MAI DAKI BOOK 1 HAUSA NOVELS BY SODANGI.docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   1 / 7

1 to 3K   out of 19.3K words

MAI DAKI...

NA

HAJ. HAFSAT C. SODANGI

(Mrs. Yunus Abdullahi Dabai)

1

MAI DAKI... (1)

auwa'u Idris." Nayi maza na

Lmike tsaye tare da amsawa

saboda tun kafin ya kira sunana dama na

riga na harhada littattafaina, na zuba su a

cikin Jakata.

Ya waiwayo ya zub. mun ido sannan ya

ci gaba da kallon dogon littafin da ke ajiye

a kan teburin gaban nashi, wanda yake

littafin sunayen dalibai ne wadanda suka

biya kudin Makaranta, da kuma wadanda

ake bi bashi.

Ya ci gaba da kiran sunayen daliban

daya-bayan-daya duk wacce ya kira kuma

to zata tashi.

Sai da ya gama kiran sunayen ne sannan

ya waiwayo ya kalle mu ya ce, "To

tsayuwar me kuma ku ke yi a nan?

Cikin sauri kowacce ta fara nufar inda

yake, tana fada mishi uzurinta, wata ta ce

"Malam Babana yayi tafiya ya ce na bada

hakuri kafin ya dawo, sati mai zuwa.

7

Wata ta ce "Malam ni Babana ya ce ayi

hakuri kasuwa ce tayi gardama, zuwa wata

mai kamawa. Cikir sa'a kuma duk wacce

ta kawo uzurinta yana sauraronta tare da

ba wata dama.

Sai dai ni kam ban ma doshi inda yake

ba, don kuwa a wannan karon ban san me

zan cewa Malam Ali ba.

Ya waiwayo a karo na biyu ya sake

kallona "To ke tsayuwar me ki ke yi a

nan? Ko kuwa kina da wani abin da ki ke

son fada ne?

Na ce, "A'a a hankali ya ce ai ke ko ma

me za ki ce mun a wannan karon babu

abinda zai sa na saurare ki.

Ni na dade ko ma na ce tunda nake a

cikin Malamtaka ban taba haduwa da

dalibar da ke cin garabasar karatu irin naki

ba. Haba! Wane irin abu ne wannan?"

Na rataya Jakata na juya tare da kokarin

fita a cikin ajin, cikin sanyin jiki lokacin

8

da naji an kira sunana cikin sauri, na amsa

tare da juyawa.

Sadiya Tanimu ce dalibar da ke zaune a

kujerar da ke bayana.

"Ba ni littafina da ki ka karba dazu."

Na dora Jakata a kan bencin da ke

gabana na fara kokarin binciko mata

littafinta na darasin English (Turanci) da

na ara a safiyar yau don kwafar rubutun da

aka yi a lokacin da bana nan.

Malam ya ce, "Uhum, ba ka ji abin ba,

zat tafi miki da littafi. Allah dai ya

sauwake irin wannan abu to wai idan uba

bai tsaya yaga ya ilmantar da ya yanshi a

wannan zamani ba me zai yi mishi ne na

gata kuma?

Da irin wannan wahalar banzan da ki ke

yi na kullum kina cikin wadanda ba su

biya kudin Makaranta ba dama aure aka yi

miki ki ka huta don ban san yadda za a yi

kici jarrabawar gama Makaranta ba a irin

wannan tambelen da karatunki yake yi.

9

Ni halina da Hausawanmu kenan wai ba

za su tsaya suga sun biyawa ya'yansu

kudi sun yi karatu ba, amma idan an tashi

aurensu sai kaga mata ta sunkuya

karkashin gado tana zaro 'yan marofiya da

masu hannun katako."

Yan aji suka kwashe da dariya,

yayinda na mikawa Sadiya littafinta na

kama hanyar barin ajin.

"Ki hutar da kanki kada ki dawo, don

kuwa sai dai idan ban gan ki ba ko a ina ne

kuwa za a kore ki gida.

In tsaya cewa maganar Malam Ali bata

6ata mun rai ba ma to zance ne, kuma ku

san kullum haka yake yi mun, idan yazo

ajinmu koran kudin Makaranta ba zai bar

ni da takaicin koran kawai ba, sai ya bini

da bakaken maganganu.

Ni kuma ba abin in yi zuciya na ce na

daina zuwa ba tunda idan na ce haka ba

zan yi karatun ba kenan, don kuwa ba biya

mun din za a yi ba.

10

Duk wadannan takaicin da nake sha

lada ne akan a ce an fara jarrabawa, ranar

da duk wani dalibi yake. dokin zuwanta

saboda lokaci ne na nuna bajinta da kuma

gwaji kan abin da aka koyar da kai da

kuma gane irin fahimtar da ka yi. ab

Sai dai ni takan zo mun ne cikin

tsananin fargaba, don kuwa rana ce ta babu

sani babu sabo, idan har ana binka ko da

kwandala ce daya to babu ko shakka za a

kore ka gida.

Na rinka bin Malamai kenan ina kamun

kafa wadanda za su tabuka mun wani abu

ma wadanda babu wani taimako da za

su yi mun ba.

Wani lokaci ma kaga an bar wasu sun

shiga ajin jarrabawar wata kila saboda su

din kudin zango daya ake bin su, ko kuma

wasu sauran canji da ba su gama biya ba

N1 kuma a hana ni ko wani Malami ya

tausaya yasa baki sai ka ji Malam Ali yana

11

cewa ai ko an barta ta shiga da alkawarin

biya ba biya zata yi ba.

Ana binta bashin da ya kai na shekaru

uku, don haka barta nan kawai ta karaci

zamanta ta tafi.

Idan har akwai wani abu da nake burin

yin shi a rayuwata, to kuwa karatu ne, sai

dai ina ji ina gani abin yana nema yafi

karfina.

Babana ba shi da karfi, ba zai iya biya

mun kudin Makaranta ba, haka nan bai

ciyar da gida ba. Har a yanzu da muke mu

bakwai 'ya'yan Mamanmu, shi din

albashinshi a wurin da yake aiki bai fi

Naira dubu goma sha biyar ba a wata.

To da me ya ciyar damu, da me ya biya

mana kudin Makaranta da kuma sauran

hidindimu na rayuwa? Ta kai ma shi

kanshi ya hakura da karatun kannena maza

ya saka su a sauran wurare irin su, koyon

dinki da kuma kanikanci don ganin ya

12

maida hankalinshi kan nawa karatun ni

kadai amma abin ya gagara.

Don kuwa da albashin nashi kafin wani

watan ya zagayo an lamushe shi a bashi.

Dan sauki-saukin da muke samu to na

sana'ar dinkin da Ummanmu take yi ne

inda wani lokaci takan samu tayi cikon

cefane har ta adana mana dan abinda muke

hidima da shi na sallah.

ldan shekara ta zagayo babban abu guda

daya kuma mai muhimmanci a wurinmu

gaba daya shi ne muna da kwanciyar

hankali da nutsuwa tare da addini mnai

yawa a cikin gidan namu.

Don haka zama muke yi cikin

kwanciyar hankali da nutsuwa.

Na kamo. hanya don komawa gida

zuciyata cike da kunci, don kuwa wani irin

nisa ne a tsakanin gidanmu da Makarantar

wanda kuma a kullum da kafa nake zuwa

nake kuma dawowa.

13

Sannan a mafi akasarin lokuta na kan

tafi ne ba tare da nayi karin kumallo ba,

don kuwa na kan kasa hakurin jira don

kada nayi latti.

Tafiya zan kuma tafi ne ba tare da ko

sisi ba har sai na dawo ne zan ci abincin da

na samu an yi.

Ina karyo kwanar unguwarmu na hango

Abdussamad zaune kan dakalin shagon

askin dake makwabtaka da gidan su.

Wani irin faduwar gaba na samu, nan

take na juya na koma ta daya hanyar duk

kuwa da cewar ita din tafi nisa zan iya

cewa kusan kullum aka koro ni kudin

Makaranta, to sai na ganshi matukar ba

komawa tashi Makarantar yayi ba.

Na kane da niyyar na share shi nayi

kamar ban ganshi ba, don haka na

sunkuyar da kaina na ci gaba da tafiyata

har na dan gota su.

14

Sai naji ya ce "Barka da dawowa, ranki

shi dade. Cikin wayancewa na ce "Af, ai

ban ganka ba ne. 9 Tare da dan murmushi.

Ya mike ya nufo ni tare da kakkabe

wandonshi yayinda yake karasowa inda

nake. Ya dan tabe baki tare da cewa.

"Da dai kamar ban sanki ba ne ki ka

fada mun haka, to dana yarda.

Na fara gaishe shi bayan mun faraa

tafiya yana amsawa. Na ceAshe baka

koma ba har yanzu?

Ya ce, "A'a na koma jiya dai na sake

dawowa da yamma saboda wani yajin

aikin da Jami'o'i suka fara satin can da ya wuce.

Na ce, "Cabdijam! Abin dai babu dadi

Ya ce, "Eh to, kusan hakan, kin san

yanzu babu ranar komawa dai kenan

halin yajin aikin kasar nan, idan ba

matukar sa'a muka ci ba sai mukai

watanni biyar nan gaba zaune Gwamnati

15

bata dauki wani kwakkwaran mataki a kai ba.

Tunda su babu ruwansu, don talaka ne a

matsala tunda mu ne muka cika

cikin Jami'o' i kasar, su nasu suna can Turai

suna karatun cikin kwanciyar hankali, mu

kuma muna nan muna gwagwagwa.

Karatun da zai dauke ka shekaru hudu

idan ba matukar sa'a kayi ba sai ya kai ka

shekaru shida kana yi ba ka gama ba.

Shi yasa ai tun yanzu muke muku

addu'a komai ya gyaru kafin zuwan naku

lokacin, sai dai banga alamar ke za ki yi

nisa ba, nafi zaton aure za ki yi da alama.

Na kalle shi na ce, "Uhum! Sai anjima.

Na shiga gida saboda karasowar da muka

yi kofar gidan mu.

Akwai mutunc1 mai yawan gaske a

tsakanina da Abdussamad, don kuwa duk

shariyata da mutane suke magana akai, shi

kam muna gaisawa har ma mu dan yi hira

saboda shi ko na wuce shi to zai yi mun

16

magana har ta kai ma ba na ma iya wuce shin.

Makwabcinmu ne sosai, haka nan

Babana da Babanshi suna mutunci sosai a

tsakaninsu.

Nayi sallama na shiga gida, yan

kananan kannena ne suke wasa a tsakar

gida da alama Umma ta hana su fita zuwa

kofar gida ne.

Tasi'u da Sabi'u, a guje suka taho suna

rige-rigen karbar Jakar Makarantana. Na

mikawa Tasi'u saboda nasan Sabi'u ba iya

dauka zai yi ba, na kuma yi mishi dabara

ta hanyar daukanshi na cilla shi sama na

cabke.

Don kada ya saka mun rikici muka

karasa shiga dakı, suna yi mun hirar su ta

shirme Umma tana zaune a kan tabarma a

tsakar dakinta, yanka take yi na atamfa.

Na tsugunna nayi mata sannu da gida,

ta amsa ba tare da ta tambaye ni dalilin

17

dawowana ba, don ta riga tasan abinda ke

dawo da ni a irin wannan lokacin.

"Shiga ki tube kayan Makarantarki ki

saka na gida, ga dumame nan sai ki diba

kici. Na ce, "To.

Sai dana gama cinye dumamena daa

muka ci tare da su Tasi'u sannan na sake

hada kwanukan da sukalalacena wanke na

sake gyara gidan, na wanke bayan gida

sannan na sake dawowa wurin Ummana

ce, "Umma za a dora wani abu nea

wuta?

Ta ce, "Dan saurara dai tukuna muga

dawowar Auwalu ko?" Na ce, "To." Na

mikena shiga dakina dake tsakar gida na

dauko littattafaina na Makaranta don na

dan yi bita.

Har karfe daya na rana shiru Auwal bai

dawo ba, hakan ne ya sani sake tashi na

shiga cikin kicin dinmu na dauko dan

sauran garin kwakin da ke ajiye don na

jika musu.

18

Na kawo sugar na saka na mika musu

cokala sannan na dauki buta don yin

alwalar sallar Azahar.

Haka rayuwarmu take a gidanmu, kusan

kullum muna kwanciya ne da daddare ba

tare da mun san abinda zamu ci idan gari

ya waye ba.

Haka nan idan safiyar tayi muka samuu

muka karya kumallo, to ba ma sanin abin

da zamu ci idan rana tayi.

Saukin abin ma shi ne, yanzu Auwalu

ya kawo karfi yana kuma matukar

taimakawa.

Auwalu shi ne wana da nake bi, shi ne

kuma da na fari a wajen Iyayenmu baki

daya.

A yanzu haka makanike ne a cikin

babbar kasuwa, sai dai har yanzu ba

kwarewa yayi ba, amma yana matukar

samun' alheri ba kadan ba.

19

Saboda sa'ar da yayi na haduwa da

shugaba na kwarai, illa ko yau ma shi ne

ya shigo da cefane a hannunshi

Don haka na shafa fatiha cikin sauri na

fito na karbe shi.

"Akwai itace ne? Na ce, "Bari na

duba. Na leka kicin din na ce, Akwai,

amma dai babu yawa.

Ya juya ya fita, yayinda ni kuma na fara

kacaniyar dora girkin, ya sake shigowa da

itace kai biyu a hannunshi ya zuba tare da

miko mun Naira ashirin.

Ki bai wa Tasi'u ya sayo miki maggi,

ni na manta ban siya ba. Na ce, "To." Ya

juya da niyyar komawa wajen aikinshi.

Tuwon masara nayi tare da miyar

kubewa danya, saboda ita na gani a cikin

cefanen, ta kuma yi dadi da yawa na tuka

don mu samu na dumamen safe.

Na kwashe na adana na kowa tare da

rufewa na janye itacen na dora ruwan

20

wankana a kan garwashin sannan na

kawowa Umma nata.

Sai da nayi wanka na yiwo alwalar

sallar La'asar, don kuwa zan iya cewaa

yanzu dabi'ata ce hakan saboda kusan

kullum abincin yamma muke yi.

Na idar da sallar La'asar na jawo

kwalbar maina da Auwalu yake kawo mun

mai kamshi.

Duk da ba wani mai tsada ba ne, shafa

shi yana sani naji ni'ima saboda kamshin

shi.

Na murza hoda da dan kwalli na jawo

atamfata na daura sannan na fito nazo 1in

da Umma take na zauna don naci nawa

abincin.

Muka dan fara hira wacce yawancinta

akan Makarantata ce. Tace "Sai ki

yawaita addu'a, Allah ya zabar miki mafi

alheri a ciki, ko karatun idan zai yiwu.

21

ldan kuwa ba mai yiwuwa ba ne to sai

kiyi aure a kai ki dakinki kema ki nutsu ki

zauna a wuri daya.

Babban burin Iyayena bai wuce na

ganin nayi karatu ba, ko da kuwa wacce

irin wahala za su yi don ganin hakan.

Hakan ne yasa da Umma tayi mun

wannan maganar gabana yayi matukar

faduwa, ta soma hakura kenan ko ya ya?

Na ce, "Umma aure fa ki ka ce?

Ta ce, "Eh shi na ce idan karatun ba zai

yiwu ba menene amfanin zaman gidan

tunda kin riga kin isa auren.

Shi ma Babanku ai ya nga ya fara

hakura tunda naga an kwan biyu ba tare da

yayi maganar Makarantarki ba.

Jikina yayi matukar yin sanyi, dafin

maganar Umma sai dai ban ce mata komai

ba, don ba maganata ba ce tunda ba zan

iya tuna ranardas wata magana

makamancinyar wannan da ta danganci

aure ta hada ni da ita ba.

22

Aunty Hauwa'u kizo in ji Yayan su

Lubabatu. Na waiwayo na zuba ma

Tasi'u ido, na ce "In zo fa ka ce?

Ya ce, "Eh shi ne ya aiko ni gashi nan

ma a zaure. Umma ta ce "To ki ka sani ko

wani abu zai tambaye ki?

Na ce, To bari naji naga bai taba

aikowa gidanmu a kira ni ba." Hijabina na

sako na fita kofar gida inda yake tsaye.

Wata gaisuwar muka sake yi yana

kallona "Ya na ganki fuskarki wata iri?

Na dan yi murmushi na ce, "Ai da ka

kirani ne baka ji yadda zuciyata tayi ba, sai

da gabana ya fadi.

Ya ce, "To da alama dai ba ki da

gaskiya kenan." Na ce, "A'a rashin

gaskiyar me? Na dai dauka wani abu ne ya

faru kuma ka san ban saba hakan ba. 99 Ya

ce, "Eh to, ai komai dama farashi ake yi

ko?

Ua juya inda su Tasi'u da Sabi'u suke

harkokinsu ya mika musu Naira ashirin ya

23

ce a siyo biskit suka karba tare da fallawa

da gudu don sayowan.

Ba wai don yazo wurina ko kuma kofar

gidanmu ba ne yasa shi yin hakan, dama

can dabi'arshi ce inda duk ya gan su to zai

saya musu ko biskit ko cakulet.

Ya waiwayo inda nake "To ya ya

yanmata ya karatu? Na ce, To mun

gode Allah, ni yanzu kina aji nawa ne?"

Na ce, "SS1." Ya ce, "Dama nayi zaton

kina tafiya ne tare da su Luba, sai dai a

hanya za ki tsaya tunda ban ga alamar kina

mayar da hankali tare da bada himmar yin

karatun ba."

Na ce, "Me yasa ka fadi haka? Ya ce,

A'a na gane kamar aure ki ke so.

Wayancewa nayi tamfar maganar bata bata

mun rai ba.

Kuma kafin na samu amsar ba shi sai na

hango Babanmu yana tahowa daga wurin

aiki kuma yake na ce "Ni zan shiga gida

ga Baba nan ya dawo.

24

Har kasa Abdussamad ya tsugunna ya

gaida Babana, sannan ya wuce ni kuma na

shigo gida ina yi mishi barka da zuwa.

Ban wuce dakina ba abincin Babanmu

na dauko na kai mishi dakin Umma tare da

ruwa. Yana sanye da kayan gida da alamar

har ya cire na aikin shi sannan na sake

mishi sannu da zuwa na wuce dakina.

Washegari da sassafe kamar kullum sai

da na hada mana abin karyawa, kunu da

dumamen tuwo sannan na saka uniform

dina na dauko hanyar Makaranta.

Kamar daga sama ina shiga ajinmu

kafin na zauna sai ga Malam Ali ya shigo,

ya ce "Maras zuciya, ai dama nasan yau

ma sai kin dawo shi yasa na bugo

sammakon zuwa ajin naku don na gani.

Ba kuma zan bar ki ko darasi daya ki

samu ba. Juya kawai ki tafi." Na juyo na

kamo hanyar dawowa gida, yau kam ta

lungun unguwarmu na biyo don kaucewa

idon Abdussamad.

25

Ban tsaya yin komai ba kan yar

yamushashshiyar katifata na hau na

kwanta ba zan iya cewa ga iyakacin abinda

Zuciyata take gaya mun ba, illa iyaka dai

kawai nasan babu mamaki, ni din ba zan

samu cikar burina ba ne a rayuwata shi ne

na ni din na zama Nos, wato Malamar

jinya.

Nayi kuka har na gaji ban san sanda

barci ya dauke ni ba, na dai farka ne naji

ana kiran sallar azahar.

Na mike tare da yin salati da na tuna ko

abincin rana ban dora ba, tunda idan ina

gida ni ce mai yi. Na fito cikin sauri na

samu har Umma ta riga ta sauke tana rabo.

Shinkafa da wake ne, da mai da yaji.

Nayi mata sannu sannan na shiga bandaki

don kama ruwan in alwala.

Har na gama hidimomina na gida yau

ko waiwayon littafan Makarantana ban yi

ba, don

1 / 7