MAI DAKI BOOK 1 HAUSA NOVELS BY SODANGI.docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   7 / 7

18K to 19.3K   out of 19.3K words

ce, "Uhm, Allah dai ya samu a

124

danshinku. Na ce, To Amin. Kin san

kuwa ban taba tunanin zuwanki ba.

Ta ce, Yaushe kuwa za ki yi tunanin

zuwana? Ai ke kam Hauwa'u ba ki da

kirki, daga kin yi aure sai ki ki mutane?

Na ce, Ayya, ba na samun fita ne. Ta

ce, Eh ai ban ga laifinki ba ko kadan ko ni

nayi aure na samu wadata haka ina za ni?

Ai sai kawai nayi zamana na yi ta shan

gara.

Na mike don kawowa Sadiya abinci da

kayan shaye-shaye da ciye-ciye saboda

hirar tata ba wani dadi take yi mun ba.

Don nasan Ishak yana jinta. Tana nufin

kenan don ka samu gidan miji mai wadata

shi kenan babu ruwanka da sauran

mutane?

Yan uwanka, 1yayenka da abokan

arziki. Idan kuma ya zamana shi ba shi da

lokacinka kamar Ishak fa? Sai ka yi ta

rayuwa kai kadai takamar ya wadataka'

125

Lalura kuma idan ta same ka fa? Na

debo abinda zan kawo mata na ajiye a

gabanta tana tambayana maigidan yana

nan ne?

Na ce, Eh yana barci. Na mike na shiga

dakin Ishak na zauna kusa da inda ya ajiye

kanshi don nayi maganar da zan yi a

hankali.

Na ce, Za kủ gaisa ne? bai ce mun

komai ba har na gaji da zamana na fito na

dawo falo muka ci gaba da hirar mu.

Na ce, Sadiya ya Makaranta? Ta ce, Ga

mu nan mun usa gamawa muna ta shirin

zana jarrabawa, Malam Ali kuwa kullum

sai ya tambaye ki.

Na ce, To da yake tambayata ai sai ki ce

mishi iyayena sun dauki shawarar da

kullum yake ba su sun kuma aurar da ni.

Tayi dariya, Ke Malam Ali fa

shakiyanci kawai yake yi miki. Amma ke

kin zauna kenan ba za ki koma Makaranta

ba?

126

Ke kina ganin hakan ya yi miki daidai?

Yanzu fa watan gobe ne za mu rubuta

jarrabawa kowa kuma sai ya kama

gabanshi a yi ta tafiya babu ke.

Karatu ai shi ne adon mace a duk

lokacin kuma da ta rasa shi to tayi babbar

asara, don kuwa ko aure ki ke yi ai ba kin

rinka zama ke kadai ba kenan wata rana za

a yi miki kishiya ki ka san wacce za a auro

miki?

Na yi nufin katse Sadiya na ce, Ke

Sadiya bar wannan maganar haka muyi

wata kuma. Na dauko wata hirar ina

tambayarta, Ni kuwa ina Zubaida?

Ta tabe baki ta ce, Uhum, tayi aure ita

ma har ma ta haihu ai tsiranku babu yawa.

Kema dai da alama cikin ne da ke tunda

gashi nan har ya fito.

Aini kam yanzu idan nayi aure family

planning zan yi kafin na gama karatuna

sannan na fara haihuwa. Na ce To idan

mijin naki bai yarda da hakan ba fa?

127

Ta ce, To yaushe dama zan sanar da shi,

ai tuni zan je nayi abina bai ma san lokacin

ba.

Ke! Cikin saurina waiwaya Ishak ne a

tsaye cikin wani irin bacin rai. "Tashi ki

fita a gidan nan."

Sadiya ta fara kokarin gaishe shi,

"Common get out, idiot! 'yan banzan yara

kawai marasa kunya."

Sadiya ta mike sum-sum-sum ta fita, ni

kuwa jikina sai bari yake yi ga kunya ga

takaici, "Ke kuma." Yana nuna ni da dan

yatsarshi "Ki kiyaye ni na gaya miki.

Ki san irin mutanen da za ki rinka kawo

mun gidana. Wanene Malam Ali?" Cikin

kuka na fara kokarin yi mishi bayani.

"Shut up dalla kiyi mun bayani. Na ce,

Malamin mune na Makaranta. "Menene

gaminki da shi da take yi miki maganar shi

iye?"

Taratsatsin bala'in da na gani a wajen

Ishak ranar ba kadan ba ne. Na lallaba na

128

hau gadona na kwanta, don kuwa na ga

da irin wadannan abubuwan.

Har hutunshi na sallah ya kare ya koma

bai yarda ya kai ni gida ba, wai a madadin

zuwan da nayi babu izininshi.

Yanzu kuwa kullum idan zai fita a gida

kullewa yake yi, ya yi tafiyarshi da nayi

mishi magana akan illar yin haka sai ya ce,

Idan ina da matsala nayi mishi waya ba zai

ji kuiyar zuwa ba, na ce To.

Don haka yanzu ni kadai ce nake wuni

a cikin gidan ko dan littattafan da nake

samu na daina.

A yanzu da nake cikin watanni na

takwas cikina ya bayyana sosai, kowa.

yana gani nima kuma ina matukar jin shi a

jikina, don kuwa abubuwa suna dan yi

mun wahala, kuma ba ni da mataimaki.

Shi kanshi Ishak ya lura da hakan,

amma ba zai iya hakura da halinshi ba.

Tashin da muka yi yau ba mai dadi ba ne a

wurina.

129

Don kuwa jikina yayi nauyi ba kadan

ba, da kyar nake motsawa. Ishak da kanshi

ya ce muje asibiti. Muna zaune gaban

Likita ya ce, Yaron a karkace yake

sakamakon da scanning dina ya bayar

kenan.

Don haka za a yi kokarin gyara mishi

kwanciya, don haka Ishak yaje gidanmu

ya sanar da Ummana, sannan ya dawo.

Ina zaune a bakin gadon dakin da aka

bani shi kuma yana zaune a kan kujera,

yanzu ya ya ki ke ganin zamu yi kenan

tunda dole naje wurin aiki, kina ganin ba

ki da wata matsala a kan hakan?

Na ce, Eh Umma zata zo ai. Ya ce, To

tunda haka ne bari na jira zuwanta kada a

bar ki ke kadai."

Sai washegari da safe ne aka yi mun

gyaran tare da kyakkyawan kashedin kada

na rinka aiki komai kankantarshi. Kwana

daya na kara a ka sallamo ni na dawo gida.

130

Da safe Ishak ne ya tashi ya hada mana

abin karyawa, ya share dakin gaba daya ya

shirya cikin sauri ya fita.

Na sha shayina na koma na kwanta,

wajen karfe daya sai ga dan aiken da ya

saba aikowa ya kawo mun abinci. Na bude

take a way ne na abinci mai kyan gaske."

Shinkafa fried rice da sálad da kuma

kwatan kaza. Da yamma kirana ya yi yana

tambayata abinda zai taho mun da shi, na

ce ni a koshe nake zan sha tea.

Duk da hakan bai fasa kawo mun wani

irin gashi ba na bankararren kifi da aka

gasa da lemon tsami yayi mun dadi ba

kadan ba.

Don haka na ci sosai. A daren yayi "yan

aikace-aikacen da zai yi bai kwanta ba sai

wajen karfe goma da rabi saboda wankin

da yayi na under wcars din shi.

Sanin halayyar Ishak yasa nake ta jin

shakkun yi mishi magana akan shawarar

131

da. nayi aina, sai dai duk da hakan ban

fasa ba.s

Ina kwanoe & gefehshi na ce, Ko zan yi

wa Umha magand ne ta samo mana wacce

2amu rinka. żarňa tare runda ka ga ni ko

wannan aikin ma da ka ke yi ba kai ne ya

kamáta kayi ba.

Ya ce, Kin ji nayi miki wani kora a

kan hakan? Na ce, To naji ba ka yi ba

amma idan naæo haihuwa fa?

Ya ce, Sai ki bari idan haihuwar tazo

kiyi magana, ba zan tsaya na yi ta jayayya

dashi ba don haka naja bakina nayi shiru.

llai ko ba a fi sati guda ba bayannan sa

na tashi da wani irin ciwon mara ma

musaltuwa, nayi ta wani irin murkususu ni

kadai a daki, don kuwa Ishak baya nan bai

dawo daga wurin aiki ba...

To bari mu jira dawowar Ishak din

muma, sai in ce mu hadu a littafi na biyu.

Taku;

Haj. Hafsat C. Sodangi

130

7 / 7