Author : Jamsy Category : Complete Novels
Ya furta cikin ɓacin rai xai fice.
Wani irin ƙara ta saki saki ta ruga da gudu cikin ɗakinta.
Tsaki ya ja yana kallonta."Wawiya kawai!" Ya furta sannan ya murɗa ƙofa ya fice.
A hanya tafe yake yana tsaƙa da warwara. Gani yake sam iyayensa ba su yi masa adalci ba, amma kuma in ya tuna lamarin da yake shirin ibo ma kasa sai ya ji damuwa sosai.
Shi kansa ya sani ihu yake bayan hari. Ko da ace ba a yi wa Hilah aure ba, ba shi da damar da xai bayyana yana sonta.
Wayarsa ya ɗauka da ya sanya a caji. Numbar Hilah ya nemo sannan ya danna kira.
Hilah da ta fito daga lectured kenan suna tafiya da Affrin za su je Cafateria.
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 08144072423
'*RANAR WANKA...*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMCY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
SADAUKARWA
Kacokam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga ƙawata sahibata Aysha Na Lado. Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.
PAGE 24
Jin wayarta na ringing, ya sanya ta buɗe jakarta ta ɗauko.
Ganin Huwais ne, sai ta tsaya tare da danna gurin kiran, ta kanga ta a kunni.
"Hello Yayana." Ta furta da muryarta da ya bayyana, tsantsar gajiyar da take ciki.
Jin muryarta ya sanya shi rintse idanunsa, yana jin wani abu yana yawo a kwanyarsa.
"Hilaaah, kina ina?" Ya yi mata tambayar tare da jan sunanta.
"Ina school mun gama lectured zan nemi abinci."
"Ok, ki yi ma za ki ci abincin zan jira ki a bakin get ina kan hanyar makarantarku."
Daɗi ta ji a ranta sosai, dama tuntuni take son ya sanar mata da ranar da za su huɗu.
"Ok, sai ka zo amma Yaya lafiya kake?"
"Lafiya lau." Ya ce mata tare da kashe wayar yana sauke numfashi.
Bin wayar ta yi da idanu, tamkar za ta ga abin da ke damunsa a wayar.
"Ya Huwais, ne ya kira ni yana kan hanyar zuwa makarantarmu. Mu yi sauri na mu ci abincin kafin yazo."
"Yayanki yana matuƙar ji dake. Ina ma ace ni ce na samu wannan gatar. Na ɗauka zai canza in ya yi aure, amma abin gaba ya ci."
Dariya ta yi jin abin da ta ce."Wannan dalilin ya sa na ke son shi sosai."
Suna gama cin abincin kenan, ya kira wayarta tare da sanar mata da ya iso.
"Tashi mu je kar na barshi jira."
"Ki dai je in har kuna tare mantawa muke da kowa."
"To shikenan, tun da ba za ki je ba." Ta ce tana dariya.
A hankali take takunta cikin natsuwa kanta a ƙasa. Yana tsaye ya hangonta. Gyara tsayuwarsa ya yi, tare da zuba mata idanu, tamkar zai cinyeta har ta ƙaraso tana masa murmushi.
"Yayana," Ta ce tana kallonsa.
Yanayin fuskarta ya canza hannunsa ta kamo.
"Lafiya Ya Huwais?" Ta yi masa tambayar cikin damuwa.
"Mu samu guri za mu yi magana." Ya ce mata tare sakin hannunta.
Babu musu ta shiga gaban motar ya ja suka fara tafiya. Sun yi nisa sosai, babu wanda ya yi magana, sai ita da take satan kallonshi cikin damuwa.
Ajiyar zuciya ya saki mai ƙarfi wanda ya sanya ta kalle shi.
"Yayana, mai ke faruwa? Na damu da halin da kake ciki."
Bai ce mata komai ba, sai da ya yi parking sannan ya fito. Ganin haka ya sanya ta buɗe ƙofar ta fito.
Gurin wasu fararen kujeru suka samu suka zauna.
Kimanin ƴan sakanni sun zauna babu mai cewa komai.
"Hilah Abu ya gaya mini xai sanar da iyayen Hamad su kawo kuɗin aurenki."
Ras! Ta ji gabanta ya yi matuƙar faɗi. Miƙewa ta yi, yayin da hawaye ya wanke mata fuska.
Ganin razanar da ta yi ya sanya shi jin sanyi. Hannunta ya kamo ya xaunar da ita.
"Kina son Hamad?" Ya yi mata tambayar yana kallon ƙwayar idanunta.
Kallon da yake mata ya sa ta ji wani irin nauyi. Domin kalar idanun da ya canza ba ta taɓa hango hakan a ƙwayar idanunsa ba.
"Bana sonsa, amma kuma matuƙar xan samu saɓani da Ummu kan auren ba ni da xaɓi." Ta faɗi haka cikin rawar murya.
Ransa ya ɓace jin abin da ta ce."Kenan za ki sadaukar da kanki saboda farincikin Ummu? Karki manta rayuwar aure ana samun natsuwa ne, in har mutum ya auri xaɓin rayuwarsa. Ki duba halin da nake ciki tun da aka ɗaura mini aure ban samu kwanciyar hankali ba."
"Ya zan yi Ya Huwais? Ka san halin Ummu, ko soyayyarsa ita ta sanya na amince har na yarda da zan aure shi."
"Shikenan kin haƙura da mahaukacin masoyinki?"
Ɗago idanunta ta yi da sauri jin sunan da ya kira.
"Zan iya haƙura da shi tun da bai damu da ni ba. Zan yi wa Ummu biyayya na san cewa ba zan taɓa taɓewa. Mahaukacin masoyi ya cuce ni ya yaudare ni. Auren da zan yi shine kawai zan baƙanta masa rai. Ya san cewa ban rasa masoya ba. Hamad yana da nagarta kum...."
"Ya ishe ni! Ban zo nan don ki gaya mini nagartar sa ba." Ya katseta cikin fushi yana huci.
Shiru ta yi tana kallonsa tare da share hawaye.
Miƙewa ya yi, ya fara taku sai kuma ya tsaya ya juya mata baya.
"Na san wane ne mahaukacin masoy..."
"What!" Ta furta cikin tsananin razana tana kallonsa.
Yadda ta ruɗe ya firgita shi. Kama hannunta ya yi ganin ta fara kuka.
"Please, ki zauna mu yi magana na fahimta."
Zama ta yi hawayen na bin ƙuncinta."Haba Yaya, da kai xa a haɗa baki a ruguza farincikina. Dama ka san mahaukacin masoyi ya rinƙa wasa da rayuwata? Haba Yaya! Sam ban yi taɓa tunanin zaka yi mini haka ba why?" Ta ƙarashe maganar tana gurzar kuka.
Huwais ya yi shiru cikin tashin hankali yana kallonta. Irin tashin hankalin da ta nuna ya sanya shi ƙara shiga cikin damuwa sosai.
A koda yaushe gani yake tana ƙara son mahaukacin masoyi. Shin idan ta ji shine za ta so shi kamar haka?" Tambayar ya sanya cikin shi murɗawa.
"Mai ya sa aka haɗa baki aka cutar da ni?" Ta ƙara cewa ganin ya yi shiru.
"Waye shi? Waye wannan mugun azzalimi wanda ya yaudare ni? Na zaƙu da na san ko waye na ɗauki hukunci mai zafi a kansa.".
Miyau ya haɗiye da ƙyar, yana jin yadda maƙoshinsa ya bushe, babu ɗigon miyau.
"Yaya Huwais ka gaya mini wane ne?" Ta ce tana girgiza shi.
"Zan gaya miki, amma ki natsu mu yi magana ta fahimta." Ya ce bayan ya mayar da ita inda ta xauna.
Zama ta yi tana share hawayen da yake xubo mata.
"Tabbas Hilah na san shi. Abokina ne kuma yana matuƙar sonki. Saboda kyawunki da matsalar da yake hango ya kasa bayyana miki soyayyarsa. Saboda yana da hankali kuma ya dace dake shi ya sa na ƙyale shi, ya fito miki a matsayin mahuakacin masoyi don ya samu soyayyarki ya sanya ki bijire auren Hamad."
"Amma mai ya sa ya kasa bayyana kansa a gareni? Mai ya sa ya yi mini alƙawarin xamu haɗu ya ƙi zuwa?"
"Kamar yadda ya gaya miki, mahaifiyarsa babu lafiya za a yi mata aiki a ranar kuma zai sanya hannu."
"Saboda me ya kasa bayyana mini domin zan fahimce shi. Wannan ba hujja bace mai ƙarfi. In har zan iya yafe masa saboda kai ne, da kai ne don na san ba za ka taɓa yadda a haɗa baki a cuce ni ba."
Rintse idanunsa ya yi yana jin babu daɗi jin abin da ta ce.
"Ki yafe mini Hilah ba ni da zaɓin da ya wuce na samu soyayyarki ta haka."
"Na san duk abokananka don Allah ka gaya mini wanne ne daga ciki."
"Ba ki san shi ba Hilah, kamar sau ɗaya ya ganki a taron da kuka yi na musabaƙa tun daga ranar ya nuna yana sonki. Na ba shi shawarar ya fito miki ta wannan tsigar, saboda na san yana bayyana kansa za a dakatar da shi."
"Don Allah ka nuna mini hoton shi." Ta ce cikin zaƙuwa.
"Ba zai yiwu ba saboda ya roƙe ni kar na nuna miki."
Ɓata ranta ta yi jin abin da ya ce." To ya kamanninsa yake?"
"Shin idan kika samu miji mai irin surata da halina ya za ki ji?"
"Zan yi farinciki saboda samun miji kamarka, sai macen da Allah ya yi mata tagomashi. Shi yasa kullum na ke ganin Anty Wajnah a mace mafi sa'a da ta same ka."
Jin abin da ta faɗa kansa ya fasu. Ji ya yi kamar ƙasa ba za ta iya ɗaukarsa ba.
"To ki ayyana surarsa da haliinsa kamar ni, amma kuma ni na fi shi sonki." Ya ce cikin murmushi.
Dariya ta yi cikin farinciki."Aiko na samu mijin aure in har kamanka yake."
"Ba ki da kunya Hilah a gabana kike wannan murnar ko?"
Rufe fuskarta ta yi tana dariya."Amma abokin nan na ka ya cutar da xuciyata."
'Ki yi haƙuri xai bayyana kansa ba da jimawa ba. Yanzu wane shawara kika yanke game da auren Hamad."
"Zan fito fili na gaya wa su Ummu akwai wanda na ke so."
Gabansa ne ya faɗi tuna in har aka ce ta kawo shi ya xai yi.
"Yauwa ƙanwata, karki bari Ummu su yi miki auren dole kamar yadda aka yi mini."
Yadda ya yi maganar ya ba ta dariya."Ya Huwais, ka amshi Anty Wajnah a matsayin mata ku zauna lafiya. In Allah ya sa wacce kake so matarka ne sai ka aureta."
"Ba za ki gane yadda zuciya take ƙuntata ba, yayin da mutum ke zama da abin da ba ka so."
"Na fahimta, amma ka yi mata adalci ko don zumuncin da ke tsakaninku."
Shiru kawai ya yi, bai ce mata komai ba sai ya nisa ya ce,"Ki rinƙa ɗaukar kiransa, kuma ku koma kamar da in sha Allah zai bayyana kansa a lokacin da ya kamata."
"To Yaya." Ta faɗa tare da miƙewa ta maƙala jakarta, ganin shi ma ya ɗauki wayarsa ya miƙe.
Tafiya suka fara yi har suka isa mota suna hira. Daga nan makaranta ya ije ta hankalinsa ya ɗan kwanta, ganin yadda take matuƙar ƙaunarsa, ya san ba za ta yadda ayi mata auren dole ba.
Wajnah kuwa bayan ta shiga cikin ɗaki tana kuka, wayarta ta ɗauka tare da danna kiran numbar Mommy, ta zayyane mata ƙarya har da gaskiya.
Ranta ne ya ɓaci sosai ta shiga rarrashinta.
"Ki kwantar da hankalinki yanzu zan kira mahaifiyarshi, don ba xan lamunta ya rinƙa dukanki ba, daga yin aure ai ba jaka na auro masa ba."
Bayan ta kashe wayar cikin fushi ta danna layin Ummu ta zayyane mata.
Matuƙar mamakin marin da ya yi mta ya kamata.
"Ki yi haƙuri kin barni da shi xai gane ba shi da wayo."
Tana gama waya da mommy ta kashe wayar tare da neman layinsa.
A lokacin da ta kira, yana kan hanyar dawowa da ga makarantar su Hila. Ganin kiran gabansa ya faɗi amma ya daure ya ɗauka.
"Huwais, ashe ba ka da hankali? Amaryar da ko sati ba ta rufa a gidanka ba za ka dake ta."
Ransa ya ɓaci jin abin da ta ce."Umm.."
"Ma za ka zo gida ina nemanka." Ta furta cikin ɓacin rai tare da daƙile wayar.
Wayar ya bi da kallo cikin ɓacin rai, yana tunanin abin da zai yi mata don ba zai lamunta, ta rinƙa haɗa shi da Ummu ba.
Juya motar ya yi zuwa gida. A falo ya same ta, zaune ta haɗe girar sama da ƙasa tun da ta ji shigowar motarsa.
Ganin yadda ta sha kunu, ta amsa sallamar ba tare da ta kalle shi ba, ya sanya gabansa ya faɗi.
Zama ya yi cikin sanyi jiki tare da gyaran murya ya ce,"Ummu ga..."
"Ashe ba ka da hankali? Kan me za ka daki Wajnah?" Ta katse shi cikin ɓacin rai tana faɗin haka.
"Ummu, k..."
"Ba ka da hujjar da za ka kare kanka da shi. Kuma ka ji na rantse maka wannan ya xama na farko na ƙarshe da za ka kai hannunka jikinta. Sannan a matsayina na mahaifiyarka, ina umurtarka da ka karɓe ta a matsayin mata ka sauke duk haƙƙinda ke kanka, matuƙar ka ƙi yin hakan za ka fuskanci fushi mai tsanani. Kan auren nan matuƙar ba ka cire banzar tunanin da kake yi ba, kun zauna lafiya zan iya maka mummunar lafazi, domin ba zan bari a cikin dangina ana yamaɗiɗi da ni, cewar ban isa da ɗan cikina da na haifa ba"
Kansa ya ɗago da sauri cikin tashin hankali jin hukuncin da ta yanke.
"Amma Ummu sam ba a yi mini adalci ba na gaya miki bana..."
"Ai bakin alƙalami ya bushe, tun da aka ɗaura aurenku, ba ka da wani xaɓi da ya wuce ka zauna da ita."
Miƙewa ya yi, cikin damuwa xai fice sai ya ji ta kira sunanshi.
"Huwais, wannan ya xama magana ta ƙarshe kan aurenka. Kar na ji kuma kar ta ƙara kawo mini ƙararka."
Ƙarashe ficewa ya yi cikin ɓacin rai zuciyarsa na tafasa.
A hanya tafe yake, yana tunanin abin da Hilah ta gaya masa. Tabbas Allah ya ba shi damar da xai iya auren mata har huɗu, amma ba ya jin zai iya karɓar Wajnah a matsayin mata. Kalaman da Ummu ta gaya masa, suka ƙara rikita ƙwaƙwalwarsa har ya gaza tunanin mafita.
A lokacin da ya isa gida. Ƙarasa shiga cikin dakin yana huci tamkar mesa."Da ma kin aure ni ne don ki haɗa ni da iyayena?" Ya yi mata tambayar cikin fushi yana tsaye a kanta.
Raurau ta yi da idanunta tana kallonsa."Don Allah kar ka yi mini mummunar fahimta, wallahi ina sonka Ya Huwais."
"Ki ji daɗi kin haɗa ni da mahaifiyata. Ki sani ko zan zauna da ke bisa umurnin mahaifiyata ce, amma bana sonki kuma babu soyayyarki a zuciyata."
Miƙewa ta yi, cikin sanyin jiki tana jin ɗacin kalmar bana sonki, da yake gaya mata.
"In har na ci albarkacin Ummu, zan yi farinciki na sam watarana za ka so ni."
"Kin yaudari kanki domin ba zan taɓa ƙaunarki ba." Ya ce tare da wucewa fuu zuwa ɗakinsa.
Jaɓar ta xauna kan kujera, tana jin babu daɗi yadda yake gaya mata ya tsaneta. Hawayen da ke zuba a ƙuncinta, ta share tare da miƙewa zuwa ɗakinta.
Wayarta ta fara ƙara alamun ana kira. Ganin kirar Ummu ce ya sanya ta ɗauka da sauri ta shige cikin ɗakinta.
Bayan ta ɗauki wayar ta yi sallama ta gaishe ta.
"Ki na jina Wajnah? Dole sai kin yi haƙuri tun da kin san dole aka yi masa. Ki daina rashin kunyar da kike masa sannan ki zama mai biyayya, cikin sauƙi za ki mallake shi a hannunki. Ita wacce yake son hauka yake yi, saboda ko mutuwa zau yi don sonta ba zai aureta ba."
Mamaki ya kamata, domin ba ta taɓa sanin Ummu ta san wacce yake so ba.
Ajiyar zuciya ta yi jin abin da ta ce take hankalinta ya kwanta.
"Ba ya cin abincina kulle ɗakinsa yake yi da na shiga yake koro ni." Ta ƙarashe maganar cikin kuka.
"Kar ki damu ki yi masa girkin, kuma ki shirya kinje ɗakinsa, na yi masa mummunar lafazi matuƙar ya ƙi kula ki."
Zuciyarta fes ta rinƙa murna tana gode wa Ummu.
"Duk abin da xai yi miki karki kula shi ki yi masa biyayya kin ji?"
"To Ummu," Ta ce tare da kashe wayar tana tsallen murna.
Miƙewa ta yi cikin farinciki, ta shiga kicin ɗin, tana kallon ƙaton kicin da aka cika shinda kaya.
Tunanin abin da za ta girka masa ta yi. Buɗe frij ta yi ta ɗauko naman kaza ta kunna famfo don ta saki.
Cikin farinciki take yi masa tuwon shinkafa da miyar taushe. Bayan ta kammala ta koma ta dafa masa farfesun kan rago.
Ɗaki ta koma ta yi wanka ta sanya kaya masu kyau.
A lokacin da ta fito falo shi kuma ya fito don ya je sallar isha'i. Kallonsa ta yi cikin shauƙin ƙauna tana wani tafiya tana yauƙi.
Ko inda take bai kalla ba ya wuce zuwa massalaci. Ganin haka ita ta miƙe cikin gaggawa ta yi nata sallar sannan ta fito tana jiran dawowarsa.
Bayan an idar da sallar zama ya yi, yana tunanin umurnin da Ummu ta yi masa, domin bai san ta yadda xai ɗauke ta a matsayin matarsa ba.
Mace ɗaya kawai yake so kuma yake burin ya yi rayuwar aure da ita. Ita ce wacce yake ganin duk ji da kansa da yake yi, zai xama bawa matuƙar xai mallaki zuciyarta, amma kuma ba zai iya bijirewa umurnin Ummu ba.
Miƙewa ya yi, ya kulle masallacin sannan ya shigo cikin gidan. Zuciyarsa na yi masa nasihar ya bi umurnin mahaifiyarsa.
Jin alamun buɗe ƙofa, ya sa ta miƙe da sauri ta ƙarasa gurin ƙofar don ta buɗe masa, dama ta kulle ƙofar saboda ta san lokacin da xai shigo.
Buɗe ƙofar ta yi da murmushi a fuskarta."Barka da dawowa farincikin rayuwata." Ta faɗa cikin wani irin murya yayin da ta matsa kusa dashi kamar xa ta rungume shi.
Karo na farko ya yi mata kallon tsanaki, domin tun lokacin da ta fara nuna maitarta a fili ya ji babu wacce ya tsana fiye da ita, kuma tun daga lokacin bai ƙara yi mata kallon da xai gane yadda take ba.
Ganin ya kalleta ya sanya ta ƙara matsowa kamar xa ta shiga jikinsa.
Ya buɗe baki da nufin ya magana, amma sai ya ji ya gaza furta kalami.
Wucewa ciki ya yi, ba tare da ya ce mata komai ba, wanda ganin