Author : Hafsat C Sodangi Category : KDP NOVELS
na sauran kwanakin.
Don haka na shirya mishi abin karyawa.
Ya fara ci kenan ya kalle ni Na baki
mintina goma kI shirya na sauke ki a
gida."
Ban san sanda na fara godiya ba, duk da
cewar mintina goman ba 1sa na za su y ba.
Na riga nayi wanka don haka atamfata
na dauko Exclusive na daura da gyalenta
da set din takalmi da Jaka 'yan taly, sai
yan canji na da ba su fi Naira dubu daya
ba.
Da wasu yan abin kwalam da nake
ajiyewa idan ya kawo sun ban sha'awa na
karewa dakin kallo na rasa abinda zan
kaiwa Umma.
66
Don haka na bude akwatin aurena da
zannuwa suke ciki na dauko mai kyau na
fara nadewa ban san ya shigo ba ya ce
"Me za ki yi da ita? "
Na rasa abinda zan ce, ya ce To
mayar. Na sake budewa na mayar
gwiwata a sanyaye.
A kofar gida ya ajiye ni na shiga rabona
da gidanmu watanni biyar. Haka na Umma
da Babana. Gani na rinka yi kamar ba ni ba.
Haka nan Umma ta rinka ina ta ka saka
da ni. Ta zuba mun ido ko kyaftawa bata
yi. Ni kuwa kunya duk tà kama ni.
Farin ciki mai yawa Umma ta nuna na
ganina. Ita ma na ganta tayi kyan gani ba
kadan ba.
Na bude Jakata na ciro ma su Tasi'u
Bueno cakulet da biskit kwali biyu na
mika musu suna ta murna, wanda iyakacin
kuma abinda na riko nusu kenan.
67
Ni ce na tashi yau ma nayi mana girkin
rana muna ta yar hirar mu da Umma.
Wacce ganin irin murnar da take yi ne
yasa ni kasa gaya mata mnaganar da ke cina
a cikin raina.
Wato maganar Makarantata. Ba zai
yiwu na dakushe mata wannan farin cikin
da take ciki na ganina ba.
Karfe hudu da rabi daidai sai ga
sallamar dan aika wai na fito na dauko
gyalena na zo inda Ishak ke hakimce a
cikin mota na dan risina ta gefe na ce "Ai
na dauka zaka shigo ku gaisa da Umma ne
ko da ba za ka bar ni na jira dawowan
Babana ba."
Ya ce, A'a ba zan shiga ba, fito
kawai. Na ce, "To." Na koma na ciro "yar
Naira dari taran da nake ta nuku-nuku na
kasa bai wa Umma, na mikawa su Tasi'u
nayi wa Umma sallama na fito zuciyata
kamar ta fashe.
68
Muka iso gida ya ajiye ni ya juya, ni
kuma na shiga kicin da nufin dorà abincin
dare.
Tunani nake yi na yadda zan rinka
taimakon iyayena, don kuwa ba zai yiwu.
na zauna a haka ba. Ishak ba ya bani ko
sisi zan iya cewa tun bayan aurena a shi
sile biyar bata shiga tsakanina da shi ba.
Haka nan duk wani abu na amfanin gida
shi ke kawowa bani da wata hanya da zan
bi na samu kudi da zan iya yi musu wani
abu. Ya zama mun dole nasan abin yin.
Tun daga ranar da na samu matsala da
Ishak kan zuwana gidan su Hindu ban
sake ba, sai dai da yake ya daina kulle ni
bayan na roki yayi mun hakan, to ita takan
shigo.
Mafita daya ce shi ne na dan rinka
taimaka musu da dan abinda za su ci
wanda shi kam ina da shi, don haka da
Hindu ta shigo na roke ta ta gayawa
Mominsu ina son aikanta gidanmu.
69
Na debi shinkafa mudu biyar da su
Taliya da cous-cous, man gyadan (Turkey)
da soyayyen nama da sauran abubuwan
amfani na hada mata rigijif ta kai ta dawo.
ow Zuciyata tayi mun dadi naji sanyi na
dan yi wani abu. Sai dai babban abin
takaicin shi ne, bayan kwanaki biyu kawai
da faruwar hakan sai naji wa'azi a Rediyo
ana yi na matar da ta yi wa miji kyauta da
abinci ba tare da ya sani ba, irin
hukuncinta.
Sai dai har idan ta tabbatar da shi din
ma zai yi hakan, to sai tayi da nufin Allah
ya ba shi ladan.
Nayi shiru a raina ina tunanin to shi zai
yarda da hakan ko kuwa shisshigi nayi? Ba
zai yiwu na gaya mishi ba kada na Ballo
wa kaina liki, tunda dai an ce haramun ne
gara kawai na nemi hanya da zan nemi
nawa ita ce ta hanyar dinki tunda na iva,
kuma ina da keken yin dinkin.
70
Sannan unguwarmu sabuwar unguwa
ce, da alama za a samu alheri idan mutum
ya ce zai yi wata sana'a.
Washegari asabar don haka Ishak yana
gida da rana. Sai da na gama aikace-
aikacena na gida sannan nazo falon da
yake na zauna na fara yi mishi magana kan
tunanin da nayi na dinki tunda na iya.
Amsar da ya bayar a gajarce ce, ita ce
idan ina gidanshi to ba zan yi dinki ba. Ba
zai lamunci irin wadannan abubuwan na
nuna karanta ba.
Ba ni da abin fada, don haka naja
bakina nayi shiru. Kamar yadda shima ya
yi. Bani da wani abu da nake yi da ya
wuce aikin gida da girki.
Wannan a yanzu nake rayuwa akai babu
abinda yafi damuna irin tsayawar karatuna.
Ba zan ce Ishak ya yaudareni da
1yayena ba, don kuwa matsayj shi ya
wuce hakan mijina ne.
71
Sannan babu wanda zai kalle ni ya ce
Ina da matsala don kuwa a bayyane yake
na samu canji. Kana kàllona ka san ina
cikin wadata,
Sai dai to iyavena fa? Wannan shi ne
babbar matsalata.
Yau ma zama nayi da nufin jiran
dawowar Ishak na nemi i2inin zuwa gida a
washegari don kada ya ce ban fada mishi
da wuri ba.
Ina matukar kewar Babana saboda zan
iya cewa tun da aka yi aurena rabona da
shi, a yanzu kuma wata na bakwai nake
ciki.
Na jira shi har na gaji na hau kan
doguwar kujerar dake dakin na kwanta.
Bai shigo ba sai karfe goma sha biyu
daidai.
Na mike zaune saboda jin motsin da
nayi na kuma yi mishi sannu' ya amsa: Ban
tsaya zancen kawo mishi abinci ba don
72
kuwa ma a yanzu idan ya dawo ba yaci ko
na kawo mishi,
Ban yi mishi maganar ba sai da ya
kammala shirin kwanciya sannan na fara
kokarin yi mishi maganar.
Bai bar ni ba saboda dago mun hannu
da yayi alamar dakatawa.
Wai ke ba ki da wata magana ne sai ta
gidanku? Mits! Yayi tsaki ya yi
kwanciyarshi.
Sai mutum ya wuni aiki amma idan ya
dawo gida a maimakon a barshi ya huta
wai sai a tasa shi a gaba da surutan banza.
Ya ja abin ruhuwarshi ya kwanta.
Na riga na saba da dabi'un Ishak, don
haka a yanzu ba su cika damuna ba.
Washegari har na gama mishi shirinshi na
karyawa da sauran abubuwan shi na tafiya
aiki a raina ina tunanin zai yi mun
maganar zuwana gida da nayi mishi bai ce
komai ba ya tafi.
73
A duk 1ökacin da ya tafi aiki na kan
dauki wayata na kira Hindu ta taya ni hira,
hakan ne yasa muka yi wata irin shakuwa
ba kadan ba.
Hindu wayayyiyar yarinya ce ba kadan
ba, haka nan yanayin irin gidajen da muka
tashi ma ba daya ba ne.
Don kuwa kamar yadda nake "yar talaka
ita kuwa ya ce ga babban Ma'aikacin
Gwamnati, Mominsu ma wayayyiyar mace ce.
Wunin da nake yi da ita a cikin gida
yayi matukar taimaka mun kwarai da
gaske kan al'amurana. Ban taba zama na
fada mata wani abu game da mijina ba,
amma sai ta gane hakan.
Wanda yasa ta yi mun magana, ban
saurari abin ba don ganin da nake yi mata
na cewa ita din ko da muke kusan sa'o'in
juna ita ba macen aure ba ce.
74
Haka nan kullum Umma tana gaya mun
na rike sirrina. Don haka ko da ta yi mun
magana murmushi kawai nayi.
An dan dade kafin na samu Ishak ya
bani izinin zuwa gida. na zaune cikin
motar daidai ya tsaya a kofar gidanmü na
ce mishi "Ko za ka bar ni ne zuwa dare
don na gaisa da Babana?"
Bai ce komai ba, nima kuma ban sake
yin magana ba. Hira sosai muka yi da
Umma ina mata korafin ba a taba kawo
min su Tasi'u ba
Tayi murmushi ta ce, "To sai ki gayawa
Babanku tukunna. Na ce, "To." Babana
ba karamin jin dadin ganina ya yi ba.
Yayi ta murmushi ba iyaka, yana ta dan
yi mun tambayoyi ina ba shi amsa tare da
jaddada tambaya daya da yake yi min.
Babu matsala dai ko Hauwa'u? Na
ce, "A'a babu." Ya ce, "To ki yi ta hakuri
kin ji, shi zaman tare hakuri ake yi."
75
Na ce, "To Baba." Kamar na danne
abinda ke damuna sai dai na kasa. Na ce
"Baba sai dai maganar Makarantata ne har
yanzu shiru.
Nayi mishi bayanin yadda muka yi da
Ishak ya dan yi shiru zuwa can ya ce, "Too
babban al'amari a wurin mu ai shi ne ki
zauna lafiya a dakin aurenki.
Kuma ga dukkan alamu kina da
kwanciyar hankali. Ita maganar karatu tana
zuwa ne daga baya.
Amma tunda dama can yasan da
maganar ina ganin bari ni da kaina nayi
mishi tuni muji abin da zai ce."
Tun kan Ishak yazo daukana nayi wa
Babana magana akan ina bukatar su Tasi'u
su zo min kwana biyu, ya ce "To."
Ba a wani dade ba rannan kawai da rana
sai ga Yaya Auwalu da su Tasi'u da dan
kayansu a kullin leda.
76
Murnata bata boyuwa, na rasa inda zan
ajiye su. Nan da nan na shiga kicin na fara
ajiye musu dan abinda nake dashi.
Muka yi hira da Yaya Auwalu sosai
daga ni kuma ya yaba da inda nake don
kuwa bai taba zuwa ba shima sai yau.
Ya jima sosai kafin yayi mun sallama
ya tafi, ya bar mun Tasi'u da Sadisu akan
za su y1 mun sati guda.
Muka wuni muna harkokinmu ba kadan
ba cikin raha da jin dadi. Hindu kuma tazo
ta debe su ta kai wa Mominsu suka gaisaa
suka dawo tare da kaninta Abubakar.
Da daddare kuwa hira muka sha ba
kadan ba, nayi dariyar abubuwan da suke
bani labari har na gaji.
Rabon da naji dadi irin a yau har na
manta. Ba su yi barci da wuri ba saboda
kallon da suke yi sai wajen karfe goma na
dare kafin nan kuwa ni kaina na gaji.
Nayi wanka na gyara na hau gadona na
kwanta, kan ka ce meye har nayi barci
77
abinda ya hana ni jin dawowar Ishak don
kuwa ban farka daga barci ba sai da naji
kiran sallar Asubahi,
Da sassafe Ishak ya fita wanda shi ne
dalilin da ya sa ban tuna gaya mishi zuwaan
su Tasiu ba sai bayan tafiyarshi.
A yau mna wuni muka yi muna
harkokinmu. Nayi mana abinci mai dadi
dafadukar taliya da taji hanta ga kuma
farfesun kayan ciki, don kuwa nasan babu
abinda suke so irin taliyar.
Yau ma sai da muka yi hirarmu wajen
karfe goma sannan na shinfide su a dayan
dakin na gyara musu komai na fito na hau
gadona ina tunani a raina irin kewar da zan
ji ranar da su Tasi'u za su koma gida.
Idan da da hali da na roki Umma ko
Babanmu su bar mun su Tasi'u.
Kwanciyar nayi da nufin na yiwa Ishak
maganar idan ya amince to, tunda muna da
wadatar waje.
78
Yau ma ban san sanda ya dawo ba
saboda barci mai nauyi da ya dauke ni.
Can cikin barcina naji kamar ana kirana.
Na bude ido cikin sauri saboda gane ba
mafarki nake yi ba. Sadisu ne. Sai dai ba
ni kadai ce na tashi ba har da Ishak.
"Menene ya faru Sadisu? Ya ce,
"Aunty zan yi fitsari ne." Na mike cikin
sanyin jiki saboda irin kallon da Ishak
yake yi mun, na dawo dakin da suke nasa
shi a bayan gida yay.
Na sake shimfide shi ina kara jaddada
musu in sun ji wata bukata ba sai sun tashe
ni ba su shiga bandaki kawai su yi.
Na kuma gaya musu hakan tun kafin su
kwanta amma kuma sha'ani irin na yaro.
Na shigo dakin, Ishak yana zaune a kan
bakin gadon nayi nufin wucewa naje na
kwanta, duk kuwa da sanin da nayi na
cewa ni yake jira.
79
Sai, dai yanayin shi da ke sani cikin
faduwar gaba. "Zo nan. Abinda yace mun
kenan.
Na nemi wuri a kasa na zauna. Me
wadannan yaran suke yi mun a gida?
Lafazin da yayi amfani da shi yasa na rasa
abunda zan ce, ko kuma ta inda zan fara.
Cikin daga murya ya ce, "Ba ki ji
abinda na ce ba ne ko ya ya? Na ce, "Eh
naji, ba ka gane su ba ne? Su Tasi'une fa
da Sadisu kannena.
"Hala kin ga alamar makanta ne a tare
da ni ko? Nayi maza na ce "A'a ba haka
ba ne."
Idan na ce zan tsaya fadin irin tashin
hankalin da na gani ranar a tare da lshak to
nayi karya. Duk kuwa da irin bayanan da
nayi mishi wanda ko saurarona bai yi ba.
Maganar kuwa da muka wayi gari da ita
ita ce, ta bai yarda su sake kwana mishi a
gida ba, maza-maza na sa a mayar da su
kwana biyun da suka yi ya isa haka.
80
Bai ci komai ba ya fita. Bai bani kudin
motar mayar da su ba, duk kuwa da yasan
banida ko asi.
Nayi iyakacin kokarina wajen juriya
kada 'yan yaran nan su fahimci wani abu.
Tasi'u bai fi shekara shida ba, shi kuwa
Sadi yafi uku amma bai cika hudu ba.
Yan kannena da nake da su amma wai
Ishak ba zai iya mu'amalla da su ba.
To sai da wa? Ko da yake ni din ma da
ya aura ga irin yadda yake tafiyar da ni.
Sanin hakan da nayi bai hana ni bakin ciki
mai yawa ba. Biye mishi zan yi?
Ko kuwa dai zan nemi mafita ne? Na
gama ayyukana nayi lullubi tare da rufe
gidan na shiga gidan su Hindu.
Mominsu tana daki nayi sallama na
shiga, na bar su Tasi'u a wajen yara suna
wasa. Ban boyewa Momi komai ba.
Ta tashi ta shiga daki ta dauko kudi
masu yawa ta bani ta ce "Ki koma gida
81
idan Hindu ta dawo zan turo miki ita sai ki
bata ta mayar da su gida.
Kiyi hakuri, ki kuma yiwa mijinki
iyakacin biyayyar da za ki iya idan har
bata sabon Ubangiji ba ce.
Kada ki să damuwa a ranki ko kuma ki
ce wai za ki yi fushi da shi kin ji ko?" Na
ce "Eh."
Na dawo gida na ci gaba da kwanciya,
don kuwana rasa kuzari tunani iri-iri a
cikin raina.
To da Ishak ya yi mun haka a kan
kannena shi nashi 'yan uwan baya tunanin
za su iya zuwa ko kuwa idan suka zo ya ya
yake so ayi?
Na sake yin shiru, to a zaman da nake
yi ma zan iya cewa bai taba yi mun wata
magana ta game da 'yan uwanshi ba kamar
yadda ban taba ganin wani yazo ya ce shi
abokin shi ne ba.
82
Nayi saurin mikewa na zauna ina wasu
yan anane-tunane a raina, tambayoyi iri-
iri da nake bukatar na samu amsarsu...
Sallamar Abubakar kanin Hindu ne ya
katse mun tunanina. Ya miko inun bakar
leda ya ce "Ga shi in ji Momi. Na karba
ina dubawa.
Littattafai ne na Hausa da alama ta bani
ne na samu na karanta ni ba ma'abociyar
karatun ba ne, amma sai naga barı na ajiye
kada ta ce na gwasaleta.
Na mike don samarwa kaina abinda zan
Ci tunda yamma ta fara yi. Chives kawai
na soya da kwai naci na sha shayi aka:
sannan nayi sailar Magriba.
Ina idar da saliah sai kawa naji
sallamar shigowar Ishak, mamaki ne yayi
Ihatukar kama ni, zan iya cewa tunda, aka
yi aurenmu ya koma aiki bai taba dawowa
kafin ayi saliar isha'i ba.
Asali na ya dawo karie tara yayi sauri.
Na mike ina nade dardumar sallah tare da
83
yi mishi sannu da zuwa, bai amsa ba don
dama nasan hakan ne zai biyo baya.
Saboda zai yi mun abu wanda zai sani
bakin ciki amma shi ne kuma mai yin
fushi idan har ba hakun na bashi ba, kuma
to ba zai taba saukowa ba.
Sai dai a wannan tunda dai nasan ban yi
mishi wani laiff ba, to nima ban shirya
bada hakurin ba.
Na shiga kicin cikin sauri nayi mishi
abinda zai ci, fried rice da farfesun danyen
kifi wanda duka aikin bai dauke ni awa
guda ba.
Na kawo na ajiye mishi. Sai dai ban
ganshi a falon ba. Na shiga cikin dakin
kwananmu nan ma hakan. buruntun da
naji a daya dakin ne yasa ni lekawa.
Gyarawa yake yi yana kakkawar da
wasu abubuwa duk da dai har da ba a wani
amfani da daki banabarin shi da datti.
Ine tsaye ina kallon 'irin gyaran da yake
yi na shiga daki na dauko wani zanin
84
gadon na shimfida akan gadon na sa
tsintsiya na share dakin.
Bai ce mun kala ba ya shiga asalin
dakinmu ya fara kwaso kayan shi yana
maida su daya dakin.
Aikin da ya dauke shi har karfe goman
dare, don kuwa tsinke nashi sai da ya
dauke ya kai shi daya dakin, kuma ya
gyare shi tsaf ina zaune a. falon ina
kallonshi.
Ya shiga bandaki yayi wanka ya bada
tea yasha bai ko kalli abincin da na ajiye
mishi ba ya shiga sabon dakinshi ya
kwanta.
Ba sai na jira an yi mun wani bayani ba
nima da kaina na fahimci abinda hakan
yake nufi, nima sai na shiga tsohon
dakinmu ko kuma na ce na asalin na
kwanta.
Al'amarin Ishak ba na