MAI DAKI BOOK 1 HAUSA NOVELS BY SODANGI.docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   6 / 7

15K to 18K   out of 19.3K words

ba za a bari ba, ki kiyaye ni fa! Me

take zuwa ku ke yi? Gulma ko ba ki

munanan shawarwari da koya miki

dabi'un banza? To ya ishe ni haka."

Karo na farko da al'amarin Ishak ya

gundure ni na zuba mishi ido ina kallonshi.

Yana dandanna wasu lambobi ne a

waya, alamar zai yi kira. Kamar na ba shi

amsar maganganunshi sai naga ba zan iya

ba.

Yayi mun kwarjini da yawa sai kai na

wuce shi na shiga bandaki nayi wankana

na fito.

105

Lokacin nan kuwahar ya gama

shirinshi. Jamfa ce a jikinshi dogųwa ta

yadin shadda geitzner ja. Tayi mishi wani

irin kyau.

Ban taba ganin ya saka babbar riga ga

wata kila don baya ra'ayinta. Yana rike da

hularshi yana kokarin karyata haka kawai

na ga kalanta bai yi mun ba.

Na mika hannu na dauko watamai

ruwan ja da brown da wani ratsin nace ko

za ka ajiye wannan ne ka saka wannan

zuba mun ido ya yi yana kallona.

A hankali na ce mishi na gane kamar

tafi shiga da kayan. Ya mika hannu ya

karba bayan ya ajiye ta hannun nashi.

Ya karyata ya saka a kannan shi sannan

ya feshe jikinshi da turare. Yayi mun kyau

a idona. Ina matukar son yin mu'amalla

mai kyau da Ishak irin wacce nake ji ana

bada labari,

106

Don na san rayuwa ce da take faruwa a

zahiri. Ya juyo da kallonshi gare ni, nima

shi nake kallo.

"Zan tafi hawan Idi, ana saukowa zan

dawo, don zan yi baki daga office dinmu.

Ayi mun shiri na abubuwan ci sosai don

suna da yawa."

Na ce,To Allah ya bada sa'a." Ya

kuma amsa mana lbadunmu. " Ya ce,

"Amin.Ya fita.

Zama nayi na yi kwalliya ta burgewa ba

kadan ba, na dauko yadin material wanda

Ishak ya karbo mun daga gun Tela na saka

ya kuma karbi jikina ba kadan ba.

Gashi kuma na fara yin kibar ciki ga

fatata da ta yi haske tayi laushi zan iya

cewa ban taba yin kyau irin hakan ba.

Hindu ta shigo ita ma tayi kwaliya sosai

ta shadda da ta sha ado. Ta ce, "Kai Aunty

Hauwa, kin gan ki kuwa? Kin ga irin kyan

da ki ka yi?

107

Nayi murmushi na ce, Haba Hindu,

har na kai ki? Ta ce, "Haba wane ni, keta

dubi kalari kin san yadda ado yake yi wa

farin mutum kyau kuwa?"

Na ce,"Ke kuma ga ki doguwa kin san

kyau yana ga dogon mutum. 99 Gaba daya

muka yi dariya. Na ce mataTo barka da

sallah, Allah ya maimaita mana."

Ta ce,"Amin." Ta kwashe manyan food

flask guda biyu da na cika da abincin

gidanmu, daya dai miya ce da taji nama

don kuwa raba miyar nayi biyu na juye

rabi.

Dayan food flask din kuwa soyayyen

naman kaji ne da cincin da kek. Na saka

mata a nan ne don kaninta ne zai rike

gudun bari.

Ban zuba shinkafa ba don nasan Umma

zata dafa. Na shiga shiryawa Ishak abincin

bakinshi komai na tanadan mishi.

Karfe goma daidai ya shigo gidan. Nayi

mishi barka da sallah ina kallon shi ga

108

zatona zai yaba kwalliyata tunda ko da ba

dabi'arshi ba ce yin hakan.

Ai kuma yau sallah. Bai ce mun komai

ba har na gama shirya mishi abincin shi.

Ya ce "Da kin bari sai sun zo muci tare."

Na ce, Ai ba ka da tabbacin lokacin

zuwan nasu tunda yanzu ne ma aka sauko

daga Idi, kaci ko babu yawa zai rage maka

yunwa." Sai dai na daure ne kawai nayi

mishi wadannan bayanan.

Don tuni zuciyata ta fara hankoron

fushi. Na shiga daki na zauna a bakin gado

naga abin bai yi mun ba.

Na gaji da abubuwan ko in kula da

Ishak yake yi mun ko ma meye zai faru

kawai ya faru a yau dinnan.

B Ban san lokacin da na ganni zaune kan

kujerar da ke gabanshi ba.

Na kare mishi kallo yana cin abincin shi

cikin nutsuwa kana kallon shi ka san ba shi

da matsala.

109

Ya dago ya kalle ni Yaya lafiya?

kullum salon tambayarshi kenan. Ban ce

mishi komai ba ban kuma daina kallon

nashi ba.

Kina da matsala ne? ko wani abu yana

miki ciwo. Wani tunani yazo mun cikin

raina da kuma yasa na fasa yi mishi

magana na mike da nufin komawa daki.

Hauwa'u na juyo tare da amsawa. A tun

farkon zamana da Ishak zan iya kirga

adadin lokutan da ya kira sunana.

Zo ki kwashe wadannan kwanukan na

gama." Na zo ina kwashewa., Dan

sassaucin da na samu na mu'amalla ni

kaina nasan don juna biyun da nake dauke

da shi ne wani lokaci ya kan tambaye ni

akwai matsala ne ko kuma wani abu yana

yi miki ciwo?

Haka nan ya rage yawan dadewa a waje

karkari ya kai karfe goma shi kenan.

Na gama kwashewa da karin gyaran

wurin na dawo dakina na kwanta don

110

dan samu na huta ayyukan da na kwana

biyu ina yi.

Ya shigo dakin sanye da farar singilet

da wandon kayan da ya cire ya miko mun

kudi bandir din Naira dari sababbi fil da

su.

Na mika hannu na karba ina jira yayi

mun bayanin abinda za a yi. Ya ce, "Ki

ajiye barka da sallanki ne. in tsaya cewa

kudin nan sun yi mun dadi ma bata baki ne.

Sai dai kan nayi mishi godiya aka fara

buga sallama. Ya juya ya shiga dakinshi

don dauko rigar shi da ya tu6e.

Ni kuma na jawo gyalena mahadin

material din jikina na yafa na fito har ya

ba su izinin shigowa. Lallai kam bakin

Ishak da yawa.

A can gefe na zauna müka gaisa da su.

Ban tsaya kallonsu ba amma nasan sun

kusa goma. Ban iya komawa ba lokacin daa

111

na shiga kicin tunanin yadda zan yi na kat

musu sa'a shima ya fito ya zo kicin din.

Bani abincin kawai ba sai kin shiga ba

tunda kun gaisa.Ya fara kwasa yana

shigarwa sannan na hada Plate-Plate da

kofuna na sake mika mishi ya shiga.

An dai kai kamar mintina talatin na

motsin plate da cokula kawai nake jiwowa,

yayin da nake zaune a single dakin dake

tsakar gidan.

Kafin daga baya hira ta barke. Ina

sauraronsu kowa da abinda yake fada

game da abincin yayin da ake sakawa

wasu waigi.

Hira sosai şuka shiga yi daga baya da ta

kunshi wajen aiki da kuma wasu al'amura.

Koda nake kwance a kan gadon dakinnan

na kasa barci duk kuwa da irin gajiyar da

nayi saboda muryar Ishak da nake jiyowa,

Da yadda yake dariya da wasu

abubuwa. Mamaki ya kama ni, dama yana

112

hira da mutane da ni ne.bai yi ko kuwa ya ya?

Ba su tashi tafiya ba sai wajen azahar

suka fita gaba daya don yin sallah, bayan

sun nemi nazo muyi sallama ya ce musu

nayi barci.

Na dawo dakin na sake gyara shi tsaf

kamar ba a yi komai a ciki ba, sannan nayi

sallah na hau gadona na sake kwanciya.

Ishak bai dawo ba sai wajen hudu da

rabi. Na mike na bishi dakinshi baya ciki

alamar yana wanka na zauna a bakin

gadon ina jiran fitowar shi.

Tunda ya fito nake bin shi da kallo har

ya sanya short da jallabiya fara sol, sannan

ya sake kallona.

Ga wannan suka ce na baki goron

sallah. Yana miko mun kudi na kalli

kudin a hannunshi da yake miko min,

sannan na kalle shi shima ni yake kallo.

113

"Ya ya dai akwai matsala ne?" Na ce,

"Eh akwai, wannan ma da ka bani da safe

gasu nan na dawo maka da su bana so."

Ba karamun kada shi maganata tayi ba,

don tsawon zamana da Ishak ban taba

amsa mishi magana ba ballantana nayi

jayayya da shi.

Kuka na fara yi a daidai lokacin da na

fara magana. "Ni ba zan iya irin wannan

rayuwar ba. Dama abinda yasa nake ta

hakuri na dauka haka ka ke, haka

dabi'arka da halayyarka suke. To ashe ni

kadai ka ke yi ma.

Ya ce, "Wacce irin banzar magana ce

wannan, ke lafiyarki kuwa?" Na ce,

"Lafiya kalau, na dai gaji ne. Ban taba

saka kaya a gidan nan ka ce yayi kyau ba.

Ban taba yin girki kaci ka ce yayi dadi

ko bai yi ba, ban taba yin wani abu da

nufin na burge ka ka yaba mun abinda nayi

ba.

114

Ni a kullum a wajen ka a kushe nake.

Bana gwaninta a wajenka sai kuskure. Ni

kulluma wajen ka mai laifi ce ni.

Ba ka ganin nawa da mutunci saboda

ni, babu wani mutum da zai shigo cikin

gidan nan da sunan wurina yazo ba tare da

ka wulakantashi ni kuma ka bata min

ba..."

"Ke dakata! cikin tsawa ya dakatar da

ni. "Ita ce ta turo ki ki zo ki titsiye ni?

Kina nufin kin isa ki sa ni nayi abinda ban

yi niyya ba?

Wannan abin da ki ka zo ki ke yi ba zai

sa na canza daga dokata ta kada wani ya

shigo mun gida ba ko wanene ba tare da

yardata ba.

Kuma tunda yanzu na kara gane aibun

hakan nasan abinda zan yi kenan har kin

fara bin shawarwarinsu ne kina titsiye ni

akan abin da bana so. To babu laifi."

"Ba titsiyeka nayi ba, kuma ni babu

wani wanda yasan abinda muke yi

115

ballantana har ya bani shawara a kan

abinda zan yi.

Amma wacce irin rayuwa ce wannan?

Za ka iya zama da abokai kuyi hira kuyi

dariya tare amma ni matarka ta aure ba ka

da lokacina?

Idan gari ya waye ka fita ba zan sake

saka ka a idona ba sai wani wayewar

garin? Amma ni kana saka mun takunkumi

na yin mu'amalla har da 'yan uwana, to...

kafin na karasa tuni ya dauke ni da

marin da na kife a kasa.

"Ki rinka fahimtar lokacin da mutum yá

gundura da abu." Ya watsar mun da kudin

a wajen ya dauki mukullin motarshi yayi

waje.

A hankali na mike na goge hancina da

naji alamar ruwa-ruwa yana biyowa, jini

ne. Ban ci gaba da kukan da nake yi ba sai

dai duk da gargadin da zuciyata take yi

mun kan abinda nayi nufin yin ban fasa ba.

116

Wannan karon shi ne karo na uku da

Ishak yake dukana, Jakata na dauko har na

fito na nufe ko'ina sai na tuna ko kudin

mota ba ni da shi.

Dawowa nayi na bude dakin Ishak har

yanzu kudin suna watse a kasa na sunkuya

na dauki gudan dubu guda uku a kudin da

bakin shi suka ce ya bani na sake shig

dakina na dauko kaya set daya na sake fita

a gidan bayan na rurrufe ko ina na tafi

gida.

Ba karamin mamakın ganina suka yi ba,

don kuwa ban gaya musu zuwana ba.

Babana muma yake yi daga ganinshi

kuma na san ya dan samu canji, don kuwa

yayi fes da shi. Umma atamfar da nayi

mata ce a jikintą, haka nan su Taşi'u.

Umma ta zubo mun abinci ta ce "Ga shi

nan duk da dai daga gidanki yake." Na dan

yi murmushi na ce "Umma ba ni, naki

mana na ci,"

117

Ta ce, "Fuwo ne miyar taushe." Na ce,

Eh bani kawai. Cin abincin nayı sosai

sannan na sha kunun zaki. Ta ce, "Amma

ai ba yau muka yi da ke za ki zo ba ko?

Lafiya dai ko?"

Na dan yi shiru ban ce wa Umma koai

ba. "Idan akwai wani abu kiyi magana

mana, naga kamar ranki a bace yake."

Na rasa ta inda zan fara yin maganar

nan take kuma na kama kuka, sosai da

sosai. Sai dai na kasa cewa Umma ga

matsalata.

Ta ce, "To ko nayi, iki magana da

Babanku ne? Na girgiza kai na ce, "A'a."

Ta ce "To ki share hawayenki kiyi hakuri

kowacce mata da ki ka gani, da irin

matsalarta.

Shi aure haka yake, kina hango na wani

ne wani kuma yana hango naki. Ki daure

ki zamo mai sirTi a tsakaninki da mijinki.

Babu mai ganinki ya ce kina da matsala

kwata-kwata, tunda mijinki ba gaza miki

118

ba, bai kuma yi tsari ba a ce tun yanzun

kin koyi kai kararshi ba ki iya warware wa

kanki matsalarki ba tare da wani ko wata

ya fahimta ba.

Ki tashi ki koma kada ki dade kuma ya

zama matsala, tunda dai da'alama ma ba ki

sanar da shi zuwan ki ba."

Sai da Umma tayi wannan maganar ne

naji gabana ya yi matukar faduwa. Na

koma gida idan Ishak ya dawo kuma muyi

ya ya kenan?

Ban bari Umma ta fahimci halin da

nake ciki ba, dauko kudin dake Jakata nayi

na bata biyu na baiwa su Tasi'u canjin

kudin mota ta dari takwas na rage kudin

da za su mayar da ni gida.

Fitowar da zan yi kenan na hango motar

Ishak ta karyo kwanar unguwarmu, cikin

sauri na koma gida.

Umma ta ce "Lafiya?" Na ce, "Gashi

nan zuwa shima.". Ta ce, "To, to Allah

119

yasa kalau. Umma ce da kanta tayi mishi

shimfida suka gaisa.

Sannan aka kira Babana da ke tare da

wasu daga cikin makwabtanshi suna

tattaunawa. Gaisuwa sosai suka yi sannan

ya kawo goron sallah ya baiwa su Tasi'u.

An dan jima kafin ya nemi na fito mu tafi.

Bai ce mun komai ba har muka iso gida,

daidai an fara kiran sallar Magriba. Bayaan

gida na wuce nayi alwala na fito don bada

farali.

Shima a dakin shi yayi sallah. Ban fito

ba don kuwa na riga na kudurawa rainaa

zan zauna ne da lshak irin zaman da yake

so muyi da shi, tunda dai haka ya zaba.

Lekowa yayi dakina ya kira ni na shiga

yana tsaye. "Kwashe mun kudin nan. Na

sunkuya na kwashe su gaba daya..

Ya ce, "To zauna." Na nemi wuri a kasa

na zauna. Tashi ki zauna a bakin gado.

Nayi kamar yadda ya ce shima yazo bakin

gadon kusa da ni ya zauna.

120

"Na dauka kina da tarbiyya hakan ne

yasa ban taba yin zaton za ki yi abin da ki

ke yi a yau ba. Sake gaya mun abubuwan

da ki ka ce ba kya so wadanda nake yi

miki sai na kula nan gaba na daina.

Amma abinda ba zan lamunta ba shi ne,

ki kara zuwa mun cikin fusata irin na yau

ki ce za ki gaggaya mun bakaken

maganganu kin gane ko? Ba ke ce za ki

koya mun yadda zan rinka mu'amallata da

wasu ba.

Ina so ki san ke din ba za ki taba zama

mai sa ni ko mai hana ni ba, koyi samuna

cikin nutsuwa kina yi mun magana ta

yadda zan gane har kullum cewa ni ne

mijinki ba ke ce mijina ba kin gane ko?

Dokata ba za ta sauka ba na cewar ban

son shigowar waccan yarinyar cikin

gidana ba don a zahiri ga abinda ki ka yi

mun a yau wanda a da ba ki taba yi mun

ba, gabanin fara mu'amallarki da ita.

121

Na dago ido ina kallonshi "Zan kuma

dauki mataki da kaina ba sai kin shiga

matsala tunanin fuskantarta ba. Ba zan

lamunci masu son shiga lamarin aurena ba.

Na kuma yafe miki fita da ki ka yi ki ka

je gida a yau ba tare da kin nemi izinina ba

sai dai ina so ki san kin fitan ne a madadin

wunin da za.ki je na gaisuwar sallah."

Na mike da nufin fita a dakin. Ya ce

"Dawo ki zauna. Na dawo na hau gadon

na kwanta sai dai kuka na kama yi saboda

tukukin da zuciyata take yi mun.

Washegari da safe kamnar ba zan yi

kwalliyar ba, sai kuma naga kaina kawai

nake yi wa, don haka sai na yi kwalliyata

na sanya atamfa super exclusive holland

wacce ya yi mun a sallar.

Kadan ya rage na ce tafi yi min kyau a

jikina a kan material din da na saka jiya,

ita ma kalarta mai kyau ne kwarai, ruwan

kwai da jajja da kore kadan.

122

Adon atamfa tana matukar sanya

mutum kwarjini ba kadan ba. Na kammala

shirina na fita kicin ko bi ta kan Ishak ban

yi ba.

Sai da na gama ayyukana na kicin

sannan na shiga dakinshi don na kwaso

abubuwan da ya yi amfanida su da kuma

gyaran bandakin shi.

ldon shi biyu na same shi, sabanin dazu

da yake barci. Na shiga bayan gidan na

gama gyarawa sannan na zo don komawa

duba girkina.

"Zo mana." Na juyo na ce "Ga ni. "

Magana yake son yi sai dai ya rasa ta inda

zai yi ta, abinda na fahimta kenan.

Ya dai zuba mun ido sai da na gaji na

ce "Ka kira ni. Ya ce, "Eh na gane baki

nuna mun kwalliyar taki ba ballantana na

ce tayi kyau, ko ba haka ki ka ce na ringa

yi miki ba?"

Na juya nayi tafiyata ba tare da na ce

komai ba, ina gab da gama abinci ne naji

123

ana ta6a kofa. Na leka ta wurin da ake

ganin mutum.

Gabana ne yayi mummunan faduwa a

madadin farin ciki, Sadiya Tanimu ce. Na

dawo kamar na kyaleta ta gaji ta tafi, sai

kuma naga bai dace ba.

Dakin Ishak na shiga har yanzu yana

kwance na rasa yadda zan yi nayi mishi

bayanin don nasan yadda yake daukan

baki.

Sai shi ne ya yi mun tambayar tashi ta

fama Ya ya dai?" Na ce, Nayi bakuwa ne

kawata ta Makaranta ce tazo."

Bai sake kallona ba ya ce, "To menene

ki bude mata mana." Na juya na koma

muka rungume juna cikin tsananin farin

ciki.

Ta rike baki daidai ta shigo falo ta ce

"Kai Hauwa'u, kin gan ki kuwa? Kin yi

wani irin kyau abin ma ba a ko magana."

Na dan yi murmushi na ce "Sadiya

kenan. Ta

6 / 7