukowa ƙasa wanda ya sa ta fasa.
Huwais da ya ji dawowarta ya taho da sauri don y ganta yana shigowa Ummu ta ji daɗin hakan.
"Sannu da fitowa Ummu." Ta furta cikin girmamawa.
Ummi da take a fusace ba ta yi wata-wata ba ta ɗuke ta da mari.
"Haba Ummu mai ta yi miki?" Ya yi tambayar cikin tashin hankali wanda kafin ya gama ta ɗaura masa na shi, sai ya riƙe kumatunsa cikin tsananin ɓacin rai.
"Haihuwarku na yi! A tunaninku za ku yi mini wayo ne? Kar nake ganin ku marasa tunani kawai. Na tambayeka inda za ka ka yi mini ƙarya she tare kuka fita? In har ba rashin gaskiya kuke ƙullawa ba uban mene ne na ƙin gaya mini gaskiya. Har da ke munafuka kin kwashi littafai za ki makaranta gidan uban wa kuka je?" Ta yi musu tambayar cikinn tsare ido.
Mamaki ya kama su duka musamman shi da yake tunanin wa ya gaya mata.
"Ummu kar ki yi zargi babu inda muka je kuma ni ba ƙarya na yi miki ba, da gaske tare muka fita da shi."
"Ok Hamsiya ƙarya ta yi maka da ta ganta ta yi parking ka shiga cikin motarta ko?"
Zare ido ya yi don ba shi da bakin magana, amma da ya tuna umurnin da ya ɓata, kar faruwar hakan ya sa ta ƙi bin umurninsa domin so yake ta saki da shi ya koya mata sonshi yadda babu wanda ya isa ya raba su.
"Eh, dama ita za ta rage mini hanya kuma abin da ya sa ban gaya miki ba, sam ba kya son kusantarmu da ita, wanda ban san dalili ba."
"Dalili kake nema na ga ko cewa na yi ba za ka fita ba, dole ka yadda tun da ni na haife ku?" Ta ce cikin zafi.
Abu da ya ji hayaniya daga sama ya saukkowa da sauri tare da ƙarasawa gurinta ya kama hannunta.
"Kai Huwais, tafi inda za ka. Hilah je ki yi wanka kici abinci." Ya basu umurni wanda ya sa suka juya suka fita.
"Ke kuma muje ciki ina son magana dake."
"Ni ma maganar nake son mu yi." Ta ce tare da juya babu musu ta haye sama ranta na tuƙiƙi.
Da ya shigo ya same ta a tsaye sai safa da marwa take yi. Hannunta ya kama tare da ƙarasawa da ita gaban frij ya ɗauko ruwa mai sanyi ya zuba a cup, ya miƙa mata wanda babu musu ta karɓa ta shanye.
"Kina zafafa wa yarannan! Ki tsani tun ka ba sa tunanin wani abu sai su yi zargi bayan babu komai a ransu illa shaƙuwa ta jini."
"Kai ne idanunka ya rufe kake ganin haka, amma ni na san mai nake ganin yaronnan a zuciyarsa. Ba ka san wane ne Huwais, ba ne shi ya sa kace haka, amma ni na haife shi na san abin da yake so da wanda baya so."
Ta yi shiru ko zai ce wani abu, amma sai ta ga bai ce komai ba wanda ya bata damar ɗorawa da ce,
"A lokacin da ya ji Hammad na sonta kamar zai yi hauka, wai ta fi ƙarfin shi kuma shi yake so ya zaɓa mata miji, amma a wannan ka ji ya yi ƙorafi? Ka na dai sane da irin haukan da yake nuna wa duk wanda ya bayyana soyayyarsa gareta, amma wannan ƙorafin me ya yi? Babu hankalinsa kwance har shawara yake bata. Na tabbata da ace babu sa hannunsa da yanzu ya tada hankalinsa. ko da ace ita babu komai kuma ba ta gane ba shi sonta yake."
"Don Allah ki daina wannnn haukar tunanin ta yaya za a yi ya so yar uwarsa wacce suka fito ciki ɗaya? Kawai shaƙuwar jini ne, amma babu wani soyayya tunanin ku ne na manta na rashin hankali." Ya faɗa cikin ɓacin rai yana kallonta.
"Humh ba za ka gane ba kamar yadda ba na fatan lokacin da zai ganar da kai hakan, amma mafita ita ce kawai ayi musu aure. Hankalina zai fi kwanciya tun dama shi Wajnaah tana nan tana jiransa har ta gama servise don kamar ta samu aiki ba ta fara zuwa bane.."
"Ni ma tunanina hakan, amma shi kawai ita sai ta gama karatun don ba zan yi mata aure tana karatu ba, duka guda nawa take."
"Ko shi ɗin ne a fara masa hankalina zai fi kwanciya." Ta ce tana yarfar da hannunta cikin rashin dubara, yayin da zufa ke keto mata.
"Kwanta ki huta zan yi mishi magana na ji ra'ayinsa sannan zan yi wa mahaifinta magana."
"Kan me za a ji ra'ayinsa uzurin da ya bayar ai ya je kuma ya dawo. Yarinyar ma ta yi haƙuri, duk da tarin masoyanta ta zauna ta jira shi har na tsawon shekaru biyu, ai ta yi masa halacci in ba butulci xai yi mata ba." Ta ce tare da kwantawa kamar yadda ya bata umurni.
Kamar yadda ya bata shawara sai ta ƙi yi har aka yi kwana uku duk da tarin tsaƙon da mahaukacin masoyi ke tura mata, amma da ta tuna ko don ta fita da ga zargin Ummu da take ganin kamar ta san mutumin ɓoyewa ta ke yi, sai ta saka a ranta gara ta yadda ta yaudare shi don ya bayyana kansa.
Ta fara kula shi da kalamai mai daɗi har ta sanar mishi da tana son shi wanda ya yi dariya da stikers tare da nuna farincikin sa ya ce,
"Jikina na bani kamar bakya sona kin amince ne don na bayyana kaina, amma ki sani ina da hankali da wayau, domin a iya sonki kawai na haukace don haka zan gwada soyayyarki na ga mizaninta."
Tun daga ranar bai ƙara yi mata magana wanda har aka kwashe sawon sati biyu.
Tun ba ta damuwa har ta fara shiga, sai ya zamana kullum cikin tunanin yaushe zai kira to ko ya daina sonta ne, in kuma haka ne kan wane dalili zai sanya ta fara tunaninsa sannan ya fita daga rayuwarta.
Ire-ire waɗanɗan tarin tambayoyin suke damunta kullum wanda ta rasa amsarsu.
Zaune take ta rafka uban tagumi hannu biyu-biyu. Idanunta cike fal da hawaye.
Kamar dai kullum tunanin mahaukacin masoyi take yi. Bayan haukarsa ta lura mutum ne mai izza da girman kai. Domin a tarihin rayuwarta ba ta taɓa yi wa wani magana ba ya gani, amma babu reply. Sai ga shi yau ta yi duk kimarta da ji take ita ma wata ce. Ya ga messeges ɗinta amma bai duba ba.
"Anya ma yana sona?" Ta yi wa kanta tambayar tare da miƙewa ta fara taku a ɗakin.
Tabbas a ranar musabaƙarsu ta yi tunanin ya shigo rayuwarta ne don kar ya barta ta yi nasara, amma bayan ta dawo ya kawo mata kyauta sai wannan tunanin na ta ya kau.
"Ƙanwata!"Ta ji muryar Ya Huwais da ya ƙaraso har cikin ɗakinta tare da rufe mata fuska.
Ɗan murmushi ta yi wanda iya kansa saman leɓenta. Da hannunta tasa ta kamo hannunsa ta jawo shi gabanta.
"Ya Huwais ka yi kyau matuƙa! Ina zuwa haka?" Ta ce masa tare da tambayarsa.
Ba tare da ya amsa mata tambayar ba ya zauna a gabanta tare da kama hannunta ya rungume a kirjinsa yana jin kamar ita ya rungume, wanda ya sanya ta maza ta janye hannun.
"Ina tsoron Ummu domin mundin muka ƙara shiga hannunta ba za ta yi mana da sausauci, don a wancan ranar Abu ya ce ce mu. Kuma ina zargin ta saka Hamsiya ta rinƙa spying ɗinmu"
Kallonta ya yi cikin tausayawa. Ummu ta fita dubiya ita da Abidin dalilin da ya sa nazo kenan."
Jin abin da ya ce ya sa ta saki ranta ta na yaƙe masa baki.
"Meke damunki? Na lura kwana biyu ba kya magana, duk da cewar ba ki da yawan magana, amma shuru-shurun ya yi yawa."
"Babu komai." Ta ba shi amsa tare da raurau da idanunta sai hawaye.
"Wai ke baki da hanyar da za ki sanar ma mutum kina cilin damuwa sai kuka?" Ya yi mata tambayar cikin takaici ganin hawayen sun ci gaba da zuba.
TUNATARWA
Shin kina daga cikin matan da karatun Novels yake ɗauke musu hankali suke barin sallah ta wuce su? Ko kina daga cikin masu daina karanta Kur'ani ko azkar duk saboda karatun Novels? Don Allah yar'uwata musulma ki daina barin sallolinki na wuce ki saboda karatun litattafai Hausa, saboda ko mu MARUBUTA da muke yin typing da zarar lokacin sallah ya yi muke tashi mu yi sallah. A kiyaye da ibadu musamman sallah saboda ita ce farko da za a fara dubawa a cikin ayyukan mu. Da fatan za ki ji kuma ki hankalta. Fatanmu mu gudu kuma mu tsira tare. Allah ya bamu ikon aikatawa Amin. Taku Jamila lawal Zango.
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LQfVU1ABdFI14btWRhUB1K
*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kwacakwan labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 7
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
"Wai ke baki da hanyar da za ki sanar ma mutum kina cikin damuwa sai kuka?" Ya yi mata tambayar cikin takaici ganin hawayen sun ci gabaa da zuba.
Ƙoƙarin sharewa ta yi tare da kallonsa da yake tsaye shi ma ita yake kallo.
"Kin san fa ba kya ƙarya wannan dalilin ya sa da kin yi nake gano ki, ko a yarinyatarki." Ya ce mata wanda ya sa buɗe baki za ta gaya masa haskiyar damuwarta.
"Mahaukacin masoyi ya daina kir..." Maganar ta maƙale mata sakamakon wani birkitaccen kallo da ya yi mata.
"To kuma kan me za ki damu kanki don ya daina saboda dama neman hanyar rabuwa muke yi da shi, cikin sauƙi kuma ya kori kansa? Ni banga dalilin damuwar hakan ba." Ya faɗa ransa a ɓace.
"Ni ma haka nake gani, amma ban san dalilin da ya sa zuciyata ta damu da hakan ba, domin sati biyun sa bamu waya sai na ke jin na kasa sukuni. Duniyar ta yi mini zafi." Ta ba shi amsa cikin wauta wanda hakan ya sa ya yi sororo yana kallonta.
"To kan me za ki yi tunaninsa na ga kina da wanda kike so? Ke da bakinki kin gaya mini ba ki da ra'ayi akansa?"
"Eh, haka nace. Ni ma haushin zuciyata na ke ji a bisa abin da ta bijiro mini da shi."
"To wannan ba damuwa bane, kuma da yau kar na ƙara ganin kin saka kanki damuwa, domin kamar kin tsose ƙwallon mangwaro ne kin huta da ƙuda."
"Har yanzu ka kasa fahimta ta Yaya, na gaya maka zuciyata ta aminta da shi."
Kallonta ya yi kamar na baki da hankali tare da zare idonsa.
"What! Mai kika ce? Kin ko san girman abin da kika saka kanki a ciki? Ni fa cewa na yi ki nuna masa soyayyar ƙarya, don mu gane wanda yake wasa da hankalinki amma ban ce ki aminta da shi ba, domin in har bai bayyana kansa ba bani da hanyar nemo miki shi." Ya faɗa yana kallonta da mamaki tare da kishi sosai a ransa ganin haka take da sauƙi da yawa, don ya ɗauka zai sha wuya sosai. To in da kuma ba shi bane shi ke nan ya rasa ta kenan.
"Ba laifina bane laifin zuciyata ce. Kuma in har za ka iya ganin laifina tabbas za ka iya ganin laifin jaririn da ya faɗo duniya a mace."
"Humh." Ya ce don ya rasa bakin magana sai kallonta yake yi.
"Yanzu to mene ne abin yi?" Ya tambayeta cikin rashin dubura.
"Ni ma ban sani ba kuma na ga kai ka ga kawo sharawar." Ta ce tana watsa hannunta.
"Mu bar maganar yanzu ma za ta shi ki haɗa mini abincina ki bawa wannan munafukar ta kai mini ɗaki."
Duk halin da take ciki sai da ta murmusa."Ba ita ta kashe zomonn ba, rataya aka ba ta. Tun tana yarinya Ummu ta ɗauko ta. Cinta da shanta duka kanta yake, idan ba ta yi mata biyayya ba ta butulce."
"Duk da haka zan yi maganinta."Ya ce yana danna wayarsa.
Da ta fita sai ya bita da kallon mamaki yana jin sam bai kyauta mata ba.
Ko da ta dawo zama ya yi, ya rinƙa kwantar mata da hankali da ƙarfafa mata gwuiwar mahaukacin masoyi zai dawo.
"Damuwata ya hana ni numbar da xan kira na ji ko da wani abu ne ke damunsa, sannan na yi masa magana ba zai kula ni ba kuma alamun ya gani."
Da ƙyar ya samu ya rararsheta har ta daina kukan.
Da fari ta jure amma daga baya sai ta ji ta kasa ta koma ruwa. Abin duniya ya haɗu ya yi mata yawa. Ga exam da zata fara saura kwana biyu.
Lokaci guda ta rame ta fice hayyacinta ko abincin kirki ba ta ci. Ta zama tamkar amarya, don ko fitowar da take yi su yi hira da daddare ta daina.
Ganin halin da ta tsira sai suka fara ƙorafi musamman Umnaah wanda hakan ba ƙaramin takurara ya yi ba, domon suna matuƙar son junansu. Amnaah ƙaracin shekaru bai saka ta gane ba, sai dai ƙorafi da take mata ta daina mata wasa. Dama ita Azerh cele ce ba ta damu da rayuwar kowa ba daga kallo dai chatting.
Ganin hakan su Abidin suka tuntuɓi Yayan na su tare da tsare shi da tambayoyi.
Take ya ji babu daɗi ganin a dalilin biyewa muradin zuciyarsa ya ɓata farincikin kowa.
"Ni fa ina zargin patiality da Ummu ke nuna wane ya fara damunta. Which isn't good at all, domin ina agains ita dukanninmu ita ta haife mu." Cewar Naufal.
"Don Allah Ya Huwais, ka yi mata magana domin duk mun yi mata, amma