MAI DAKI BOOK 1 HAUSA NOVELS BY SODANGI.docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   2 / 7

3K to 6K   out of 19.3K words

kuwa na fara fidda rai abinda

kwata-kwata ban saba yi ba kenan.

26

Dabi'ata ce kullum Zan yi bitar

littattafai na koda nake da matsala wajen

biyan kudin Makaranta ni din ina cikin

daliban aji da suke da matukar kokari.

Tunda har Malamaina ma sun shaida

hakan, to amma ya zan yi? Malam Ali ya

taso ni a gaba, bana kuma ganin laifinshi

tunda aikinshi yake yi.

Duk wadannan tunanina ne kafin

wayewar gari, don kuwa tsintar kaina nayi

da fara shirin Makaranta, har na fito tunda

sammako nayi ina yiwa Babana sallama

wanda a yau din zan riga shi tafiya.

Ya ce, "Ke Hauwa'u ba Ummanku jiya

ta ce mun satin nan kaf idan ki ka je

Makaranta koro ki ake yi ba?

Na ce, "Eh haka ne Baba." Ya ce, "To

amma a hakan ke gara miki kiyi ta zuwa

ana korarki? Maganar gaskiya shi ne nayi

niyyar baki wani abu ki kai Makarantar

taku.

27

To sai dai mu mamatsalar wurin aikin

mu yawa ce da ita tunda wannan watan shi

ne wata na wajen uku da ba a bamu

albashi ba, amma daga zarar an bamu wani

abu zan ba ki ki kai musu ko da babu yawa

ne. Sai ki ba su hakuri yau din idan kin

je."

Na ce, "To Baba." Na fito daga gida ina

tafiya tare da tunanin maganar Babana ni

ba abin in ce mishi ai yanzu ta kai ma ko

saurarona basa yi ba.

sli Babu amfani tunda ba da gangan yake

Rin biya ba.

Na shiga aji na zauna a darare ganin har

karfe tara tayi Malam Ali bai zo ba, sai na

waiwaya bayana inda Sadiya Tanimu ke

zaune.

Saidai ban ganta ba, don haka na ce wa

wacce suke zaune tare rmai suna Zubaida.

DunsDon Allah dan bani aron littafinki ná

Chemistry na dan fara kwafa kafin a

tashi.

28

Ta kalle ni ta dan tabe baki tare da

girgiza kanta kafin ta ce, "A'a a gaskiya ba

zan miki karya ba, ba zan iya ba haka

kawai azo a kore ki na manta ki wuce mun

da littafi.

Bari dai wacce ta saba baki tazo don

naga itama kamar ke karatun ba damunta

yayi ba, bambancinku kawai ita ana biya

mata kudin Makaranta."

Na juyo na ci gaba da wasu sabgogin ba

tare da na tsaya bai wa Zubaida amsa ba.

Ba a ko kai mintina biyar ba bayan nan

sai kawai Malam Ali ya shigo. Tun kafin

ya fara kiran suna na mike na kamo hanyar

dawowa gida, zuciyata cike da kunci da

6acin rai.

Har naZO zan shiga gida sai naji ana

kirana,Abdussamad ne. Na tsaya ya

karaso inda nake.

Hauwa'u kenan, yau ma kin kasa zama

ne kiyi karatun har zuwa lokacin tashi?

29

Wani gululun bakin ciki ya taso ya

tokare ni, wai wannan me yake nufi ne?

Na dago kaina da niyyar ba shi amsa.

Sai dai na kasa saboda dama kiris nake

jira, don haka da na lura kawai kuka zai

kubucemun sai na shige gida ba tare da na

sake sauraronshi ba.

Ina shiga gida wurin Umma na wuce na

durkusa, kuka na kama yi babu

kakkautawa, ba tace mun komai ba sai da

nayi ya ishe ni ina share hawayena sai ta

ce "To ni kam Hauwa'u ai bani da abin yi

miki da ya wuce na ki hakura da wannan

sintiri da ki ke yi ana koro ki ba tare da

fashi ba.

Ki dan saurara kema ki samu nutsuwa

amadadin wannan zirga-zirgan da ki ke yi.

Idan Babanku ya samu kudi ai ya gaya

miki zai ba ki dan wani abu ki kai musu

ko? Kafin karshen wata muga abinda

Allah zai yi."

30

Na dawo daki na debi kayan wanki na

fitar na hado da na su Tasi'u gaba daya na

fara yi, sai wajen Azahar na gama nayi

wanka na nemi wuri na zauna da niyyar

hutawa a ka yi sallama da ni.

Na riga nasan Abdussamad ne, don

haka kamar ba zani ba sai kuma na dauki

gyalena na fita.

Yana tsaye a kofar gidanmu sanye da

wandon Jeans da riga shirt fitted na gaishe

shi a dake.

Ya ce, Hakuri nazo baki don naga

kamar dazu na bata miki rai, kiyi hakuri

ban yi da nufi ba. Na ce "Babu komai.

Ya ce, "Kin tabbata?

Na dan yi murmushi na ce, "Uhum!"

saboda yanayin yadda ya yi tambayar. Ya

ce, "Ban san dalili ba Hauwa'u, sai nake

ganin kamar ni din ina da ruwa a cikin

al amarin karatunki.

Don kUwa ko babu komai ai ke kanwata

ce. ko ba haka ba? Na ce, "Eh haka ne.

31

Ya ce, "To 1dan mutum ya samu halin yin

abu to baya sakaci da wannan damar har ta

kubuce mishi.

Kiyi amfani da kuruciyarki ki taimaki

kanki kiyi karatu. Muka shiga wata hirar

ta daban, yana tambayata wasu abubuwan

ina ba shi amsa har Babana ya dawo.

Yau ma ya gaishe shi ya wuce na biyo

shi a baya yana tambayataYau an bar ki

kin yi karatun ko kuwa an sake koro ki?

Na ce, An koro ni Baba. Ya ce,To

sai kiyi hakuri muga abin da Allah zai yi."

Na ce, "To.

Har satin ya kare ban koma Makaranta

ba, haka nan kullum bayan sallar La'asar

Abdussamad yana zuwa mun hira.

Ranar Lahadi da yamma kwatsam sai

ga Sadiya Tanimu, na tare ta cikin farin

ciki ba kadan ba. Makwabtanmu na tura

aka sayo mun Zobo mai tsabta,

32

Na kuma yi sa'a dafaduka muka yi ma1

Kyau ta kuma yi dadi na kai mata dakina

bayan sun gaisa da Umma.

Tana cin abincin muna dan hira tana

bani labarin abubuwan da suka faru bana

nan, da irin gwajin da aka yiyyi a aji.

Naji wani iri a raina. Ta tashi zata tafi

na mike da niyyar yi mata rakiya. Da nisa

sosai na kaita har kusan barin unguwarmu

gaba daya.

Ta wuce ni kuma na kama hanyar

dawowa gida.

Baiwar Allah salamu alaikum. Jin

yanayin sallamar ne ya sani juyawa, wani

mutum ne a tsaye sanye cikin farar shadda

jamfa da wando.

Na amsa tare da nufin ci gaba da tafiya.

Dan dakata mana yanmata. Tun daga

dan nesa fa nake bin ki ban dai yi miki

magana ba ne saboda ganin yanayinki.

Na san ba yarda za ki yi ki tsaya cikin

mutane ba, shi yasa ban tsaida ke ba sai da

33

naga mun zo nan wurin. Sunanki nake so

ki fada mun.

Na ce, "Hauwa'u. 99 Ya ce, Gidanku

fa? Ba tare da yin wani dogon tunani ba

na yi mishi kwatance.Ya ce, "To ya

gode. Na dawo gida na ci gaba da

harkokina.

Har a yau Monday ma ban yi nufin

zuwa Makaranta ba, saboda maganar da

Babana ya yi mun na jiranshi zuwa

karshen wata don ganin abin da Allah zai yi.

Da yamma ne aka yI sallama da ni,

cikin zuciyata Abdussamad ne, don haka

hijabina na dauko na fito ga zatona

Abdussamad din ne, Sai kawai naga

mutumin jiya.

Yau ma sanye yake cikin tafafe na

kamala, jamfa da wando, rigar half jamla

ta matukar yi mishi kyau.

34

"Ina wuni? Na fara gaishe shi cikin

girmamawa, don kuwa ba karamin yaro ba

ne.

Lafiya Hauwa'u, yaya karatu? Na ce,

"Mun gode Allah."

"A aji nawa ki ke a Makaranta? Na

gaya mishi ya dan yi murmushi "Kina da

saura dai ashe." Muka dan yi hirar karatu

kadan, abinda ya sa na saki jiki da shi.

"Kina da sha'awar yin karatu mai zurfi

ne? Ko za ki tsaya ne daga gama

Secondary?" Na ce, "Idan na samu halin ci

gaba haka nake so."

Ya ce, Eh yana da kyau, kin san

karatun 'ya mace ba karamin abu ba ne ga

ya'yanta, da kuma mijinta baki daya.

A daidai lokacin ne Abdussamad yazo,

ganinmu yasa shi juyawa ya tafi. Mutumin

ya kalle ni yana dan murmushi.

Ina fata dai ban tsarewa saurayin naki

wuri ba'? Na ce, "A'a ba saurayina ba ne.

Ya ce, "Menene, abokinki ne?"

35

Na dan yi murmushi, ya dan yi ajiyar

ZUciya ya ce, "To Malama Hauwa'u, ni dai

kin ganni ba yaro ba ne karami, don haka

ya kamata ki gane ba da wasa ko yaudara

nazo wajen ki ba.

Na gan ki ne na yaba da halinki da

kuma dabi'arki ta nutsuwa da na gani a

tare da ke. Ni ba mutumin garin nan ba ne,

nazo wani dan aiki ne wanda nake ganin

kamar zai dauke ni tsawon shekaru uku

zuwa hudu.

Sunana Ishak, ina kuma aiki ne da

Ma'aikatar noma wato (Ministry of

Agriculture). Ina fata zan samu hadin kan

da nake nema a.tare da ke?

Ina so na gaya miki ba zan tauye ki na

hana ki karatunki ba, don kuwa kina da

kuruciya sosai. ldan aka yi miki hakan ba

a yi miki adalci ba.

Don haka ina so kiyi tunani mai yawa a

kai zan dawo rana ita yau din nan don jin

abin da ki ke ciki.

36

Na ce, To. Y asa hannu ya miko mun

kudi, ya ce "Ungo wannan. Na dan yi jim

kamar ba zan karba ba, ya ce "A'a karbi

kawai."

Na ce,To na gode. Sannan ya bude

bayan motar shi ya sauke mana doya

manya goma da buhun shinkafa da wata

leda babba baka.

Yayi sallamaya tafi. Na dade a wurin a

tsaye kafin na shiga gida.

Ummma ta zubawa kayan idanu ta ce,

"Ikon Allah! Shi kuma wannan ko waye

sai Allah. Na zauna na jawo ledar na bude,

zannuwa ne masu kyau guda biyu da

kayan shafa masu daraja.

Sai da Babana yaci abincine sannan ya

kira ni na same shi a zaune. "Ke Hauwa'u

ashe dama kin fara tsayuwa da samar1 ne

ni ban sani ba?

Naji wani iri a cikin jikina, na kuma

rasa abinda zan ce mishi. Ya ce, Ke ía

nake sauraro don ni nayi zaton shi wanan

37

yaro Abdussamad da nake ganinku da shi

ba wani abu ba ne a tsakaninku face

makwabtaka da mutunci.

To shi kuma wannan a ina ki ka same

shi?" Nayi wa Babana bayanin komai

game da mutumin, har da ranar gamuwvata

da shi da kuma abinda ya gaya mun da kan

shi ya ce "To tashi ki tafi."

Na dawo dakina na zauna bayan na kai1

wa Umma har da kayan atamfofin da

kudin wanda ta mika su ga Babana gaba

daya.

Washegari Abdussamad bai zo ba

kamar yadda ya saba, sai bayan kwana

biyu ne inda dawowa daga siyo sugan da

naje yi a shagon unguwarmu, na ganshi

tsaye kusa da shagon

Ya ce, "Hajiya Hauwa'u. Na ce Ni

din ce kuma Hajiya a yau? Ya ce Eh

mana, ba dole nace FlajIya ba, wannan irin

luntsumemiyar mota haka a1 kin san mai

niya ake cewa llajiya ba wanda yaje ba

38

Kin ga yanzu dole mu rinka yi a hankali

kenan tunda Tunku ma yasan shurin da

yake yi wa kashi.

Na ce, "Haka ne." Ban tsaya cigaba da

jin abinda yake fada ba, tunda na fahimci

so yake ya soka mun magana sai kawai

nayi gaba.

Ranar da Ishak ya ce zai zo kuwa sai

gashi ya dawo, na kuma isar da sakon

Mahaifina a gare shi ta yana son ganinshi.

Bai tsaya wani dogon bata lokaci ba ya

ce, zai jira shi ba sai yaje ya dawo ba, don

haka shigowa gida nayi na bar shi da nufin

shi na sai yaga Babana kafin ya tafi.

Hakan kuwa aka yi, ban san yadda suka

yi ba, bani kuma da damar tambaya, don

haka harkokina kawai nasa a gabana.

Na dai yi nufin tambayar Umma ko

Babana zai bani kudin nan naje na biya

kudin Makaranta dashi, sai dai na gagara

saboda nauyin da nake ji.

39

Ban yi zaton zuwanshi a washegari ba,

kwatsam sai ga shi. Ina tsaye yayin da

yake jingine jikin motarshi ya ceNa

dawo ne yau don nayi miki magana kan

al'amuran da muka tattauna da Baba.

Muyi magana da ni da ke saboda

fahimtar juna. Jiya ganin da nayi mishi ya

bani izinin turo magabatana don daidaita

maganar aure."

Cikin wani irin mummunan faduwan

gaba na dago kai na kalle shi, karo na

farko da nayi hakan a karo na uku da fara

Zuwanshi gidanmu.

Yana cikin matsakaitan mutane, shi din

ba kyakkyawa ba ne, haka nan ba za a kira

shi mummuna ba.

Shi da kanshi ya lura da canzawata, ya

ce "Shi yasa na ce zan ganki don mu

tattauna a tsakaninmu. Kina da matsala a

kan turo magabatana da zan yi?

A hankali na girgiza kaina alamar a'a,

don kuwa babu wani hukunci da Babana

40

Zai zartar na sa kafa na shure shi da sanina,

kuma ina cikin hayyacina ba.

Ya ce, To ya naga yanayinki ya

canza? Ban san dalili ba sai na samu

kaina da ce mishi "Karatu nake yi." Ya

dan yi murmushi.

Don ta wannan nayi wa Mahaifinki

alkawarin zan sa ki a Makaranta kiyi ta

karatun har ki gama, bayan wannan kuma

sai me? na ce, "Babu." Ya ce, "To ni

ranar Jumma'a zan tafi Kaduna gida wurin

iyayena, don mu zanta kan maganar.

Na ce, "To Allah ya kiyaye hanya." Ya

ce, Amin. Ya miko mun kudi a

hannunshi na karba tare da godiya.

Duk yadda na kai da daurewa da na

zauna gaban Umma zan yi mata magana

sai kawai na fashe da kuka.

9T6 Menene kuma na kuka? Ta tambaye

ni fuskarta a yamutse. Na ce "Umma daga

zuwa biyu sai kawai maganar aure, ko

41

gama saninshi bamu yi ba, sannan

karatuna fa?"

Tayi shiru ta ci gaba da saka maballan

gar da na samu ta gama, an kai kamar

mintina biyar sannan ta fara yin magana.

"Babanki ba shi da halin daukar

dawainiyar Makarantarki, kema kin san da

haka. A yanzu ma da ki ke Makarantar

Secondary abin ya gagara ballantana kin

shiga wacce ki ke burin yi ta koyon jinya.

Idan da kina da zurfin tunani kema ya

kamata ace kin fahimci hakan. ke kadai ce

a cikin ku bakwai ki ke ka ratun nan,

amma a biya miki kudin Makaranta ma

abin ya gagara.

Babanku yana zuwa wurin aikin nan da

yake yi ne kawai ba wai don kudin da ake

ba shi ba tunda a yanzu ba biya ake yi ba

sai don kawai kada ya zauna a gida ba tare

da yana da abin yi ba.

Ba kuma zai yiwu ya ce takamar ke da

shi kuna son kiyi karatu ya yi ta ajiye ki a

42

gida ba, ke mace ce. Kin kai lokacin aure

tunda kuma sh1 ya ce ya yaba da kamalar

mutumin.

Ina ganin shi kenan magana ta kare, ya

kuma yi alkawarin zai tsaya yaga kin yi

karatun da ki ke son yi.

Na tashi na dawo dakina na kwanta

saboda yanayin da jikina ya yi mun, aure a

yanzu? Babu abinda ke zagaya mun

kwakwalwata irin ko wata guda ban yi da

sanin mutumin ba.

To amma tunda dai yayi alkawarin zan

yi karatu shi kenan magana ta kare, dama

burina kenan idan na samu hakan kuma

zan yi murna.

Bayan nan ban sake zuwa Makaranta ba

saboa abinda Babana ya ce kenan a jinkirta

aga yadda maganar zata kaya.

Na ci gaba da karatun a dakina. Sati

biyune kawai bayan nan iyayen Ishak suka

zo an sasanta da su har an daidaita lokacin

aure don suma suna son shi da gaggawa.

43

Sun kuma zo da kayansu na na gani ina

So. Tun daga lokacin da maganar aurena ta

yadu ban sake ganin Abdussamad na

gaishe shi ya amsa ba wani lokacin ma

yana hango ni yake kaucewa.

Ban san abinda yake nufi ba, don haka

nima sai kawai na share shi.

Shirye-shirye na nima nake yi da

iyakacin karfina tunda dai ba zance bana

son Ishak ba, kamar yadda ba zan ce ina

Son shi ba.

Babban burina dai da nake hangowa

kamar nishadi. Ishak da kanshi ya

shaidawa iyayena ba ya bukatar wata

doguwar dawainiya da ta danganci kayan

daki, shi gidanshi akwai komai.

Don haka shirin da Umma ma take yi

ya dan yi sauki kokarinta kawaina ganin ta

hada mun kayan kicin ne ta kuma saya

mun sabon Keke gau a kwalinshi.

Tunda nima ta koya mun dinki na kuma

iya daidai gwargwado. A shirye-shiryen da

44

aka yi mun a gida kuwa har da na zuwan

garin ma garin Babana Birmin Kudu, duk

kuwa da suma za su zo bikin.

An yi mun shirye-shirye masu yawa

daga gida amma duk da haka sai da Ishak

ya kawo kudi masu yawa ya kara mun.

Zan iya cewa tun da aka fara maganar

aurena da shi al'amarin da yanayin

gidanmu gaba daya ya canza, don kuwa

duk zuwan da zai yi zai kawo kudi masu

dan dama ya bani.

Haka nan ba zai rasa abin amfani da zai

sauke mana ba. Tun da farko da Babana

yana karba ya hana ni am fani da kayan da

yake bani.

Amma da aka zo magana tayi karfi sai

ya bar ni har da kayan da yake kawo mun

na zannuwa yana karba yanzu duk ya

dawo mun da su.

Ni kuma na kai an diddinke mun su, ina

ta kwalliyata gwanin sha'awa. Wani lokaci

45

sai nayi tunani na ce to a waje ma ya

wadata ni haka ina kuma ga naje gidan shi.

Kwanaki uku kawai nayi a birnin kudu

duk kuwa da yawan 'yan uwan Babana da

ke garin saboda gabatowar bukina na

gaiyato kawayena irin su Sadiya da wasu

daga cikin ajinmu da na san muna mutunci

da su.

Na kuma gayyato Lubabatu kanwar

Abdussamad da muke unguwa daya da su

gashi kuma dama tare muka tashi tunda

sa'o'i muke.

Ina zaune a dakina ina shafa mai na mai

tsada Ishak ne ya ke saya mun shi wanda a

yanzu ya mayar mun da jikina tamfar

wacce aka

2 / 7