Author : Hafsat C Sodangi Category : KDP NOVELS
karewa ba ne,
kuma na lura idan na ce zan zauna ina
85
kwana ido biyu saboda bacin ran da yake
sa ni to zan wahala ba kadan ba.
Kwana da kwanaki muna cikin wannan
hali ya mayar da wancani dakin na shi
nima kuina ga nawa.
Tsakanina da shi gaisuwa ce ta sate ta
dare kuwa bana ma sanin sanda yake
dawowa. Nayi iyakacin addu'o'in da zan
yi a kan hakan ban ga canji ba.
Gyaran daki nake yi lokacin da na sake
cin karo da littattafan Momi. Na bude
daya na fara karantawa. Wunin ranar bata
kare ba sai da na gama shi tas na dauko na
biyun shima haka.
Cikin kankanin lokaci sai na koma
wurin Momi neman kari. Kullum da safe
idan na gama aikina na gida sai na zauna
nayi ta karatuna bana tashi sai sallah ko
cin abinci.
Sai ya zamana na koyi abubuwa in-iri
wadanda wani bai taba zaunar da ni ya
koya mun ba.
86
Abubuwa da suka danganci zama da
miji, zama da mutane, girki, kuia da kai.
gyaran jiki, kai abubuwa daban-daban.
Idan nazo wani wajen naji takaici, wani
wajen nayi dariya, wani wajen naji tausay1,
wani wajen kuwa naji kamar labarina ake
bayarwa da' Ishaf.
Don haka ga abinda zan yi. Damuwata
tayi matukar raguwa, na kuma y1 niyyar
yin amfani da shawarwarin da Marubuta
suke bayarwa da suka danganci zama na
aure na kuma Zubar da na banza.
Tsawon sati biyun da muka yi a hakaa
muka yi ta da Ishak gaisuwar safe, dn uwa
da daddare kan ya dawo nayi barci.
Amma na kuduri aniyar gyaran aurena
don na fahimci ba haka ake auren ba.
Aure yana yin nasara ne idan har akwai
kyakkyawar alaka ta addini da
zamantakewa a tsakanin ma'aurata, uwa
uba: kuma soyayya ta gaskiya da take
haifar da yafiya a kowanne lokaci.
87
Sannan Annabi (S.A.W) ba haka yayi
Zama da nashi 1yalin ba, don kuwa babu
wani mutum da zai nunawa matarshi
kwatankwacin irin soyayyar da ya nuna ga
iyalinshi.
Babu kyamata, babu hantara bare
tsangwama a cikin al'amarin aure. Miji da
mata (ma'aurata) duka su baiwa junansu
lokaci na hira, kulawa, da tausayawa
wacce suke haifar da karin soyayya da
fahimta a tsakani.
Na jawo akwatin kananan kayana na
bude ina dubawa tare da tunanin wacce
zan yi amfani da ita.
Duk da ina jin kunyar yin hakan amma
idan har zai kawo mun gyara ga aurena to
ko meye zan yi idan ba sabon Ubangiji ba
ne.
Rigar bata wuce mun iya gwiwa ba,
haka nan shara-shara ce don kuwa kusan
koma: nawa a bayyane yake.
88
Na gyara gashin kaina wanda na wanke
shi da man wanke gashi na (Trichup)na
kuma shafe shi da kayan gyara iri-iri.
Duk da ba wani tsawo ne da gashin
nawa ba ya yi kyau ba kadan ba. Ga jikina
da yayi luwai-luwai saboda jin dadi.
Maganar gaskiya ita ce Ishak ya wadata
ni da abubuwan jin dadi da suka danganci
abinci da na gyara.
Sai dai a yanzu na fahimci ba su ba ne
masu muhimmanci wanda bai bani ba shi
ne komai, wato soyayyarsa da lokacinsa.
Na kuma kuduri aniyar nema ta hanyar
da ta dace.
Na dawo falo na zauna na ci gaba da
yan karance-karancena, don kada barei ya
dauke ni.
Yau sha daya saura kwata ya dawo. A
lokaci na dawowar Ishak kuwa to ya dawo
da wuri. Ya shige dakinshi ban ce mishi
komai ba kamar yadda bai kalle ni ba.
89
Gabana sai faduwa yake yi, kodai na
kyale shi ne kawai? Kai a'a, na dauki
abincin da na ajiye mishi wanda ni kaina
rabon da nayi girkin gidan da shi har na
manta saboda ba ya ci.
Nayi sallama a daidai. kofar dakin na
shiga ba tare da na jira amsawar shi ba.
Wanka yake yi, don haka na zaunaa
bakin gadon ina jiran shi. Ya fito yana
goge kanshi da karamin tawul nayi mishi
sannu na kuma gabatar mishi da abinci.
Bai ce mun komai ba sai da ya zo zai
kwanta.
Ya ce, "Ni fa kwanciya zan yi ko za ki
je dakinki ne?" Wani abu ne ya tokare ni a
wuya, na mike na dawo dakina na kwanta.
Don takaici sai kawai na fashe da kuka.
Me ke faruwa ne'? Shin fita hanyar Ishak
zan yi ko ya ya? Abu daya ne ya sani na ji
sanyi da naje debe kwanukan abincin da
na kai mishi naga ya dan ci.
90
Yau ma shiri sosai nayi mishi ban damu
da korata da yayi ba jiya, don kuwa gyara
nake so.
Kuma na kuduri aniyar yi ta kowacce
hanya in dai ba fin karfina abin ya yi ba.
Ganin da nayi ya dan ci abincin yasa ni
yin niyyar yi mishi wani abincin da nufin
neman burge shi.
Sai dai kash! Ban ma san abincin da
yake so ba. To amma na cire wannan
tunanin a raina kawai nayi abincina mai
kyau kuma na burgewa na dan hada mishi
da kunun zaki.
Yau ma irin kwalliyar jiya nayi. Ban
kuma yi barci ba har ya dawo. Dakin shi
na bishi yana kokarin daure igiyar rigar
barcinshi na ajiye tiren da ke dauke da
food flask da sauran plate da cokula na
Juya na je na dauko Jug din da na ajiye na
kunun zaki na dawo.
Ina shigowa ya ce, "Ki kwashe
kwanukan nan ki fita da su ba zan ci abinci
91
a wannan daren ba." Raina bai baci ba, na
ce "To ga kunun zaki mai sanyi ne sosai."
Na kalli yanayin shi yana daga kwance
hakan ne yasa na jawo kofi na tsiyaya
mishi kunun na mika mishi.
Kamar dai ba zai karba ba sai ya mike
ya zauna ya karba ya kara miko mun kofin
na kara, mishi na tashi da niyyar fitar da
kwanukan abincin da ya ce ba zai ci ba.
Har na juya ya kira ni "Zo ki zuba mun
kadan." Na ce "To." Kadan din na zuba
mishi na kara mishi kunun zakin sannan
na jira ya gama na kwashe kwanukan na
fitar.
Ban koma dakin ba nawa na shiga nayi
kwanciyata. Da sassafe ban koma barci ba
sammako nayi na yi mishi abin karyawa
cikin sauri na kawo mishi.
Har ya gama shiri lokacin da na shiga.
Kwalliya sosai nayi ya kalle ni ya kalli
tiren kayan karyawan. Na ce "Ko za ka
karya ne kafin ka fita?"
92
Bai musa ba zama ya yi na zuba mishi
ya karya har ya mike sai ya kalle ni
"Unguwa za ki je? Na ce, "A'a." Ya ce,
"Au to na dauka ko kin fara fita ne ba ki
tambaye ni ba."
Na ce, "A'a ba za a yi hakan ba." Yau
wuni nayi cikin jin dadi a raina. wajen
karfe uku da rabi yaron da ya saba aikowa
da cefane yayi sallama.
Na zauna ina duba cefanen yadda ya
saba kawowa ne bambanci kawai shi ne
kafar Saniyan da na gani a ciki. Na dauko
wayata duk da ban taba yin hakan ba, ban
kuma san ya ya zai dauki hakan ba.
Tana yin kara ya dauka, "Lafiya?
Tambayar tayi mun wani iri, amma sai na
daure na ce "Dama zan tambaye ka ne,
kafar Saniyar da na gani za ka ci abincin
dare a gida ne?"
"Da can sauran cefanen da ake kawowa
tambaya ki ke yi?" Na ce, "Aa." Ban
saurari jin karashen maganar ba na kashe
93
wayar saboda abinda naji a cikin zuciyata
na tamkar ina kokarin cusa kaina da yawa
a wajen Ishak.
Na hada kayan kawai na sanya
kowanne a mazauninshi na kuma wanke
kafar da niyyar yin miyar ganda da ita.
Sai da na hada komai sannan na dora
tuwon shinkafa. Na gyara kicin din na
kammala komai a mazauninshi. Na dawo
daki nan ma na kara kikkintsa abubuwan
da suke bukatar kintsi.
Sai da na gama ayyukan abinci sannan
na shiryawa Ishak nashi abincin a inda na
saba, tare da sauran kunun zakin jiya
wanda ya kara jika.
Yayi dadi ba kadan ba. Na shiga wanka
na hado da alwala nayi sallar Magriba
sannan na zauna domin nayi shafa.
Yau ana idar da sallar Isha'i kawai sai
ga Ishak shi kanshi ya gane nayi mamakin
hakan, sai da ya gama shirinshi kafin ya
fito ya zauna a falon.
94
"Kawo mun abincin nan wurin". Na
shiga dakinshi inda na ajiye abincin nashi
na fito dashi na zuba. Ba karamin abinci
yaci ba, don kuwa miyar tayi dadi ba
kadan ba.
Na gama kwashe kwanukan sannan na
dawo ina kallon tashar da ya kamo ta
Aljazeera yana sauraron labarai.
Sai wajen karfe goma sannan na mikKe
don kwanciya. A raina nasan 1dan na ce
zan jira Ishak ban san lokacin da zai
kwanta ba.
Haka nan kwanakin da nayi ina zaman
jiran dawowarshi sun sa barci ya kama ni
da yawa. Na gama shirina na zauna a
bakin gado ina addu'o'ina da na saba yi na
kullum kafin kwanciya, sai ya shigo.
"Zo mana." Na mike na bishi.ba zai
yiwu na ce Ishak yana neman mata ba don
kuwa ban gani da ido ba bani kuma da
wanda zai fada mun.
95
Amma idan abin shi ya motsa mishi na
fushi ko halin da ya saba yana jimawa ba
tare da ya neme ni ba sat da tun da na
samu na fara shawo kanshi ta wannan
hanyar al'amuran gidana sun dan fara yi
mun sauki.
Na farko dai ya daina zaman karfe sha
daya ko sha biyu a waje, idan yayi dare to
karfe goma, duk kokarin da nayi kuma na
ganin na gane ko na fahimci abin da yake
yi a wajen na gagara.
Tun da na lura da shi na gane ina janye
hankalinshi da irin shigar da nake yi mishi,
kullum da irin wacce nake canzawa.
nKo da ba ya cewa komai kuma ina gani
a aikace. Sai dai abubuwa kullum da irin
wacce take zuwa.
Shirin da nayi musamman don naje gida
yau amma sam 1shak ya ki yarda, duk
kuwa da na gaya mishi cewa Umma zanje
gayarwa saboda rashin lafiyar da take yi.
96
Har Hindu da Móminta sun je sun
dubota amma sam shiya ki barina ya
kuma ki żuwa shi ya dubota.
Kullum sai dai na kirata a waya. Na
záuna na buga tagumi duk wani abu da
nake Rokarin ya rage mun Bacin rai ya ki.
Da ya dawo kuwa ban fasa yi mishi
abinda na saba ba. Amma gari na wayewa
da na kara rokonshi ya ki, ban ce mishi
komai ba.
Yana fita sai na shirya na dauki gyalena
burina bai wuce naga halin da Umma take
ciki ba, tunda ni dai zamana da ita ban
taba jin tayi wata rashin lafiya ba.
Don haka hankalina a tashe yake ba
kadan ba.
Jikin nata babu dadi sosai, amma duk
da haka ban zauna ba don kuwa kwata
kwata ban fi awa daya ba na dawo.
Na dawo duk da dai ban ji dadin ganin
da na yi wa Umma ba, na samu saukin
97
damuwar rashin Zuwa dubata da.ban yi ba
kwana da kwanaki.
Ban dade da shigowa ba sai ga Ishak ya
shigo ina yi mishi sannu bai tsaya amsawa
ba sannan yanayinshi gaba daya ya canza.
Ina ki ka je? Shi ne tambayar da ya
fara yi mun. Nan da nan na kama inda-
inda kan in san abinda zan ce tuni ya
dauke ni da mari kauu!
Duka Ishak ya yi mun mai shiga jiki,
sannan yayi ficewarshi ya komawurin aiki.
Tun daga lokacin wani irin zazzabi yaa
rufe ni wanda yafi kama da na bacin rai da
bakin ciki.
Bai dawo ba sai can cikin dare. Ina
zaune a tsakiyar gadona har a lokacin
kukana bai kare ba.
Washegari, kuwa ga zazzabi, ga karin
tsamin jiki, Don haka ko, tashi nayi abin
karyawa ban yi ba. Sai da naji yunwa tana
neman nakasa ni ne na tashi na lallaba na
hada tea na sha.
98
Har dare yau ma ban samu nayi abinci
ba, don kuwa ko sallah da kyar nake iya
mikewa nayi.
Haka nan yau ma da ya dawo sha dayan
dare bai leko ni ba, dakinshi ya shige da
gari ya waye ya yi sammako kamar dai
dabi'arshi ta da.
Nayi kukan takaici har na gaji nayi
shiru, Ishak wane irin mutum ne wanda ko
kadan bai san hakkin zaman aure ba?
Amma kuma shi yana so ya sanyawa
mutum dokar rashin adalci kuma yabi.
Lallabawa nayi na shiga gidan su Hindu
duk da sanin da nayi me hakan yake nufi
idan har ya gane.
Momi tana ganina ta fara salati. "Ba ki
da lafiya ne Hauwa'u? Na ce, "Eh Momi.
Hindu nake nema." Ta ce, "To je ki gida
gata nan."
Hindu ce ta gyara mun gida ko ina,
sannan na sa ta tayi mun faten tsaki don
abinda zan iya ci kenan.
99
Na kuma yi matukar sa'a na samu na
sha sosai nayi wanka na dan samu karfi a
jikina.
Ita ce kuma ta taya ni nayi girki sosai,
tuwon semovita miyar kubewa danya da
taji tantakwashi da naman rago na' hada
komai na ajiye wa Ishak a wurin cin
abincinshi na shige daki na kwanta.
Duk da dan (Paracetamol) din da na
samu na sha jikina bai yi sauki ba, sai
dada tsananta yake yi.
Da sassafe na lallabo na shiga dakin
Ishak yana zaune yana duba wasu takardu
rabon da na saka shi a idona kwana hudu
kenan yau.
Yanayin da ya ganni a ciki bai hana shi
yamutsa fuska ba. Wane irin abu ne haka
ke wai wacce irin yarinya ce? Kin ga
yadda ki ka yi wujiga-wujiga kuwa?
Don Allah can wuce ki gyara jikinki
kafin ki zo mun nan muryata tana rawa ta
ce, "Ba ni da lafiya ne.
100
To idan ba ki da lafiya sai ki zo mun
haka? Mits! Fita don Allah kije kiyi wanka
wawiyar yarinya kawai."
Dawowa daki nayi na zauna sai da
nasha kukana ya ishe ni sannan na mike na
lallaba nayi wanka na saka doguwar riga
mai gyale na zauna na hada tea din da zan
sha.
Ruwan lipton ko birebi ban iya ci ba, na
koma na sake kwanciya don ko
Paracetamol din da zan sha ba ni da shi ya
kare.
Ishak bai fito ba sai wajen sha daya
kasancewarta Asabar. Sanye yake da Jeans
blue a shirt long sleeve wuce muje.
Hijabi na dauko muka fita zuwa asibiti.
Muna zaune a gaban Likita bayan ya
tabbatar mana ciki ne da ni karami, ya
kuma rubuta mana prescription na
magunguna wadanda muka karba a
chemist din asibiti muka kamo hanyar
komawa gida.
101
Tsananin zazzabin da ke damuna vasa
ban ma lura na gane hanyar da Ishak yab
ba sai da ya ce mun fita ki shiga ina
jiranki.
Na duba naga a kofar gidanmu muke,
cikin sauri na bude kofar motar na shiga.
A kicin na samu Umma taji sauki sosai, na
durkusa a gefen kicin din tana kallona.
"Hala kema ba ki da lafiyar ne ko naga
kin zama haka?" ban bata amsa ba sai
kuka da na fara yi mata.
"To menene kuma na kuka ai hakuri za
ki yi ba a yiwa ciwo kuka Hauwa'u, ki
zama jaruma. Ban daina kukan da nake yi
ba har ta gaji ta.ce "Ko dai kina da wata
matsala ne?"
Ban san me zan cewa Umma ba, ta gaji
da tambayata ta ce "Uhm, hakuri fa ake yi
da komai ma da ki ka gani na duniyar nan,
ballantana zaman aure.
Kada ki sa wa kanki wata damuwa
game da lamarin mijinki tunda dai bai
102
gaza miki da komai ba. Bai zama lallai sai
ka samu yadda ka ke so a kowanne lokaci
ba, kin gane.?"
Na tashi na yi wa Umma sallama na fito
muka dawo gida da Ishak. Wanda tsawon
watanni goma sha daya da nayi da shi a
matsayin matarshi ta aure bai sa shi ya yi
tunanin rana daya yaje ya gaisa da iyayena
da suka ba shi aurena ba.
Har kuma da rashin lafiyar da Ummana tayi.
Ciwo sosai nayi na wajen wata kusan
guda ina kwance ko aikin gida bana iyawa,
sai Hindu ta shigo tayi mun.
Ban samu saukin laulayin da naketyi ba
sai ana gab da sallah, ba ta fi sati biyu ba.
A cikin akwatina na dauki atamfa daya
da shadda mai laushi na bayar aka kaiwa
Umma don ta dinka atamfar ta bayar da
shaddar don a dinka wa su Tasi'u, tunda
bani da kudin da zan saya musu.
103
Ni kam Ishak yayi mun har kala biyu
masu kyau sosai, ban ma san da su ba sai
da ya karbo su daga wurin Tela.
Daga ni har shi din shirin sallar muke yi
ba kadan ba. Ta bangare na dai wannan ita
ce sallar da zan yi ta farko a dakin aurena.
Shi kuma yayi sayayya na abinci ba
kadan ba. Nayi cincin, cake, sannan nayi
miya mai dadin gaske da taji naman
Saniya.
Sannan na soya naman kajina gaba
daya. Ga kunun zakin da nayi wanda ya ji
kayan yaji sosai da busasshen dankali.
Hindu ce ta shigo da sassafe tun kafin a
tafi sallar Idi ta rinka mika mun abincin
gidajen makwabta saboda sammakon da
nayi na gamawa.
Tayi sallama a bakin kofä saboda sahin
da tayi Ishak na nan, na amsa mata na fito
ina tambayarta akwai,sauran gidan da ba a
baiwa ba ne?
104
Ta ce, "A'a." Na ce, "To don Allah idan
kin yi wanka sai ki kai mun na gidanmu
Ta ce, "To."
Na shiga daki da shiri na shiga wanka.
Ke zo nan. Ishak ne ya kira ni.
Kwanakin baya ba na hana yarinyar
nan shigowa gidan nan ba? Ba na ce bana
so ba? Gidannan wai shin ba gidana ba ne?
Idan na ce bana son abu menene dalilin
da yasa